< Ezekiyel 9 >

1 Sai na ji ya yi kira da babbar murya yana cewa, “Kawo matsaran birni a nan, kowanne da makami a hannunsa.”
Puis il cria d'une voix forte moi l'entendant, et il dit: faites approcher ceux qui ont commission contre la ville, chacun avec son instrument de destruction dans sa main.
2 Na kuma ga mutane shida suna zuwa daga kowane gefen ƙofar ta bisa, wadda take fuskantar arewa, kowanne da makamin kisa a hannunsa. Tare da su akwai mutum saye da lilin yana rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa. Suka shiga suka tsaya kusa da bagaden tagulla.
Et voici six hommes venaient de devers le chemin de la haute porte qui regarde vers l'Aquilon, et chacun avait en sa main son instrument de destruction; et il y avait au milieu d'eux un homme vêtu de lin, qui avait un cornet d'écrivain sur ses reins; et ils entrèrent, et se tinrent auprès de l'autel d'airain.
3 To, fa, ɗaukakar Allah na Isra’ila ta haura daga bisa kerubobi, inda ta kasance, ta tashi zuwa bakin madogarar ƙofar haikali. Sai Ubangiji ya kira mutumin da yake saye da lilin wanda ya rataye jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa
Alors la gloire du Dieu d'Israël s'éleva de dessus le Chérubin sur lequel elle était, [et vint] sur le seuil de la maison, et il cria à l'homme qui était vêtu de lin, [et] qui avait le cornet d'écrivain sur ses reins.
4 ya ce masa, “Ka ratsa birnin Urushalima ka sa shaida a goshin waɗanda suke baƙin ciki da kuma makoki a kan dukan abubuwan banƙyamar da ake yi a cikinsa.”
Et l'Eternel lui dit: passe par le milieu de la ville, par le milieu de Jérusalem, et marque [la lettre] Thau sur les fronts des hommes qui gémissent et qui soupirent à cause de toutes les abominations qui se commettent au dedans d'elle.
5 Yayinda nake saurara, sai ya ce wa waɗansu, “Ku bi shi ta birnin ku kuma kashe, babu tausayi ko kuwa jinƙai.
Et il dit aux autres, moi l'entendant: passez par la ville après lui, et frappez; que votre œil n'épargne [personne], et n'ayez point de compassion.
6 Ku kashe tsofaffi da samari da’yan mata, mata da yara, amma kada ku taɓa wani wanda yake da shaida. Ku fara a wuri mai tsarkina.” Saboda haka suka fara da dattawan da suke gaban haikali.
Tuez tout, les vieillards, les jeunes gens, les vierges, les petits enfants, et les femmes; mais n'approchez point d'aucun de ceux sur lesquels sera [la lettre] Thau, et commencez par mon Sanctuaire. Ils commencèrent donc par les vieillards qui [étaient] devant la maison.
7 Sa’an nan ya ce musu, “Ku ƙazantar da haikalin ku kuma cika filayen da kisassu. Ku tafi!” Saboda haka suka fita suka kuma fara kisa a duk birnin.
Et il leur dit: profanez la maison, et remplissez les parvis de gens tués; sortez, et ils sortirent, et frappèrent par la ville.
8 Yayinda suke kisan sai aka bar ni kaɗai, na fāɗi rubda ciki, na yi kuka na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka dukan raguwar Isra’ila a wannan zafin fushinka a Urushalima?”
Or il arriva que comme ils frappaient, je demeurai là, et m'étant prosterné le visage contre terre, je criai, et dis: Ah! ah! Seigneur Eternel! t'en vas-tu donc détruire tous les restes d'Israël, en répandant ta fureur sur Jérusalem?
9 Ya amsa mini ya ce, “Zunubin gidan Isra’ila da Yahuda ya yi girma ainun; ƙasar ta cika da rashin adalci. Suna cewa, ‘Ubangiji ya yashe ƙasar; Ubangiji ba ya gani.’
Et il me dit: l'iniquité de la maison d'Israël et de Juda est excessivement grande, et le pays est rempli de meurtres, et la ville remplie de crimes; car ils ont dit: l'Eternel a abandonné le pays, et l'Eternel ne [nous] voit point.
10 Saboda haka ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba, amma zan kawo wa kansu abin da suka yi.”
Et quant à moi, mon œil aussi ne [les] épargnera point, et je n'en aurai point de compassion; je leur rendrai leur train sur leur tête.
11 Sai mutumin da yana saye da lilin yake kuma rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa ya mayar da magana, yana cewa, “Na yi yadda ka umarci ni.”
Et voici, l'homme vêtu de lin, qui avait le cornet sur ses reins, rapporta ce qui avait été fait, et il dit: J'ai fait comme tu m'as commandé.

< Ezekiyel 9 >