< Ezekiyel 9 >

1 Sai na ji ya yi kira da babbar murya yana cewa, “Kawo matsaran birni a nan, kowanne da makami a hannunsa.”
Então ele gritou em meus ouvidos com uma voz alta, dizendo: “Porque aqueles que estão no comando da cidade se aproximem, cada homem com sua arma destruidora na mão”.
2 Na kuma ga mutane shida suna zuwa daga kowane gefen ƙofar ta bisa, wadda take fuskantar arewa, kowanne da makamin kisa a hannunsa. Tare da su akwai mutum saye da lilin yana rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa. Suka shiga suka tsaya kusa da bagaden tagulla.
Eis que seis homens vieram do caminho do portão superior, que fica ao norte, cada homem com a sua arma de matança na mão. Um homem no meio deles estava vestido de linho, com um tinteiro de escritor ao seu lado. Eles entraram, e ficaram ao lado do altar de bronze.
3 To, fa, ɗaukakar Allah na Isra’ila ta haura daga bisa kerubobi, inda ta kasance, ta tashi zuwa bakin madogarar ƙofar haikali. Sai Ubangiji ya kira mutumin da yake saye da lilin wanda ya rataye jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa
A glória do Deus de Israel subiu do querubim, onde estava até a soleira da casa; e ele chamou o homem vestido de linho, que tinha o tinteiro do escritor ao seu lado.
4 ya ce masa, “Ka ratsa birnin Urushalima ka sa shaida a goshin waɗanda suke baƙin ciki da kuma makoki a kan dukan abubuwan banƙyamar da ake yi a cikinsa.”
Yahweh disse-lhe: “Passe pelo meio da cidade, pelo meio de Jerusalém, e ponha uma marca na testa dos homens que suspiram e que choram sobre todas as abominações que são feitas dentro dela”.
5 Yayinda nake saurara, sai ya ce wa waɗansu, “Ku bi shi ta birnin ku kuma kashe, babu tausayi ko kuwa jinƙai.
Para os outros ele disse em minha audiência: “Vá pela cidade depois dele, e faça greve”. Não deixe que seu olho poupe, nem tenha piedade”.
6 Ku kashe tsofaffi da samari da’yan mata, mata da yara, amma kada ku taɓa wani wanda yake da shaida. Ku fara a wuri mai tsarkina.” Saboda haka suka fara da dattawan da suke gaban haikali.
Matem totalmente o homem velho, o jovem, a virgem, as crianças pequenas e as mulheres; mas não se aproximem de nenhum homem em quem a marca seja a marca. Comece em meu santuário”. Então eles começaram nos velhos que estavam antes da casa.
7 Sa’an nan ya ce musu, “Ku ƙazantar da haikalin ku kuma cika filayen da kisassu. Ku tafi!” Saboda haka suka fita suka kuma fara kisa a duk birnin.
Ele lhes disse: “Desonrei a casa e encherei os tribunais com os mortos”. Saiam”! Eles saíram, e atacaram na cidade.
8 Yayinda suke kisan sai aka bar ni kaɗai, na fāɗi rubda ciki, na yi kuka na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka dukan raguwar Isra’ila a wannan zafin fushinka a Urushalima?”
Enquanto matavam, e eu fiquei, caí de cara, chorei e disse: “Ah Senhor Javé! Vós destruiríeis todos os resíduos de Israel em vosso derramamento de vossa ira sobre Jerusalém”?
9 Ya amsa mini ya ce, “Zunubin gidan Isra’ila da Yahuda ya yi girma ainun; ƙasar ta cika da rashin adalci. Suna cewa, ‘Ubangiji ya yashe ƙasar; Ubangiji ba ya gani.’
Então ele me disse: “A iniqüidade da casa de Israel e Judá é extremamente grande, e a terra está cheia de sangue, e a cidade cheia de perversão; pois dizem: 'Javé abandonou a terra, e Javé não vê'.
10 Saboda haka ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba, amma zan kawo wa kansu abin da suka yi.”
Quanto a mim também, meu olho não poupará, nem eu terei piedade, mas lhes trarei a cabeça”.
11 Sai mutumin da yana saye da lilin yake kuma rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa ya mayar da magana, yana cewa, “Na yi yadda ka umarci ni.”
Eis que o homem vestido de linho, que tinha o tinteiro ao seu lado, relatou o assunto, dizendo: “Eu fiz como me mandou”.

< Ezekiyel 9 >