< Ezra 3 >
1 Da tsayawar watan bakwai, sai Isra’ilawa waɗanda suka koma garuruwansu suka taru da nufi ɗaya a Urushalima.
Lorsque le septième mois fut arrivé, et que les enfants d'Israël furent dans les villes, le peuple se rassembla comme un seul homme à Jérusalem.
2 Sai Yeshuwa ɗan Yozadak da sauran firistoci, da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da abokan aikinsa, suka fara gina bagaden Allah na Isra’ila don miƙa hadaya ta ƙonawa bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa mutumin Allah.
Alors Josué, fils de Jotsadak, se leva avec ses frères les prêtres et Zorobabel, fils de Shealtiel, et ses proches, et ils bâtirent l'autel du Dieu d'Israël, pour y offrir des holocaustes, comme il est écrit dans la loi de Moïse, homme de Dieu.
3 Duk da tsoron da suke ji na mutanen da suke kewaye da su, sun gina bagaden a wurinsa, suka kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagaden ga Ubangiji safe da yamma.
Malgré la crainte qu'ils éprouvaient à cause des peuples des contrées voisines, ils posèrent l'autel sur sa base, et ils offrirent sur lui des holocaustes à l'Éternel, des holocaustes matin et soir.
4 Bisa ga abin da yake a rubuce kuma, suka yi biki Bikin Tabanakul, suka miƙa hadayu kowace rana gwargwadon yawan hadayun da ake bukata.
Ils célébrèrent la fête des tabernacles, comme il est écrit, et offrirent les holocaustes quotidiens en nombre, selon les prescriptions, comme l'exigeait le devoir de chaque jour;
5 Bayan wannan, suka miƙa hadayu na ƙonawa yadda aka saba. Suka miƙa hadayu na Sabon Wata, da hadayu na bukukkuwan Ubangiji, da kuma hadayun da aka bayar da yardar rai ga Ubangiji.
puis l'holocauste perpétuel, les offrandes des nouvelles lunes, de toutes les fêtes de l'Éternel qui étaient consacrées, et de tous ceux qui offraient volontairement une offrande à l'Éternel.
6 A ranar farko ta watan bakwai, sai suka fara miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko da yake ba a riga an aza harsashin ginin haikalin Ubangiji ba.
Dès le premier jour du septième mois, ils commencèrent à offrir des holocaustes à l'Éternel, mais les fondations du temple de l'Éternel n'étaient pas encore posées.
7 Sai suka ba wa magina da kafintoci kuɗi, suka ba wa mutanen Sidon da na Taya abinci, da abin sha, da mai, don su kawo itatuwan al’ul a Yaffa daga Lebanon ta teku, yadda Sairus sarkin Farisa ya ba da umarni.
Ils donnaient aussi de l'argent aux maçons et aux charpentiers. Ils donnèrent aussi de la nourriture, des boissons et de l'huile aux habitants de Sidon et de Tyr pour qu'ils apportent des cèdres du Liban jusqu'à la mer, à Joppé, selon la concession qu'ils avaient reçue de Cyrus, roi de Perse.
8 A wata na biyu na shekara ta biyu, bayan sun komo gidan Allah a Urushalima, sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, Yoshuwa ɗan Yozadak da sauran’yan’uwansa (Firistoci da Lawiyawa da duk waɗanda suka komo Urushalima daga bauta) suka fara aiki, aka zaɓi Lawiyawa daga masu shekaru ashirin da haihuwa zuwa waɗanda suka wuce haka don su dubi aikin ginin gidan Ubangiji.
Or, la deuxième année de leur arrivée à la maison de Dieu à Jérusalem, au deuxième mois, Zorobabel, fils de Shealthiel, Josué, fils de Jotsadak, et le reste de leurs frères, les prêtres et les lévites, et tous ceux qui étaient venus de la captivité à Jérusalem, commencèrent le travail et désignèrent les lévites, depuis l'âge de vingt ans et au-dessus, pour surveiller l'ouvrage de la maison de Yahvé.
9 Yeshuwa da’ya’yansa maza, da’yan’uwansa, da Kadmiyel da’ya’yan Yahuda (’yan zuriyar Hodawiya), da’ya’yan Henadad, da’ya’yansu da’yan’uwansu, dukansu Lawiyawa ne, suka haɗa kai cikin duban masu aikin gidan Allah.
Alors Josué se tint avec ses fils et ses frères, Kadmiel et ses fils, les fils de Juda, ensemble pour avoir la surveillance des ouvriers de la maison de Dieu: les fils de Henadad, avec leurs fils et leurs frères les Lévites.
10 Da masu ginin suka aza harsashin ginin haikalin Ubangiji, sai firistoci suka sa kayansu na firistoci suka riƙe ƙahonin busa, Lawiyawa (’ya’yan Asaf) kuwa suka riƙe kuge, suka yi shiri domin su rera yabo ga Ubangiji kamar yadda Dawuda Sarkin Isra’ila ya ba da umarni.
Lorsque les bâtisseurs posèrent les fondations du temple de Yahvé, ils mirent les prêtres en tenue avec des trompettes, et les lévites, fils d'Asaph, avec des cymbales, pour louer Yahvé, selon les instructions de David, roi d'Israël.
11 Suka rera waƙar yabo da godiya ga Ubangiji, suna cewa, “Shi nagari ne; ƙaunarsa kuwa ga Isra’ila har abada ce.” Dukan jama’a kuwa suka yabi Ubangiji da murya mai ƙarfi, domin an aza harsashin ginin gidan Ubangiji.
Ils chantaient l'un après l'autre en louant et en remerciant Yahvé: « Car il est bon, car sa bonté dure à jamais envers Israël. » Tout le peuple poussa de grands cris en louant Yahvé, car les fondements de la maison de Yahvé avaient été posés.
12 Amma tsofaffin firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai da yawa, waɗanda dā suka ga yadda haikali na farko yake, suka fashe da kuka mai ƙarfi sa’ad da suka ga an aza harsashin ginin wannan haikali, yayinda waɗansu kuma suka yi ihu da farin ciki.
Mais beaucoup de sacrificateurs, de lévites et de chefs de famille, de vieillards qui avaient vu la première maison, lorsque les fondements de cette maison furent posés sous leurs yeux, pleurèrent à haute voix. Beaucoup aussi poussaient des cris de joie à haute voix,
13 Ba wanda zai iya rabe tsakanin ihun farin ciki da na kuka, domin mutanen sun tā da murya sosai har aka ji su daga nesa.
si bien que le peuple ne pouvait distinguer le bruit des cris de joie du bruit des pleurs du peuple; car le peuple poussait de grands cris, et le bruit était entendu au loin.