< Ezra 3 >

1 Da tsayawar watan bakwai, sai Isra’ilawa waɗanda suka koma garuruwansu suka taru da nufi ɗaya a Urushalima.
Or le septième mois approchant, et les enfants d'Israël étant dans leurs villes, le peuple s'assembla à Jérusalem comme si ce n'eût été qu'un seul homme.
2 Sai Yeshuwa ɗan Yozadak da sauran firistoci, da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da abokan aikinsa, suka fara gina bagaden Allah na Isra’ila don miƙa hadaya ta ƙonawa bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa mutumin Allah.
Alors Jésuah, fils de Jotsadak, se leva avec ses frères les Sacrificateurs, et Zorobabel fils de Salathiel, avec ses frères, et ils bâtirent l'autel du Dieu d'Israël, pour y offrir les holocaustes, ainsi qu'il est écrit dans la Loi de Moïse, homme de Dieu.
3 Duk da tsoron da suke ji na mutanen da suke kewaye da su, sun gina bagaden a wurinsa, suka kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagaden ga Ubangiji safe da yamma.
Et ils posèrent l'autel de Dieu sur sa base, parce qu'ils avaient peur en eux-mêmes des peuples du pays, et ils y offrirent des holocaustes à l'Eternel, les holocaustes du matin et du soir.
4 Bisa ga abin da yake a rubuce kuma, suka yi biki Bikin Tabanakul, suka miƙa hadayu kowace rana gwargwadon yawan hadayun da ake bukata.
Ils célébrèrent aussi la fête solennelle des Tabernacles, en la manière qu'il est écrit [dans la Loi]; et ils [offrirent] les holocaustes chaque jour, autant qu'il en fallait, selon que portait l'ordinaire de chaque jour;
5 Bayan wannan, suka miƙa hadayu na ƙonawa yadda aka saba. Suka miƙa hadayu na Sabon Wata, da hadayu na bukukkuwan Ubangiji, da kuma hadayun da aka bayar da yardar rai ga Ubangiji.
Après cela, l'holocauste continuel, et ceux des nouvelles lunes, et de toutes les fêtes solennelles de l'Eternel, lesquelles on sanctifiait, et de tous ceux qui présentaient une offrande volontaire à l'Eternel.
6 A ranar farko ta watan bakwai, sai suka fara miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko da yake ba a riga an aza harsashin ginin haikalin Ubangiji ba.
Dès le premier jour du septième mois ils commencèrent à offrir des holocaustes à l'Eternel; bien que le Temple de l'Eternel ne fût pas encore fondé.
7 Sai suka ba wa magina da kafintoci kuɗi, suka ba wa mutanen Sidon da na Taya abinci, da abin sha, da mai, don su kawo itatuwan al’ul a Yaffa daga Lebanon ta teku, yadda Sairus sarkin Farisa ya ba da umarni.
Mais ils donnèrent de l'argent aux tailleurs de pierres et aux charpentiers, [ils donnèrent] aussi à manger et à boire, et de l'huile, aux Sidoniens et aux Tyriens, afin qu'ils amenassent du bois de cèdre du Liban à la mer de Japho, selon la permission que Cyrus, Roi de Perse, leur en avait donnée.
8 A wata na biyu na shekara ta biyu, bayan sun komo gidan Allah a Urushalima, sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, Yoshuwa ɗan Yozadak da sauran’yan’uwansa (Firistoci da Lawiyawa da duk waɗanda suka komo Urushalima daga bauta) suka fara aiki, aka zaɓi Lawiyawa daga masu shekaru ashirin da haihuwa zuwa waɗanda suka wuce haka don su dubi aikin ginin gidan Ubangiji.
Et la seconde année de leur arrivée en la maison de Dieu à Jérusalem, au second mois, Zorobabel, fils de Salathiel, et Jésuah, fils de Jotsadak, et le reste de leurs frères, les Sacrificateurs, et les Lévites, et tous ceux qui étaient venus de la captivité à Jérusalem, commencèrent [à fonder le Temple]; et ils établirent des Lévites, depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, pour presser l'ouvrage de la maison de l'Eternel.
9 Yeshuwa da’ya’yansa maza, da’yan’uwansa, da Kadmiyel da’ya’yan Yahuda (’yan zuriyar Hodawiya), da’ya’yan Henadad, da’ya’yansu da’yan’uwansu, dukansu Lawiyawa ne, suka haɗa kai cikin duban masu aikin gidan Allah.
Et Jésuah assistait avec ses fils et ses frères, et Kadmiel avec ses fils, enfants de Juda, pour presser ceux qui faisaient l'ouvrage en la maison de Dieu; [et] les fils de Hémadad, avec leurs fils et leurs frères, Lévites.
10 Da masu ginin suka aza harsashin ginin haikalin Ubangiji, sai firistoci suka sa kayansu na firistoci suka riƙe ƙahonin busa, Lawiyawa (’ya’yan Asaf) kuwa suka riƙe kuge, suka yi shiri domin su rera yabo ga Ubangiji kamar yadda Dawuda Sarkin Isra’ila ya ba da umarni.
Et lorsque ceux qui bâtissaient fondaient le Temple de l'Eternel, on y fit assister les Sacrificateurs revêtus, ayant leurs trompettes; et les Lévites, enfants d'Asaph, avec les cymbales, pour louer l'Eternel, selon l'institution de David, Roi d'Israël.
11 Suka rera waƙar yabo da godiya ga Ubangiji, suna cewa, “Shi nagari ne; ƙaunarsa kuwa ga Isra’ila har abada ce.” Dukan jama’a kuwa suka yabi Ubangiji da murya mai ƙarfi, domin an aza harsashin ginin gidan Ubangiji.
Et ils s'entre-répondaient en louant et célébrant l'Eternel, [chantant]: Qu'il est bon, parce que sa gratuité demeure à toujours sur Israël. Et tout le peuple jeta de grands cris de joie en louant l'Eternel, parce qu'on fondait la maison de l'Eternel.
12 Amma tsofaffin firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai da yawa, waɗanda dā suka ga yadda haikali na farko yake, suka fashe da kuka mai ƙarfi sa’ad da suka ga an aza harsashin ginin wannan haikali, yayinda waɗansu kuma suka yi ihu da farin ciki.
Mais plusieurs des Sacrificateurs et des Lévites, et des Chefs des pères qui étaient âgés, [et] qui avaient vu la première maison sur son fondement, se représentant cette maison-là, pleuraient à haute voix; mais plusieurs élevaient leur voix avec des cris de réjouissance, et d'allégresse.
13 Ba wanda zai iya rabe tsakanin ihun farin ciki da na kuka, domin mutanen sun tā da murya sosai har aka ji su daga nesa.
Et le peuple ne pouvait discerner la voix des cris de joie, et d'allégresse, d'avec la voix des pleurs du peuple; cependant le peuple jetait de grands cris de joie, en sorte que la voix fut entendue bien loin.

< Ezra 3 >