< Ezra 10 >

1 Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
While I was kneeling down in front of the temple and praying and crying, I was confessing [the sins that the Israeli people had committed]. Many people, men and women and children, gathered around me and also cried very much.
2 Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
Then Shecaniah, the son of Jehiel from the clan of Elam, said this to me: “We have disobeyed God. [Some of] us have married women who are not Israelis. But we can still confidently expect [Yahweh to be merciful to] us Israeli people.
3 Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
We will do what you, and the others who have an awesome respect for what our God has commanded, tell us to do. We will do what God told us in his laws. We will make an agreement with our God, saying that we will divorce our wives who are not Israelis, and we will send them away with their children.
4 Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
(It is your responsibility to/Because you are our leader, you must) [tell us what to do]. So get up, and be courageous, and do [what is necessary]. We will (support you/tell people to do what you say).”
5 Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
So I stood up and demanded that the leaders of the priests, the [other] descendants of Levi, and all [the other] Israeli people solemnly declare that they would do what Shecaniah said that they should do. So they all solemnly promised to do that.
6 Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
Then I went away from the front of the temple and went to the room where Jehohanan lived. I stayed there that night, but I did not eat or drink anything. I was still sad because some of the Israelis who had returned [from Babylonia] had not faithfully obeyed [God’s laws].
7 Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
Then we sent a message to all [the people in] Jerusalem and [in other towns in] Judah, saying that all those who had returned [from Babylonia] should come to Jerusalem immediately.
8 Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
We said that if any of them did not arrive within three days, the leaders of the people would order that all the property of those people would be taken from them, and that they would no longer be considered to belong to the Israeli people; [they would be considered to be foreigners].
9 A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
So within three days, on December 19, all the people of the tribes of Judah and Benjamin gathered in Jerusalem. They were there, sitting in the courtyard in front of the temple. They were trembling because it was raining hard and because they were worried [that they would be punished for what they had done].
10 Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
Then I stood up and said to them, “[Some of] you men have committed a very bad sin. You have married women who are not Israelis. By doing that, you have made us Israeli people more guilty [than we were before].
11 Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
So now you must confess to Yahweh, the God whom your ancestors [worshiped/belonged to], the sin which you have committed, and you must do what he wants. Separate yourselves from the people of other nations and from the women from those nations whom you have married.”
12 Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
The whole group answered, shouting loudly, “Yes, what you have said is right! We will do what you have said.”
13 Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
But then [one of] them said, “But we are a very large group, and it is raining hard. Also, there are many of us who have committed this bad sin. This is something that we cannot (take care of/handle) in one or two days, and we cannot stand here in this rain.
14 Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
So allow our leaders to decide for all of us what we should do. Tell everyone who has married a woman who is not Israeli to come at a time that you decide. They should come with the elders and judges from each city. If we do that, our God will stop being angry with us [because of what we have done].”
15 Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
Jonathan the son of Asahel, Jahzeiah the son of Tikvah, Meshullam, and Shabbethai, a descendant of Levi, were the only ones who objected to this.
16 Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
All the others who had returned from Babylonia said that they would do it. So I chose leaders of each of the clans, and I wrote down their names. On December 29, these men came and sat down to investigate the matter.
17 A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
By March 27 of the next year they finished determining which men had married women who were not Israelis.
18 A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
This is a list of the names of the priests who had married non-Israeli women, and the clans to which they belonged. From the clan of Jeshua and his brothers, who were sons of Jehozadak, there were Maaseiah, Eliezer, Jarib, and Gedaliah.
19 (Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
They solemnly promised to divorce their wives, and they each sacrificed a ram to be an offering [to atone] for their sins.
20 Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
From the clan of Immer there were Hanani and Zebadiah.
21 Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
From the clan of Harim there were Maaseiah, Elijah, Shemaiah, Jehiel, and Uzziah.
22 Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
From the clan of Pashhur there were Elioenai, Maaseiah, Ishmael, Nethanel, Jozabad, and Elasah.
23 Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
The [other] descendants of Levi [who had married non-Israeli women] were Jozabad, Shimei, Kelaiah (whose other name was Kelita), Pethahiah, Judah, and Eliezer.
24 Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
There was Eliashib the musician. From the temple guards there were Shallum, Telem, and Uri.
25 Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
This is a list of the names of the other Israelis who had married foreign wives: From the clan of Parosh there were Ramiah, Izziah, Malchijah, Mijamin, Eleazar, Hashabiah, and Benaiah.
26 Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
From the clan of Elam there were Mattaniah, Zechariah, Jehiel, Abdi, Jeremoth, and Elijah.
27 Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
From the clan of Zattu there were Elioenai, Eliashib, Mattaniah, Jeremoth, Zabad, and Aziza.
28 Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
From the clan of Bebai there were Jehohanan, Hananiah, Zabbai, and Athlai.
29 Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
From the clan of Bani there were Meshullam, Malluch, Adaiah, Jashub, Sheal, and Jeremoth.
30 Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
From the clan of Pahath-Moab there were Adna, Kelal, Benaiah, Maaseiah, Mattaniah, Bezalel, Binnui, and Manasseh.
31 Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
From the clan of Harim there were Eliezer, Ishijah, Malkijah, Shemaiah, Shimeon,
32 Benyamin, Malluk da Shemariya.
Benjamin, Malluch, and Shemariah.
33 Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
From the clan of Hashum there were Mattenai, Mattattah, Zabad, Eliphelet, Jeremai, Manasseh, and Shimei.
34 Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
From the clan of Bigvai there were Maadai, Amram, Uel,
35 Benahiya, Bedeya, Keluhi,
Benaiah, Bedeiah, Keluhi,
36 Baniya, Meremot, Eliyashib,
Vaniah, Meremoth, Eliashib,
37 Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
Mattaniah, Mattenai, and Jaasu.
38 Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
From the clan of Binnui there were Shimei,
39 Shelemiya, Natan, Adahiya,
Shelemiah, Nathan, Adaiah,
40 Maknadebai, Shashai, Sharai,
Macnadebai, Shashai, Sharai,
41 Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
Azarel, Shelemiah, Shemariah,
42 Shallum da Amariya da Yusuf.
Shallum, Amariah, and Joseph.
43 Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
From the clan of Nebo there were Jeiel, Mattithiah, Zabad, Zebina, Jaddai, Joel, and Benaiah.
44 Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.
Each of those men had married a woman who was not an Israeli. [But immediately] they divorced those women and sent them and their children away.

< Ezra 10 >