< Ezekiyel 1 >

1 A shekara ta talatin, a wata na huɗu a rana biyar, yayinda nake cikin’yan zaman bauta kusa da Kogin Kebar, sai sammai suka buɗe na kuwa ga wahayoyin Allah.
Now it came to pass in the thirtieth year, in the fourth month, in the fifth day of the month, as I was among the captives by the river Chebar, that the heavens were opened, and I saw visions of God.
2 A rana biyar ga wata, a shekara ta biyar ne ta zaman bautan Sarki Yehohiyacin,
On the fifth day of the month, in the fifth year of the captivity of King Jehoiachin,
3 maganar Ubangiji ta zo wa Ezekiyel firist, ɗan Buzi, kusa da Kogin Kebar a ƙasar Babiloniyawa. A can hannun Ubangiji yana a kansa.
the word of Jehovah came to Ezekiel, the son of Buzi, the priest, in the land of the Chaldaeans, by the river Chebar; and the hand of Jehovah was there upon him.
4 Na duba, sai na ga guguwa ta taso daga arewa babban hadari cike da walƙiya kewaye da haske mai haske sosai. Tsakiyar wutar ta yi kamar ƙarfe mai cin wuta balbal,
And I looked, and behold, a stormy wind came from the north, a great cloud, and a mass of fire; and a brightness was round about it, and in the midst of it the appearance of bright brass, in the midst of the fire.
5 a cikin wutar kuwa akwai abin da ya yi kamar halittu guda huɗu. A bayyane kamanninsu ya yi kamar siffar mutum,
And in the midst of it were the forms of four living creatures. And this was their appearance. They had the form of a man.
6 amma kowannensu yana da fuskoki huɗu da fikafikai guda huɗu.
And every one had four faces, and every one had four wings.
7 Ƙafafunsu miƙaƙƙu ne; kuma ƙafafunsu sun yi kamar na maraƙi suna kuma walƙiya kamar tagullar da aka goge.
And their feet were upright; and the sole of their feet was as the sole of a calf's foot; and they sparkled like polished brass.
8 A ƙarƙashin fikafikansu huɗu suna da hannuwan mutum a kowane gefe. Dukansu huɗu suna da fuskoki da fikafikai,
And they had the hands of a man under their wings on their four sides, and all four had faces and wings.
9 kuma fikafikansu suna taɓan juna. Kowanne ya miƙe gaba; ba sa juyawa sa’ad da suke tafiya.
Their wings were joined one to another; they turned not about when they went; they went every one straight forward.
10 Fuskokinsu sun yi kamar haka. Kowanne a cikin huɗun yana da fuskar mutum, kuma a gefen dama kowanne yana da fuskar zaki, a hagu kuma fuskar maraƙi; kowanne yana kuma da fuskar gaggafa.
As for the form of their faces, all four had the face of a man, and the face of a lion on the right side, and all four had the face of an ox on the left side, and all four had also the face of an eagle.
11 Haka fuskokinsu suka kasance. Fikafikansu sun buɗu sama; kowanne yana da fikafikai biyu, ɗaya yana taɓa fikafikan ɗayan halittar a ɗayan gefe, fikafikai biyu kuma suna rufe jikinsa.
Thus were their faces. And their wings were expanded upward; two wings of every one were joined, and two covered their bodies.
12 Kowanne ya miƙe gaba sosai. Duk inda ruhu zai tafi, can za su, ba tare da juyawa ba yayinda suke tafiya.
And they went every one straight forward; whither the spirit was to go, they went, and they turned not about when they went.
13 Kamannin halittun ya yi kamar garwashi mai cin wuta ko kuwa kamar fitilu. Wuta tana kai da kawowa a cikin halittun; ta yi haske ƙwarai, walƙiya kuma tana wulgawa daga cikinta.
And the appearance of the living creatures was as coals of fire, burning like torches; and the fire moved about among the living creatures, and shone forth brightly; and out of the fire came forth lightning.
14 Halittun suna gaggauta kai da kawowa kamar walƙiya.
And the living creatures ran backward and forward like a flash of lightning.
15 Yayinda nake kallon rayayyun halittun nan, sai na ga da’ira a ƙasa kusa da kowace halitta da fuskokinsa huɗu.
Now as I beheld the living creatures, behold, there stood a wheel upon the earth by each of the living creatures, with its four sides.
16 Ga kamanni da fasalin da’irorin. Suna ƙyalƙyali kamar kirisolit, kuma dukan huɗun sun yi kama da juna. Kowacce ta yi kamar da’ira a cikin da’ira.
The appearance of the wheels, and their work, was like that of a chrysolite, and all four had one form, and their appearance and their work was as if a wheel had been within a wheel.
17 Yayinda suke tafiya, sukan nufi duk wani gefe guda cikin gefe huɗun da halittun suka nufa; da’irorin ba za su juya ba sa’ad da halittun suke tafiya.
When they went, they went upon their four sides, and they turned not about when they went.
18 Ƙarafansu da suka yi kamar zobe sun yi tsayi suna kuma da bantsoro, dukan ƙarafan nan huɗu kuwa da suka yi kamar zobe suna cike da idanu a kewaye.
As for their felloes, they were high and terrible; and their felloes were full of eyes round about upon all four of them.
19 Sa’ad da rayayyun halittun suke tafiya, da’irorin da suke kusa da su kan motsa; kuma sa’ad da rayayyun halittun sun tashi sama, da’irorin su ma sukan tashi sama.
And when the living creatures went, the wheels went beside them; and when the living creatures were lifted up from the earth, the wheels were lifted up.
20 Duk inda ruhu za shi, su ma can za su, kuma da’irorin za su tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun nan yana a cikin da’irorin.
Whithersoever the spirit was to go, they went, whithersoever the spirit was to go; and the wheels were lifted up beside them; for the spirit of the living creatures was in the wheels.
21 Sa’ad da halittun sun motsa, sai su ma su motsa; sa’ad da halittun sun tsaya cik, su ma sai su tsaya cik, sa’ad da kuma halittun sukan tashi sama, da’irorin suka tashi tare da su, domin ruhun rayayyun halittun nan yana a cikin da’irorin.
When those went, these went; and when those stood, these stood; and when those were lifted up from the earth, the wheels were lifted up beside them; for the spirit of the living creatures was in the wheels.
22 A bisa kawunan rayayyun halittun nan akwai abin da ya yi kamar ƙanƙara, mai bantsoro.
And over the heads of the living creatures was the appearance of a firmament, like crystal, terrible, spread out over their heads above.
23 A ƙarƙashin al’arshin fikafikansu sun miƙe kyam ɗaura da juna, kuma kowanne yana da fikafikai biyu da suka rufe jikinsa.
And under the firmament were their wings upright, the one toward the other; and every one had two, which covered his body.
24 Sa’ad da halittun suke tafiya, sai na ji ƙarar fikafikansu, kamar rurin ruwaye masu gudu, kamar muryar Maɗaukaki, kamar hayaniyar rundunar mayaƙa. In sun tsaya cik, sukan sauko da fikafikansu.
And I heard the sound of their wings, as the sound of great waters, as the voice of the Almighty, when they went, —a sound like the noise of a host. And when they stood still, they let down their wings.
25 Sai aka ji murya daga al’arshi a kan kawunansu yayinda suke tsaye da fikafikansu a sauke.
And there was a voice from the firmament, that was over their heads; and they stood still, and let down their wings.
26 A bisa al’arshin a kan kawunansu akwai abin da ya yi kamar saffaya, kuma a can bisa a kan kursiyin akwai siffa kamar na mutum.
And above the firmament over their heads was an appearance like a sapphire-stone, the form of a throne; and upon the form of the throne there was a form like that of a man above.
27 Na ga daga abin da ya yi kamar kwankwasonsa zuwa bisa ya yi kamar ƙarfe mai walƙiya, sai ka ce wuta, kuma daga kwankwasonsa zuwa ƙasa ya yi kamar wuta; haske kuma mai walƙiya sosai kewaye da shi.
And I saw what had the appearance of bright brass, what had the appearance of fire round about within it, from the appearance of his loins and upward. And from the appearance of his loins downward I saw what had the appearance of fire, and its brightness was round about him.
28 Kamar kamannin bakan gizo a cikin gizagizai a ranar da aka yi ruwan sama, haka hasken da ya kewaye shi. Wannan shi ne kwatancin kamannin ɗaukakar Ubangiji. Sa’ad da na gani, sai na fāɗi rubda ciki, na kuma ji muryar wani tana magana.
As the appearance of the bow that is in the cloud in the day of rain, so was the appearance of the brightness round about. This was the appearance of the glory of Jehovah. And when I saw it I fell upon my face, and I heard the voice of one who spoke.

< Ezekiyel 1 >