< Ezra 10 >

1 Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
Pendant qu'Esdras priait et se confessait, pleurant et se prosternant devant la maison de Dieu, une très grande assemblée d'hommes, de femmes et d'enfants s'assembla auprès de lui de la part d'Israël, car le peuple pleurait très amèrement.
2 Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
Shecania, fils de Jehiel, l'un des fils d'Élam, répondit à Esdras: « Nous avons péché contre notre Dieu et nous avons épousé des femmes étrangères parmi les peuples du pays. Mais maintenant, il y a de l'espoir pour Israël à ce sujet.
3 Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
Maintenant, faisons donc alliance avec notre Dieu pour répudier toutes les femmes et celles qui sont nées d'elles, selon le conseil de mon seigneur et de ceux qui tremblent devant l'ordre de notre Dieu. Qu'il en soit fait selon la loi.
4 Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
Lève-toi, car l'affaire est entre tes mains et nous sommes avec toi. Prends courage, et fais-le. »
5 Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
Alors Esdras se leva et fit jurer aux chefs des prêtres, aux lévites et à tout Israël qu'ils feraient selon cette parole. Et ils jurèrent.
6 Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
Esdras se leva de devant la maison de Dieu et entra dans la chambre de Jehohanan, fils d'Eliashib. Quand il y arriva, il ne mangea pas de pain et ne but pas d'eau, car il était en deuil à cause de la faute des exilés.
7 Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
On publia dans tout Juda et Jérusalem une annonce à tous les enfants de la captivité, pour qu'ils se rassemblent à Jérusalem,
8 Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
et que quiconque ne viendrait pas dans les trois jours, selon le conseil des princes et des anciens, perdrait tous ses biens, et serait lui-même séparé de l'assemblée des captifs.
9 A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
Et tous les hommes de Juda et de Benjamin se rassemblèrent à Jérusalem dans les trois jours. C'était le neuvième mois, le vingtième jour du mois; et tout le peuple était assis sur la place large, devant la maison de Dieu, tremblant à cause de cette affaire et à cause de la grande pluie.
10 Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
Le prêtre Esdras se leva et leur dit: « Vous avez commis une faute, vous avez épousé des femmes étrangères, et vous avez aggravé la culpabilité d'Israël.
11 Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
Maintenant, confessez-vous à Yahvé, le Dieu de vos pères, et faites sa volonté. Séparez-vous des peuples du pays et des femmes étrangères. »
12 Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
Alors toute l'assemblée répondit d'une voix forte: « Nous devons faire ce que tu as dit à notre sujet.
13 Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
Mais le peuple est nombreux, et c'est un temps de grande pluie, et nous ne pouvons pas rester dehors. Ce n'est pas l'œuvre d'un jour ou deux, car nous avons beaucoup transgressé dans cette affaire.
14 Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
Maintenant, que nos chefs soient désignés pour toute l'assemblée, et que tous ceux qui sont dans nos villes et qui ont épousé des femmes étrangères viennent à des heures fixes, et avec eux les anciens de chaque ville et ses juges, jusqu'à ce que l'ardente colère de notre Dieu se détourne de nous, jusqu'à ce que cette affaire soit résolue. »
15 Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
Seuls Jonathan, fils d'Asahel, et Jahzeia, fils de Tikva, s'y opposèrent; Meshullam et Shabbethai, le Lévite, les aidèrent.
16 Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
Les enfants de la captivité firent ainsi. Le prêtre Esdras, avec certains chefs de famille, selon les maisons de leurs pères, et tous selon leurs noms, furent mis à part; ils s'assirent le premier jour du dixième mois pour examiner la question.
17 A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
Ils en finirent avec tous les hommes qui avaient épousé des femmes étrangères, le premier jour du premier mois.
18 A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
Parmi les fils des prêtres, il s'en trouvait qui avaient épousé des femmes étrangères: des fils de Jeshua, fils de Jozadak, et de ses frères: Maaséja, Éliézer, Jarib et Guedalia.
19 (Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
Ils donnèrent leur main pour répudier leurs femmes; et, étant coupables, ils offrirent un bélier du troupeau pour leur faute.
20 Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
Des fils d'Immer: Hanani et Zebadiah.
21 Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
Des fils de Harim: Maaséja, Élie, Shemahia, Jehiel et Ozias.
22 Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
Des fils de Pashhur: Elioénaï, Maaséja, Ismaël, Nethanel, Jozabad et Elasah.
23 Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
Parmi les Lévites: Jozabad, Shimei, Kelaiah (appelé aussi Kelita), Pethahiah, Juda et Eliezer.
24 Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
Des chanteurs: Eliashib. Des gardiens: Shallum, Telem, et Uri.
25 Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
D'Israël: Des fils de Parosh: Ramia, Izzia, Malkija, Mijamin, Eléazar, Malkija et Benaja.
26 Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
Des fils d'Elam: Mattania, Zacharie, Jehiel, Abdi, Jeremoth et Élie.
27 Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
Des fils de Zattu: Eliœnai, Eliashib, Mattaniah, Jeremoth, Zabad et Aziza.
28 Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
Des fils de Bébaï: Jehohanan, Hanania, Zabbai et Athlaï.
29 Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
Des fils de Bani: Meshullam, Malluch, Adaiah, Jashub, Sheal et Jeremoth.
30 Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
Des fils de Pahathmoab: Adna, Chelal, Benaiah, Maaseiah, Mattaniah, Bezalel, Binnui et Manassé.
31 Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
Des fils de Harim: Éliézer, Ischija, Malkija, Schemaeja, Shimeon,
32 Benyamin, Malluk da Shemariya.
Benjamin, Malluch et Shemaria.
33 Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
Des fils de Hashum: Mattenai, Mattattah, Zabad, Eliphelet, Jeremai, Manasseh et Shimei.
34 Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
Des fils de Bani: Maadaï, Amram, Uel,
35 Benahiya, Bedeya, Keluhi,
Benaja, Bedeja, Cheluhi,
36 Baniya, Meremot, Eliyashib,
Vania, Meremoth, Eliashib,
37 Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
Mattania, Mattenai, Jaasu,
38 Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
Bani, Binnui, Shimei,
39 Shelemiya, Natan, Adahiya,
Shelemiah, Nathan, Adaiah,
40 Maknadebai, Shashai, Sharai,
Machnadebai, Shashai, Sharai,
41 Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
Azarel, Shelemiah, Shemariah,
42 Shallum da Amariya da Yusuf.
Shallum, Amaria, et Joseph.
43 Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
Des fils de Nebo: Jeiel, Mattithiah, Zabad, Zebina, Iddo, Joël et Benaja.
44 Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.
Tous ceux-là avaient pris des femmes étrangères. Certains d'entre eux avaient des femmes dont ils avaient des enfants.

< Ezra 10 >