< Ezekiyel 9 >

1 Sai na ji ya yi kira da babbar murya yana cewa, “Kawo matsaran birni a nan, kowanne da makami a hannunsa.”
And he called out in ears my a voice great saying they have drawn near [the] punishments of the city and everyone [the] weapon of destruction his [is] in hand his.
2 Na kuma ga mutane shida suna zuwa daga kowane gefen ƙofar ta bisa, wadda take fuskantar arewa, kowanne da makamin kisa a hannunsa. Tare da su akwai mutum saye da lilin yana rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa. Suka shiga suka tsaya kusa da bagaden tagulla.
And there! six men [were] coming - from [the] direction of [the] gate upper which - [is] faced north-ward and everyone [the] weapon of shattering his [was] in hand his and a man one [was] in midst of them clothed linen and [the] writing-case of scribe [was] at hips his and they came and they stood beside [the] altar of bronze.
3 To, fa, ɗaukakar Allah na Isra’ila ta haura daga bisa kerubobi, inda ta kasance, ta tashi zuwa bakin madogarar ƙofar haikali. Sai Ubangiji ya kira mutumin da yake saye da lilin wanda ya rataye jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa
And [the] glory of - [the] God of Israel it was taken up from on the cherub which it had been on it to [the] threshold of the house and he called to the man who was clothed the linen whom writing-case of scribe [was] at hips his.
4 ya ce masa, “Ka ratsa birnin Urushalima ka sa shaida a goshin waɗanda suke baƙin ciki da kuma makoki a kan dukan abubuwan banƙyamar da ake yi a cikinsa.”
And he said Yahweh (to him *Q(k)*) pass in [the] midst of the city in [the] midst of Jerusalem and you will mark a mark on [the] foreheads of the people who sigh and who groan on all the abominations which are done in [the] midst of it.
5 Yayinda nake saurara, sai ya ce wa waɗansu, “Ku bi shi ta birnin ku kuma kashe, babu tausayi ko kuwa jinƙai.
And to these he said in ears my pass in the city after him and strike (not *Q(K)*) let it look with compassion (eye your *Q(K)*) and may not you show pity.
6 Ku kashe tsofaffi da samari da’yan mata, mata da yara, amma kada ku taɓa wani wanda yake da shaida. Ku fara a wuri mai tsarkina.” Saboda haka suka fara da dattawan da suke gaban haikali.
Old [man] young man and virgin and little one[s] and women you will kill to destruction and to any person whom [is] on him the mark may not you draw near and from sanctuary my you will begin and they began with the men old who [were] before the house.
7 Sa’an nan ya ce musu, “Ku ƙazantar da haikalin ku kuma cika filayen da kisassu. Ku tafi!” Saboda haka suka fita suka kuma fara kisa a duk birnin.
And he said to them make unclean the house and fill the courts [those] slain go forth and they went forth and they struck in the city.
8 Yayinda suke kisan sai aka bar ni kaɗai, na fāɗi rubda ciki, na yi kuka na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka dukan raguwar Isra’ila a wannan zafin fushinka a Urushalima?”
And it was when were striking they and [was] remaining I and I fell! on face my and I cried out and I said alas! O Lord Yahweh ¿ about to destroy [are] you all [the] remnant of Israel when pouring out you rage your on Jerusalem.
9 Ya amsa mini ya ce, “Zunubin gidan Isra’ila da Yahuda ya yi girma ainun; ƙasar ta cika da rashin adalci. Suna cewa, ‘Ubangiji ya yashe ƙasar; Ubangiji ba ya gani.’
And he said to me [the] iniquity of [the] house of Israel and Judah [is] great with muchness muchness and it has been filled the land blood and the city it is full perverseness for they have said he has forsaken Yahweh the land and not Yahweh [is] seeing.
10 Saboda haka ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba, amma zan kawo wa kansu abin da suka yi.”
And also I not it will look with compassion eye my and not I will show pity conduct their on own head their I will requite.
11 Sai mutumin da yana saye da lilin yake kuma rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa ya mayar da magana, yana cewa, “Na yi yadda ka umarci ni.”
And there! the man - clothed of the linen whom the writing-case [was] at hips his [was] bringing back a word saying I have done (according to all that *Q(K)*) you commanded me.

< Ezekiyel 9 >