< Ezra 10 >

1 Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
Ezra låg på marki framfyre gudshuset og gret og bad og sanna synderne. Då samla det seg kring honom ein ovstor skare av Israels folk, karar og kvinnor og born, og folket gret sårt.
2 Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
Då tok Sekanja Jehielsson av Olams-sønerne til ords og sagde med Ezra: «Me hev vore utrugne åt mot vår Gud, med di me hev teke framande konor frå dei framande folki her i landet; men endå er ikkje all voni ute for Israel i denne saki.
3 Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
Lat oss no gjera samband med vår Gud, um at me jagar frå oss alle desse konorne, og borni som dei hev fenge, etter kravet frå Vårherre og frå dei mennerne som ræddast for Guds lov, og lat det so verta gjort etter lovi.
4 Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
Ris upp! for det er du som lyt greida denne saki, og me skal stydja deg. Ver frihuga og set det i verk!»
5 Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
Då reis Ezras upp og let prestehovdingarne og levithovdingarne og alle andre hovdingar i Israel gjera eid på at det måtte vera som her det var sagt. Og dei gjorde eiden.
6 Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
Ezra stod upp frå den staden framfyre gudshuset, og gjekk inn i romet åt Johanan Eljasibsson. Og då han var komen dit, var han ikkje god til å eta eller drikka, soleis syrgde han yver utruskapen åt deim som var attkomne frå utlægdi.
7 Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
So lyste dei ut yver Juda og Jerusalem til deim som var komen heim or utlægdi, at dei alle skulde samlast i Jerusalem!
8 Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
Var det nokon som ikkje kom innan tridje dagen etter, soleis som hovdingarne og styringsmennerne hadde sett, so skulde all hans eigedom verta bannstøytt, og han sjølv verta jaga ut or samlingi av deim som var komne heim or utlægdi.
9 A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
So samla alle Juda- og Benjamins-mennerne seg i Jerusalem til tridje dagen; det var tjugande dagen i den niande månaden. Alt folket sat på den opne plassen attmed gudshuset og skalv, både for saki skuld og for regnbyorne.
10 Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
Då stod presten reis Ezra upp og sagde til deim: «De hev vore utrugne, med di de hev teke framande kvende til konor, og dermed hev de auka skuldi åt Israel.
11 Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
Gjev no Herren æra, Gud åt federne dykkar, og gjer etter viljen hans; skil dykk frå dei hine folki her i landet og frå dei framande konorne!»
12 Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
Då svara heile lyden med høg røyst: «Ja, som du hev sagt, so er me skuldige å gjera.
13 Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
Men folket er mange i tal, og no er det regntidi, so me kann ikkje verta standande her ute. Dette er og ei ærend som ikkje verta avgjord på ein dag eller tvo; for me hev mykje synd på oss i dette stykket.
14 Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
Lat difor hovdingarne våre gjera greida for heile lyden, og lat so alle deim i byarne våre som hev teke framande kvende til konor, møta fram til tider som vert fastsette, saman med styresmennerne og domarane frå den same byen, til dess me kann få vendt av vår Guds brennande harm for denne saki.»
15 Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
Einast Jonatan Asaelsson og Jahzeja Tikvason gjorde motmæle mot dette, og Mesullam saman med leviten Sabbetai heldt med deim.
16 Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
Dei som var attkomne or utlægdi, gjorde som sagt var. Og utvalde vart: Presten Ezras og nokre menner, hovdingar for ættgreinerne sine, alle nemnde på namn. So sette dei rådstemna den fyrste dagen i den tiande månaden til å granska denne saki.
17 A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
Til fyrste dagen i fyrste månaden hadde dei greidt upp saki for dei mennerne som hadde teke seg framande kvende til konor.
18 A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
Millom prestesønerne fann dei desse som hadde teke framande kvende til konor: Av sønerne åt Jesua Josadaksson og brørne hans: Ma’aseja, Eliezer, Jarib og Gedalja;
19 (Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
dei vilde styra frå seg konorne sine og ofra ein ver til syndoffer for den skuld dei hadde drege på seg - det lova dei og rette fram handi si på det;
20 Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
av Immers-sønerne: Hanani og Zebadja;
21 Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
av Harims-sønerne: Ma’aseja, Elias, Semaja, Jehiel og Uzzia;
22 Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
av Pashurs-sønerne: Eljoenai, Ma’aseja, Ismael, Netanel, Jozabad og Elasa.
23 Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
Av levitarne: Jozabad, Sime’i og Kelaja, som og heitte Kelita, Petahja, Juda og Eliezer;
24 Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
av songarane: Eljasib; av dørvaktarane: Sallum, Telem og Uri.
25 Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
Av Israel elles: Av Paros-sønerne: Ramja, Izza, Malkia, Mijamin, Eleazar, Malkia og Benaja;
26 Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
av Elams-sønerne: Mattanja, Zakarja, Jehiel, Abdi, Jeremot og Elia;
27 Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
av Zattu-sønerne: Eljoenai, Eljasib, Mattanja, Jeremot, Sabad og Aziza;
28 Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
av Bebai-sønerne: Johanan, Hananja, Zabbai, Atlai;
29 Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
av Bani-sønerne: Mesullam, Malluk og Adaja, Jasub, Seal og Jeremot;
30 Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
av Pahat-Moabs-sønerne: Adna, Kelal, Benaja, Ma’aseja, Mattanja, Besalel, Binnui og Manasse;
31 Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
og Harims-sønerne: Eliezer, Issia, Malkia, Semaja, Simeon,
32 Benyamin, Malluk da Shemariya.
Benjamin, Malluk, Semarja;
33 Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
av Hasums-sønerne: Mattenai, Mattatta, Sabad, Elifelet, Jeremai, Manasse, Sime’i;
34 Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
av Bani-sønerne: Ma’adai, Amram og Uel,
35 Benahiya, Bedeya, Keluhi,
Benaja, Bedeja, Keluhi,
36 Baniya, Meremot, Eliyashib,
Vanja, Meremot, Eljasib,
37 Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
Mattanja, Mattenai og Ja’asu,
38 Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
Bani, Binnui, Sime’i,
39 Shelemiya, Natan, Adahiya,
og Selemja, Natan og Adaja,
40 Maknadebai, Shashai, Sharai,
Maknadbai, Sasai, Sarai,
41 Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
Azarel, Selemja, Semarja,
42 Shallum da Amariya da Yusuf.
Sallum, Amarja, Josef;
43 Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
av Nebo-sønerne: Je’iel, Mattitja, Zabad, Zebina, Jaddu, Joel og Benaja.
44 Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.
Alle desse hadde teke framande kvende til konor. Og millom konorne var det sume som hadde fenge born.

< Ezra 10 >