< Ezra 10 >

1 Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
Sementara Ezra berdoa sambil menangis dan mengaku dosa di depan Rumah TUHAN, banyak sekali orang Israel datang berkumpul, baik laki-laki, maupun wanita dan anak-anak. Mereka mengelilinginya sambil menangis keras-keras.
2 Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
Kemudian Sekhanya anak Yehiel dari kaum Elam, berkata kepada Ezra, "Kami berdosa kepada TUHAN karena telah mengawini bangsa asing. Meskipun demikian masih ada harapan bagi Israel.
3 Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
Marilah kita bersumpah kepada Allah, bahwa kita akan mengusir semua wanita itu bersama dengan anak-anak mereka. Kami akan menuruti segala nasihatmu serta nasihat orang-orang lain yang menghormati perintah Allah. Kami akan mentaati Hukum Allah.
4 Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
Engkaulah yang harus bertindak. Kami akan membantu engkau sepenuhnya. Bertindaklah dengan tegas sampai tuntas."
5 Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
Maka mulailah Ezra bertindak. Ia menyuruh imam-imam kepala, orang-orang Lewi dan orang-orang Israel lainnya bersumpah bahwa mereka akan melaksanakan usul Sekhanya itu.
6 Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
Setelah mereka bersumpah, pergilah Ezra dari depan Rumah TUHAN dan masuk ke dalam tempat tinggal Yohanan anak Elyasib dan bermalam di situ. Ia tidak mau makan atau minum karena sedih memikirkan perbuatan orang-orang buangan itu.
7 Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
Kemudian disiarkan sebuah maklumat ke seluruh Yerusalem dan Yehuda kepada semua orang yang telah kembali dari pembuangan, supaya berkumpul di Yerusalem.
8 Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
Barangsiapa tidak datang dalam tiga hari, akan disita seluruh hartanya dan ia tidak lagi dianggap anggota masyarakat. Maklumat itu ditandatangani oleh para pemimpin rakyat.
9 A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
Sesudah tiga hari, pada tanggal dua puluh bulan sembilan, semua orang laki-laki yang tinggal di daerah Yehuda dan Benyamin datang ke Yerusalem dan berkumpul di halaman Rumah TUHAN. Pada waktu itu hujan turun dengan lebatnya. Semua orang menggigil karena dinginnya udara dan juga karena pentingnya pertemuan itu.
10 Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
Kemudian Ezra berdiri dan berbicara kepada mereka. Ia berkata, "Kalian telah berdosa dan menambah kesalahan Israel karena mengawini wanita bangsa asing.
11 Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
Sebab itu, akuilah dosamu kepada TUHAN, Allah yang disembah nenek moyang kita, dan lakukanlah apa yang menyenangkan hati-Nya. Jauhilah orang asing yang tinggal di negeri kita dan usirlah istri-istrimu dari bangsa asing itu."
12 Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
Orang-orang itu menjawab dengan nyaring, "Kami akan menuruti nasihatmu."
13 Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
Lalu kata mereka lagi, "Tetapi yang hadir di sini banyak sekali dan hujan begitu lebat. Kami tidak tahan berdiri di luar begini. Lagipula ini bukan perkara yang dapat diselesaikan dalam satu dua hari, sebab banyak sekali dari kami yang terlibat dalam dosa ini.
14 Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
Izinkanlah para pemimpin kami tinggal di Yerusalem dan mengurus soal itu. Lalu setiap orang di kota-kota kami, yang mempunyai istri dari bangsa asing, harus datang pada waktu yang ditentukan, bersama dengan para pemimpin dan para hakim kotanya masing-masing. Dengan demikian Allah tidak akan marah lagi kepada kita karena perkara itu."
15 Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
Tidak seorang pun mengajukan keberatan terhadap rencana itu, kecuali Yonatan anak Asael dan Yahzeya anak Tikwa, disokong oleh dua orang Lewi, yaitu Mesulam dan Sabetai.
16 Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
Orang-orang buangan yang telah kembali itu tetap hendak menjalankan rencana itu, sebab itu Imam Ezra memilih beberapa orang di antara kepala-kepala kaum, lalu mencatat nama mereka. Pada tanggal satu bulan sepuluh mereka mulai bersidang untuk menyelidiki perkara itu.
17 A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
Dalam tiga bulan berikutnya berhasillah mereka menyelesaikan pemeriksaan terhadap semua pria yang telah mengawini wanita dari bangsa asing.
18 A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
Inilah daftar dari orang-orang yang mempunyai istri dari bangsa asing: Para Imam, terdaftar dengan kaumnya: Kaum Yesua dengan saudara-saudaranya, anak-anak Yozadak: Maaseya, Eliezer, Yarib dan Gedalya.
19 (Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
Mereka berjanji akan menceraikan istri mereka, lalu mereka mempersembahkan domba jantan untuk kurban pengampunan dosa mereka.
20 Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
Kaum Imer: Hanani dan Zebaja.
21 Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
Kaum Harim: Maaseya, Elia, Semaya, Yehiel dan Uzia.
22 Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
Kaum Pasyhur: Elyoenai, Maaseya, Ismael, Netaneel, Yozabad, dan Elasa.
23 Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
Orang-orang Lewi: Yozabad, Simei, Kelaya (juga disebut Kelita), Petahya, Yuda dan Eliezer.
24 Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
Para penyanyi: Elyasib. Para penjaga pintu gerbang Rumah TUHAN: Salum, Telem dan Uri.
25 Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
Orang-orang Israel yang lain: Kaum Paros: Ramya, Yezia, Malkia, Miyamin, Eleazar, Malkia dan Benaya.
26 Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
Kaum Elam: Matanya, Zakharia, Yehiel, Abdi, Yeremot dan Elia.
27 Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
Kaum Zatu: Elyoenai, Elyasib, Matanya, Yeremot, Zabad dan Aziza.
28 Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
Kaum Bebai: Yohanan, Hananya, Zabai dan Atlai.
29 Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
Kaum Bani: Mesulam, Malukh, Adaya, Yasub, Seal dan Yeramot.
30 Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
Kaum Pahat-Moab: Adna, Kelal, Benaya, Maaseya, Matanya, Bezaleel, Binui dan Manasye.
31 Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
Kaum Harim: Eliezer, Yisia, Malkia, Semaya, Simeon, Benyamin, Malukh dan Semarya.
32 Benyamin, Malluk da Shemariya.
33 Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
Kaum Hasum: Matnai, Matata, Zabad, Elifelet, Yeremai, Manasye dan Simei.
34 Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
Kaum Bani: Maadai, Amram, Uel, Benaya, Bedeya, Keluhu, Wanya, Meremot, Elyasib, Matanya, Matnai, Yaasai,
35 Benahiya, Bedeya, Keluhi,
36 Baniya, Meremot, Eliyashib,
37 Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
38 Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
Kaum Binui: Simei, Selemya, Natan, Adaya, Makhnadbai, Sasai, Sarai, Azareel, Selemya, Semarya, Salum, Amarya dan Yusuf.
39 Shelemiya, Natan, Adahiya,
40 Maknadebai, Shashai, Sharai,
41 Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
42 Shallum da Amariya da Yusuf.
43 Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
Kaum Nebo: Yeiel, Matica, Zabad, Zebina, Yadai, Yoel dan Benaya.
44 Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.
Semua orang itu telah mengawini wanita dari bangsa asing. Maka istri-istri itu diceraikan dan diusir bersama dengan anak-anak mereka.

< Ezra 10 >