< Ezra 10 >

1 Yayinda Ezra yake addu’a, yake kuma furta laifi, yana kuka, yana a durƙushe da kansa ƙasa a gaban gidan Allah, sai babban taron jama’ar Isra’ilawa, maza, mata da yara, suka taru a wurinsa. Su ma suka yi kuka mai zafi.
Now while Ezra was making his prayer and his statement of wrongdoing, weeping and falling down before the house of God, a very great number of men and women and children out of Israel came together round him: for the people were weeping bitterly.
2 Sai Shekaniya ɗan Yehiyel, daga zuriyar Elam ya ce wa Ezra, “Mun yi wa Allah rashin aminci ta wurin yin auratayya da maƙwabtanmu, amma duk da haka bai yashe mutanen Isra’ila ba.
And Shecaniah, the son of Jehiel, one of the sons of Elam, answering, said to Ezra, We have done evil against our God, and have taken as our wives strange women of the peoples of the land: but still there is hope for Israel in this question.
3 Yanzu bari mu yi alkawari da Allahnmu, mu kori matan da yaransu bisa ga abin da ranka yă daɗe da sauran shugabannin da kuke girmama umarnin Allah kuka shawarce mu, bari mu yi haka bisa ga doka.
Let us now make an agreement with our God to put away all the wives and all their children, if it seems right to my lord and to those who go in fear of the words of our God; and let it be done in keeping with the law.
4 Sai ka tashi, gama wannan hakkinka ne, za mu ba ka goyon baya. Saboda haka ka yi ƙarfin hali ka aikata shi.”
Up, now! for this is your business, and we are with you; take heart and do it.
5 Sai Ezra ya tashi ya sa firistoci da suke shugabanni, da Lawiyawa, da dukan mutanen Isra’ila su rantse, cewa za su yi abin da aka ce. Sai suka yi rantsuwar.
Then Ezra got up, and made the chiefs of the priests and the Levites and all Israel take an oath that they would do this. So they took an oath.
6 Sa’an nan Ezra ya tashi daga gidan Allah ya tafi gidan Yehohanan ɗan Eliyashib, a can ma bai ci wani abu ba, bai sha ruwa ba domin ya ci gaba da yin baƙin cikin rashin aminci na waɗanda suka dawo daga bauta.
Then Ezra got up from before the house of God and went into the room of Jehohanan, the son of Eliashib; but when he came there, he took no food or drink, for he was sorrowing for the sin of those who had come back.
7 Aka yi shela a duk fāɗin Yahuda da Urushalima cewa dukan waɗanda suka dawo daga bauta su tattaru a Urushalima.
And they made a public statement through all Judah and Jerusalem, to all those who had come back, that they were to come together to Jerusalem;
8 Duk wanda bai zo a cikin kwana uku ba, za a washe shi, a kuma ware shi daga jama’ar da suka dawo daga bauta. Haka shugabanni da dattawa suka zartar.
And that if anyone did not come before three days were past, as ordered by the rulers and the responsible men, all his goods would be put under the curse, and he himself would be cut off from the meeting of the people who had come back.
9 A cikin kwana uku duk mutanen Yahuda da na Benyamin suka taru a Urushalima. A ranar ashirin ga watan tara, dukan mutanen suka zauna a dandali a gaban gidan Allah cike da ɓacin rai saboda abin da ya faru da kuma ruwan da aka yi.
Then all the men of Judah and Benjamin came together to Jerusalem before three days were past; it was the ninth month, on the twentieth day of the month; and all the people were seated in the wide square in front of the house of God, shaking with fear because of this business and because of the great rain.
10 Sai Ezra firist ya miƙe tsaye ya yi musu magana ya ce, “Kun yi rashin aminci; kun aure mata baƙi, ta haka kuka ƙara kan zunubin Isra’ila.
And Ezra the priest got to his feet and said to them, You have done wrong and taken strange women for your wives, so increasing the sin of Israel.
11 Yanzu sai ku furta zunubanku ga Ubangiji, Allahn kakanninku, ku kuma yi nufinsa. Ku raba kanku da mutanen da suke kewaye da ku, ku kuma rabu da baƙin mata.”
So now, give praise to the Lord, the God of your fathers, and do his pleasure; and make yourselves separate from the peoples of the land and from the strange women.
12 Mutanen kuwa suka tā da murya da ƙarfi suka ce, “Gaskiya ka faɗa, dole mu yi yadda ka ce,
Then all the people, answering, said with a loud voice, As you have said, so it is right for us to do.
13 Amma akwai mutane da yawa, kuma lokacin damina ne; saboda haka ba za mu iya tsayawa a waje ba. Ban da haka ma, aikin nan ba na kwana ɗaya ko biyu ba ne, domin ba ƙaramin laifi muka yi ba.
But the number of people is great, and it is a time of much rain; it is not possible for us to go on waiting outside, and this is not a thing which may be done in one day or even two: for our sin in this business is great.
14 Bari shugabanninmu su yi wani abu a madadin mutane duka, sa’an nan sai duk wanda ya san ya auri baƙuwar mace a garuruwanmu, sai yă zo nan a lokacin da aka shirya tare da dattawa da alƙalan kowane gari, har sai Allah ya huce fushinsa mai zafi da yake kanmu.”
So now let our rulers be representatives for all the people, and let all those in our towns who are married to strange women come at fixed times, and with them the responsible men and the judges of every town, till the burning wrath of our God is turned away from us, and this has been done.
15 Yonatan ɗan Asahel, da Yazehiya ɗan Tikba su ne kaɗai ba su yarda da wannan shirin ba, sai Meshullam da Shabbetai Balawe kuma suka goyi bayansu.
Only Jonathan, the son of Asahel, and Jahzeiah, the son of Tikvah, were against this, Meshullam and Shabbethai the Levite supporting them.
16 Sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi yadda aka zartar. Ezra firist ya zaɓi mutane waɗanda su ne shugabannin iyalai, ɗaya daga kowane sashe, aka rubuta sunan kowannensu. A ranar ɗaya ga watan goma kuwa suka zauna don su yi binciken waɗannan abubuwa.
So those who had come back did so. And Ezra the priest, with certain heads of families, by their fathers' families, all of them by their names, were marked out; and on the first day of the tenth month they took their places to go into the question with care.
17 A rana ta farko ga watan farko, suka gama da bincike duk waɗanda suka auri baƙin mata.
And they got to the end of all the men who were married to strange women by the first day of the first month.
18 A cikin zuriyar firistoci, ga waɗanda suka auri mata baƙi. Daga zuriyar Yeshuwa ɗan Yozadak da’yan’uwansa, akwai Ma’asehiya, da Eliyezer, da Yarib, da Gedaliya.
And among the sons of the priests who were married to strange women were these: of the sons of Jeshua, the son of Jozadak and his brothers, Maaseiah and Eliezer and Jarib and Gedaliah.
19 (Su ne suka miƙa hannuwansu suka nuna sun yarda su kori matansu baƙi, kowannensu kuma ya ba da rago daga cikin garkensa don a miƙa hadaya don zunubi.)
And they gave their word that they would put away their wives; and for their sin, they gave an offering of a male sheep of the flock.
20 Daga zuriyar Immer, akwai Hanani da Zebadiya.
And of the sons of Immer, Hanani and Zebadiah.
21 Daga zuriyar Harim, akwai Ma’asehiya, Iliya, Shemahiya, Yehiyel da Uzziya.
And of the sons of Harim, Maaseiah and Elijah and Shemaiah and Jehiel and Uzziah.
22 Daga zuriyar Fashhur, akwai Eliyohenai, Ma’asehiya, Ishmayel, Netanel, Yozabad da Eleyasa.
And of the sons of Pashhur, Elioenai, Maaseiah, Ishmael, Nethanel, Jozabad, and Elasah.
23 Cikin Lawiyawa, akwai Yozabad, Shimeyi, Kelaya (wato, Kelita), Fetahahiya, Yahuda, Eliyezer.
And of the Levites, Jozabad, and Shimei, and Kelaiah (that is Kelita), Pethahiah, Judah, and Eliezer.
24 Daga mawaƙa, akwai Eliyashib. Daga masu tsaron ƙofofin haikali, akwai Shallum, Telem da Uri.
And of the music-makers, Eliashib; and of the door-keepers, Shallum and Telem and Uri.
25 Ga sunayen sauran mutanen Isra’ilan da suke da wannan laifi. Daga zuriyar Farosh, akwai Ramiya, da Izziya, Malkiya, Miyamin, Eleyazar, Malkiya da Benahiya.
And of Israel, the sons of Parosh, Ramiah and Izziah and Malchijah and Mijamin and Eleazar and Malchijah and Benaiah.
26 Daga zuriyar Elam, akwai Mattaniya, Zakariya, Yehiyel, Abdi, Yeremot, da Iliya.
And of the sons of Elam, Mattaniah, Zechariah, and Jehiel and Abdi and Jeremoth and Elijah.
27 Daga iyalin Zattu, akwai Eliyohenai, Eliyashib, Mattaniya Yeremot da Zabad da Aziza.
And of the sons of Zattu, Elioenai, Eliashib, Mattaniah, and Jeremoth and Zabad and Aziza.
28 Daga zuriyar Bebai, akwai Yehohanan, Hananiya, Zabbai, da Atlai.
And of the sons of Bebai, Jehohanan, Hananiah, Zabbai, Athlai.
29 Daga zuriyar Bani, akwai Meshullam, Malluk, Adahiya, Yashub, Sheyal, da Ramot.
And of the sons of Bani, Meshullam, Malluch, and Adaiah, Jashub and Sheal, Jeremoth.
30 Daga zuriyar Fahat-Mowab, akwai Adna, Kelal, Benahiya, Ma’asehiya, Mattaniya, Bezalel, Binnuyi, da Manasse.
And of the sons of Pahath-moab, Adna and Chelal, Benaiah, Maaseiah, Mattaniah, Bezalel and Binnui and Manasseh.
31 Daga zuriyar Harim, akwai Eliyezer, Isshiya, Malkiya, Shemahiya, Simeyon,
And of the sons of Harim, Eliezer, Isshijah, Malchijah, Shemaiah, Shimeon,
32 Benyamin, Malluk da Shemariya.
Benjamin, Malluch, Shemariah.
33 Daga zuriyar Hashum, akwai Mattenai, da Mattatta, Zabad, Elifelet, Irmai, Manasse, da Shimeyi.
Of the sons of Hashum, Mattenai, Mattattah, Zabad, Eliphelet, Jeremai, Manasseh, Shimei.
34 Daga zuriyar Bani, akwai Ma’adai, Amram, Yuwel,
Of the sons of Bani, Maadai, Amram, and Uel,
35 Benahiya, Bedeya, Keluhi,
Benaiah, Bedeiah, Cheluhi,
36 Baniya, Meremot, Eliyashib,
Vaniah, Meremoth, Eliashib,
37 Mattaniya, Mattenai da Ya’asu.
Mattaniah, Mattenai, and Jaasu,
38 Daga zuriyar Binnuyi, akwai Shimeyi,
And Bani and Binnui, Shimei;
39 Shelemiya, Natan, Adahiya,
And Shelemiah and Nathan and Adaiah,
40 Maknadebai, Shashai, Sharai,
Machnadebai, Shashai, Sharai,
41 Azarel, Shelemiya, da Shemariya,
Azarel and Shelemiah, Shemariah,
42 Shallum da Amariya da Yusuf.
Shallum, Amariah, Joseph.
43 Daga zuriyar Nebo, akwai Yehiyel, Mattitiya, Zabad, Zebina, Yaddai, Yowel da Benahiya.
Of the sons of Nebo, Jeiel, Mattithiah, Zabad, Zebina, Iddo, and Joel, Benaiah.
44 Dukan waɗannan sun auri baƙin mata, waɗansunsu suna da’ya’ya.
All these had taken strange wives; and some of them had wives by whom they had offspring.

< Ezra 10 >