< Ezra 3 >
1 Da tsayawar watan bakwai, sai Isra’ilawa waɗanda suka koma garuruwansu suka taru da nufi ɗaya a Urushalima.
It was the seventh month after the people of Israel came back to their cities, when they gathered together as one man in Jerusalem.
2 Sai Yeshuwa ɗan Yozadak da sauran firistoci, da Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da abokan aikinsa, suka fara gina bagaden Allah na Isra’ila don miƙa hadaya ta ƙonawa bisa ga abin da yake a rubuce a Dokar Musa mutumin Allah.
Jeshua son of Jozadak and his brothers the priests, and Zerubbabel son of Shealtiel, and his brothers rose up and built the altar of the God of Israel to offer burnt offerings as it is written in the law of Moses the man of God.
3 Duk da tsoron da suke ji na mutanen da suke kewaye da su, sun gina bagaden a wurinsa, suka kuma miƙa hadaya ta ƙonawa a kan bagaden ga Ubangiji safe da yamma.
Then they established the altar on its stand, for dread was on them because of the people of the land. They offered burnt offerings to Yahweh at dawn and evening.
4 Bisa ga abin da yake a rubuce kuma, suka yi biki Bikin Tabanakul, suka miƙa hadayu kowace rana gwargwadon yawan hadayun da ake bukata.
They also observed the Festival of Shelters as it is written and offered burnt offerings day by day according to the decree, each day's duty on its day.
5 Bayan wannan, suka miƙa hadayu na ƙonawa yadda aka saba. Suka miƙa hadayu na Sabon Wata, da hadayu na bukukkuwan Ubangiji, da kuma hadayun da aka bayar da yardar rai ga Ubangiji.
Accordingly, there were daily burnt offerings and monthly ones and offerings for all the fixed feasts of Yahweh, along with all the freewill offerings.
6 A ranar farko ta watan bakwai, sai suka fara miƙa hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji, ko da yake ba a riga an aza harsashin ginin haikalin Ubangiji ba.
They began to offer up burnt offerings to Yahweh on the first day of the seventh month, although the temple had not been founded.
7 Sai suka ba wa magina da kafintoci kuɗi, suka ba wa mutanen Sidon da na Taya abinci, da abin sha, da mai, don su kawo itatuwan al’ul a Yaffa daga Lebanon ta teku, yadda Sairus sarkin Farisa ya ba da umarni.
So they gave silver to the stoneworkers and craftsmen, and they gave food, drink, and oil to the people of Sidon and Tyre, so they would bring cedar trees by sea from Lebanon to Joppa, as authorized for them by Cyrus, king of Persia.
8 A wata na biyu na shekara ta biyu, bayan sun komo gidan Allah a Urushalima, sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, Yoshuwa ɗan Yozadak da sauran’yan’uwansa (Firistoci da Lawiyawa da duk waɗanda suka komo Urushalima daga bauta) suka fara aiki, aka zaɓi Lawiyawa daga masu shekaru ashirin da haihuwa zuwa waɗanda suka wuce haka don su dubi aikin ginin gidan Ubangiji.
Then in the second month of the second year after they came to the house of God in Jerusalem, Zerubbabel son of Shealtiel, Jeshua son of Jozadak, the rest of the priests, the Levites, and those who came from captivity back to Jerusalem began the work. They assigned the Levites twenty years old and older to oversee the work of Yahweh's house.
9 Yeshuwa da’ya’yansa maza, da’yan’uwansa, da Kadmiyel da’ya’yan Yahuda (’yan zuriyar Hodawiya), da’ya’yan Henadad, da’ya’yansu da’yan’uwansu, dukansu Lawiyawa ne, suka haɗa kai cikin duban masu aikin gidan Allah.
Jeshua and his sons and brothers, and Kadmiel and his sons, who were descendants of Hodaviah), and the sons of Henadad and their sons and brothers-all of them were Levites-joined together in supervising those working on the house of God.
10 Da masu ginin suka aza harsashin ginin haikalin Ubangiji, sai firistoci suka sa kayansu na firistoci suka riƙe ƙahonin busa, Lawiyawa (’ya’yan Asaf) kuwa suka riƙe kuge, suka yi shiri domin su rera yabo ga Ubangiji kamar yadda Dawuda Sarkin Isra’ila ya ba da umarni.
The builders laid a foundation for Yahweh's temple. This enabled the priests to stand in their garments with trumpets, and the Levites, sons of Asaph, to praise Yahweh with cymbals, just as the hand of David, king of Israel had commanded.
11 Suka rera waƙar yabo da godiya ga Ubangiji, suna cewa, “Shi nagari ne; ƙaunarsa kuwa ga Isra’ila har abada ce.” Dukan jama’a kuwa suka yabi Ubangiji da murya mai ƙarfi, domin an aza harsashin ginin gidan Ubangiji.
They sang with praise and thankfulness to Yahweh, “He is good! His covenant faithfulness to Israel endures forever.” All the people cried out with a great shout of joy in praise of Yahweh because the temple's foundations had been laid.
12 Amma tsofaffin firistoci, da Lawiyawa, da shugabannin iyalai da yawa, waɗanda dā suka ga yadda haikali na farko yake, suka fashe da kuka mai ƙarfi sa’ad da suka ga an aza harsashin ginin wannan haikali, yayinda waɗansu kuma suka yi ihu da farin ciki.
But many of the priests, Levites, and chief patriarchs, those who were old and had seen the first house, when this house's foundations were laid before their eyes, wept loudly. But many people had shouts of joy with gladness and an excited sound.
13 Ba wanda zai iya rabe tsakanin ihun farin ciki da na kuka, domin mutanen sun tā da murya sosai har aka ji su daga nesa.
As a result, people were not able to distinguish the joyful and glad sounds from the sound of people weeping, for the people were crying out with great joy, and the sound was heard from far away.