< Ezra 10 >

1 Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
A PAU ka Ezera pule ana, a me ka uwe ana, a me ka moe ana imua o ka hale o ke Akua, hoakoakoaia ae la io na la he anaina kanaka nui loa o ka Iseraela, na kane, me na wahine a me na kamalii; no ka mea, he nui loa ka uwe o na kanaka.
2 Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
A olelo mai o Sekania ke keiki a Iehiela, no na mamo a Elama, i mai la ia Ezera, Ua hana hewa makou i ke Akua, a ua lawe makou i na wahine e no na kanaka o ka aina: aka ano, he manaolana no iloko o ka Iseraela no keia mea.
3 Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
Ano hoi, e hoohiki kakou i ko kakou Akua e hookuke aku i na wahine a pau, a me na mea a lakou i hanau ai, e like me ke ao ana a kuu haku, a me ka poe e makau ana i ke kauoha a ko kakou Akua; a e hanaia ia mea ma ke kanawai.
4 Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
E ku ae oe, no ka mea, ia oe no keia mea: o makou pu kekahi me oe; e ikaika oe, a e hana.
5 Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
Alaila ku ae la o Ezera, a hoohiki aku la i na kahuna nui, i na Levi, a me ka Iseraela a pau, e hana lakou e like me keia olelo. A hoohiki iho la lakou.
6 Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
Alaila ku ae la o Ezera mai ke alo mai o ka hale o ke Akua, a komo iloko o ke keena o Iehohanana ke keiki a Eliasiba; a hiki aku ia ilaila, aole ia i ai i ka ai, aole hoi i inu i ka wai; no ka mea, uwe iho la ia no ka hewa o ka poe pio i hoi mai.
7 Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
A hai aku la lakou ma Iuda, a ma Ierusalema i ka poe pio a pau e honluulu lakou ma Ierusalema;
8 Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
A o na mea a pau i hele ole mai i na la ekolu, e like me ke kauoha a na luna, a me ka poe kahiko, e hoolaaia kona waiwai a pau, a e hookaawaleia oia mai ko anaina kanaka aku o ka poe pio i lawe pio ia aku.
9 A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
Alaila hoakoakoaia ae la na kanaka a pau o ka Iuda, a o ka Beniamina i Ierusalema i na la ekolu, i ka iwa o ka malama, a i ka la iwakalua o ka malama; a noho iho la na kanaka a pau ma ke ala o ka hale o ke Akua, e haalulu ana no keia mea, a no ka ua nui.
10 Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
Ku ae la o Ezera ke kahuna, a olelo aku la ia lakou, Ua hana hewa oukou, a ua lawe i na wahine e, e hoomahuahua i ka hala o ka Iseraela.
11 Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
Ano hoi, e hai aku oukou ia Iehova ke Akua o ko oukou poe makua, a e hana i kona makemake; a hookaawale oukou ia oukou iho mai na kanaka o ka aina aku, a mai na wahine e aku.
12 Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
Alaila olelo mai la ka ahakanaka a pau, i mai la me ka leo nui, E like me kau olelo, pela makou e hana aku ai.
13 Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
Aka, ua nui na kanaka, a he manawa ua nui, aole e hiki ia makou ke ku mawaho, a o ka hana, aole ia no ka la hookahi, aole no na la elua; no ka mea, ua nui na mea o makou i hana hewa ma keia mea.
14 Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
Ano hoi, e hoonohoia na luna o ka ahakanaka a pau, a o na mea a pau ma ko kakou mau kulanakauhale i lawe i na wahine e, e hele mai lakou i ka manawa maopopo, a me lakou pu no na lunakahiko o kela kulanakauhale keia kulanakauhale, a me na lunakanawai ona, a e hoohuli ae i ka inaina o ko kakou Akua mai o kakou aku no keia hewa.
15 Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
O Ionatana wale no, ke keiki a Asahela, a o Iahazia ke keiki a Tikeva i noho no keia mea, a o Mesulama, a me Sabetai ka Levi, i kokua mai ia laua.
16 Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
A hana aku la pela ka poe pio i hoi mai. A o Ezera ke kahuna, me na kauaka koikoi o na makua, no ka hale o ko lakou mau makua, o lakou a pau ma ko lakou inoa i hookaawaleia, a noho iho la lakou i ka la mua o ka umi o ka malama e hookolokolo ai i keia mea.
17 A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
A hoopau lakou me na kanaka a pau i lawe i na wahine e, i ka la akahi o ka malama mua.
18 A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
A ua loaa iwaena o na keiki a na kahuna, na mea i lawe i na wahine e; no na mamo a Iesua ke keiki a Iozadaka, a me kona mau hoahanau, o Maaseia, a o Eliezera, o Iariba, a me Gedalia.
19 (Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
A haawi mai lakou i ko lakou mau lima e hookuke aku i ka lakou mau wahine; a kaumaha aku lakou i ka hipakane o ka poe hipa i mohaihala no ko lakou lawehala ana.
20 Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
A no na mamo a Imera; o Hanani, a me Zebadia.
21 Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
A no na mamo a Harima; o Maaseia, o Elia, o Semaia, o Iehiela, a me Uzia.
22 Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
A no na mamo a Pasura; o Elioenai, o Maaseia, o Isemaela, o Nataneela, o Iozabada, a me Elasa.
23 Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
A no na Levi; o Iozabada, o Simei, o Kelaia, (oia o Kelita, ) o Petahia, o Iuda, a me Eliezera.
24 Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
A no ka poe mele; o Aliasiba: a no na kiaipuka; o Saluma, o Telema, a me Uri.
25 Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
A no ka Iseraela hoi; no na mamo a Parosa; o Ramia, o Iezia, o Malekia, Miamina, o Eleazara, o Malekiia, a me Benaia.
26 Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
A no na mamo a Elama; o Matania, o Zekaria, o Iehiela, o Abedi, o Ieremota, a me Elia.
27 Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
A no na mamo a Zatu; o Elioenai, o Eliasiba, o Matania, o Ieremota, o Zabada, a me Aziza.
28 Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
A no na mamo a Bebai; o Iehohanana, o Hanania, o Zabai, a me Atelai.
29 Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
A no na mamo a Bani; o Mesulama, o Maluka, o Adaia, o Iasuba, o Seala, a me Ramota.
30 Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
A no na mamo a Pahata-moaba; o Adena, o Kelala, o Benaia, o Maaseia, o Matania, o Bezaleela, o Binui, a me Manase.
31 Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
A no na mamo a Harima; o Eliezera, o Isiia, o Malekia, o Semaia, o Simeona,
32 Benyamin, Malluk da Shemariya.
O Beniamina, o Maluka, a me Semaria.
33 Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
A no na mamo a Hasuma; o Matenai, o Matata, o Zabada, o Elipeleta, o Ieremai, o Manase, a me Simei.
34 Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
No na mamo a Bani; o Maadai, o Amerama, a me Uela,
35 Benahiya, Bedeya, Keluhi,
O Benaia, o Bedeia, o Kelu,
36 Baniya, Meremot, Eliyashib,
O Vania, o Meremota, o Eliasiba,
37 Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
O Matania, o Matenai, a me Iaasau,
38 Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
A o Bani, o Binui, o Simei,
39 Shelemiya, Natan, Adahiya,
A o Selemia, o Natana, a me Adaia,
40 Maknadebai, Shashai, Sharai,
O Makenadebai, a Sasai, o Seharai,
41 Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
O Azareela, o Selemia, o Semaria,
42 Shallum da Amariya da Yusuf.
O Saluma, o Amaria, o Iosepa.
43 Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
No na mamo a Nebo; o Ieiela, o Matitia, o Zabada, o Zebina, o Iadau, o Ioela, o Benaia.
44 Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.
O keia mau mea a pau, ua lawe lakou i na wahine e; a o na wahine a kekahi poe o lakou ua hanau keiki na lakou.

< Ezra 10 >