< Ezekiyel 8 >

1 A shekara ta shida, a wata shida a ranar ta biya, yayinda nake zaune a gidana dattawan Yahuda kuma suna zaune a gabana, hannun Ubangiji Mai Iko Duka ya zo a kaina a can.
On the fifth day of the sixth month [of that year], almost six years after we Israeli people had been (exiled/forced to go to Babylon), I was sitting in my house. The elders of Judah were sitting in front of me. Suddenly the power [MTY] of Yahweh the Lord came on me.
2 Na duba, sai na ga siffa kamar na mutum. Daga kwankwaso zuwa ƙasa ya yi kamar wuta, kuma daga kwankwaso zuwa sama kamanninsa ya yi haske yana ƙyalli kamar ƙarfe mai haske.
[in a vision] I saw someone who resembled a man. Below his waist, [his body] was like fire, and above his waist [his body] was glowing like very hot metal.
3 Ya miƙa abin da ya yi kamar hannu ya kama a gashin kaina. Ruhu ya ɗaga ni tsakanin sama da ƙasa, a cikin wahayoyi kuma Allah ya ɗauke ni zuwa Urushalima, zuwa ƙofa zuwa gabas na cikin fili, inda gunki mai tsokanar kishi yake tsaye.
He reached out what seemed to be a hand and grabbed me by the hair of my head. The Spirit lifted me up high above the earth, and in visions God took me [from Babylon] to Jerusalem. He took me [to the temple], to the north gate, to the place where there was an idol that caused Yahweh to be very disgusted and furious.
4 A can gabana kuwa ga ɗaukakar Allah na Isra’ila, kamar a wahayin da na gani a fili.
And there in front of me was the brilliant light that indicated the presence of the God whom the Israeli [people previously worshiped. It was] like the vision that I had seen alongside the Kebar River/Canal.
5 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, duba waje arewa.” Sai na duba, a mashigin arewa na ƙofar bagaden kuwa na ga wannan gunki na tsokanar kishi.
Yahweh said to me, “You human, look toward the north!” So I looked, and I saw in the entrance of the gate near the altar that idol that caused Yahweh to be disgusted and furious.
6 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da suke yi, abubuwan banƙyamar da gidan Isra’ila ke yi a nan, abubuwan da za su kore ni daga wuri mai tsarkina? Amma za ka ga abubuwan da suka ma fi banƙyama.”
He said to me, “You human, do you see what those Israeli people [MTY] are doing? They are doing detestable things here, things that will cause me to abandon my temple. But you will see things that are even more detestable.”
7 Sa’an nan ya kawo ni mashigin filin. Na duba, na kuma ga rami a bango.
Then he brought me to the entrance of the courtyard. I looked and saw a hole in the wall.
8 Ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka haƙa cikin bangon.” Da na haƙa cikin bangon sai na ga ƙofar shiga a can.
He said to me, “You human, dig through the wall here.” So I dug through the wall, and I saw a doorway inside.
9 Sai ya ce mini, “Shiga ka ga mugaye da kuma abubuwa banƙyamar da suke yi a can.”
He said to me, “Go in and see the wicked and detestable things that they are doing there!”
10 Na kuwa shiga na duba, sai na ga zāne-zāne ko’ina a bangon na kowane irin abubuwa masu rarrafe da kuma dabbobi masu ƙazanta da dukan gumakan gidan Isra’ila.
So I went in through the doorway and looked, and I saw, all over the [of a big room, drawings of] all kinds of creatures that scurry across the ground and [other] detestable animals, and drawings of all the idols that the people of [were worshiping].
11 A gabansu ga dattawa saba’in na gidan Isra’ila tsaye a cikinsu, Ya’azaniya ɗan Shafan kuwa yana tsaye a cikinsu. Kowa yana da farantin ƙona turare a hannunsa, tulin hayaƙin turare mai ƙanshi ya tunnuƙe zuwa sama.
In front of them stood 70 elders of Israel. Jaazaniah, the son of Shaphan, was standing among them. Each of them was holding a pan in which incense was burning, and fragrant smoke of the burning incense was rising up.
12 Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da dattawan gidan Isra’ila suke yi a cikin duhu, kowa yana a ɗakin tsafin gunkinsa? Suna cewa, ‘Ubangiji ba ya ganinmu; Ubangiji ya yashe ƙasar.’”
Yahweh said to me, “You human, look at [RHQ] what the Israeli elders are doing here in the darkness, each of them standing in front of the shrine of his own idol! They are saying, ‘Yahweh does not see us; Yahweh has deserted this country.’”
13 Ya kuma ce, “Za ka gan su suna yin abubuwan da suka fi waɗannan banƙyama.”
He also said, “But you will see things that are even more detestable!”
14 Sa’an nan ya kawo ni mashigin arewa na ƙofar gidan Ubangiji, sai na ga mata zaune a can, suna makokin Tammuz.
Then he took me to the entrance at the north gate of the temple. I saw women sitting there, mourning for [the death of the god of the people of Babylonia], Tammuz.
15 Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan? Za ka ga abubuwan da suke masu banƙyama fiye da wannan.”
He said to me, “You human, you see this [RHQ], but you will see things that are more detestable than this!”
16 Sa’an nan ya kawo ni cikin fili na cikin gidan Ubangiji, a can kuwa a ƙofar haikali, tsakanin shirayi da bagade, akwai kamar mutum ashirin da biyar. Suka ba haikalin Ubangiji baya suna fuskanta wajen gabas, suna rusuna wa rana a gabas.
Then he took me into the courtyard outside the temple. There at the entrance of the temple, between the porch and the altar, were about 25 men. Their backs were toward the temple and their faces were toward the east, and they were bowing down to [worship] the sun [as it rose] in the east.
17 Ya ce mini, “Ka ga wannan, ɗan mutum? Ƙaramin abu ne gidan Yahuda su yi abubuwan banƙyamar da suke yi a nan? Dole ne su cika ƙasar da rikici su kuma ci gaba da tsokane ni in yi fushi? Dube su suna tsokanata!
He said to me, “You human, you see [RHQ] what they are doing. [Do you think that] it is not important that these men of Judah are doing these detestable things here? [But they are doing other terrible things]. They are acting violently throughout their country, and continually causing me to be angry. Look at them! They are insulting me by their actions [IDM]!
18 Saboda haka zan hukunta su cikin fushi; Ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba. Ko da yake suna ihu a kunnuwana, ba zan saurare su ba.”
So I will show them that I am very angry. I will not pity them or act mercifully toward them. And even if they shout to me [to help them], I will not pay attention to them.”

< Ezekiyel 8 >