< Ezekiyel 8 >

1 A shekara ta shida, a wata shida a ranar ta biya, yayinda nake zaune a gidana dattawan Yahuda kuma suna zaune a gabana, hannun Ubangiji Mai Iko Duka ya zo a kaina a can.
Now it came to pass in the sixth year, in the sixth month, on the fifth day of the month, as I sat in my house, and the elders of Judah sat before me, that the hand of the Lord Jehovah fell there upon me.
2 Na duba, sai na ga siffa kamar na mutum. Daga kwankwaso zuwa ƙasa ya yi kamar wuta, kuma daga kwankwaso zuwa sama kamanninsa ya yi haske yana ƙyalli kamar ƙarfe mai haske.
And I looked, and lo, a form having the appearance of fire; from the appearance of his loins downward, of fire; and from his loins upward, of a bright light, like the splendor of shining brass.
3 Ya miƙa abin da ya yi kamar hannu ya kama a gashin kaina. Ruhu ya ɗaga ni tsakanin sama da ƙasa, a cikin wahayoyi kuma Allah ya ɗauke ni zuwa Urushalima, zuwa ƙofa zuwa gabas na cikin fili, inda gunki mai tsokanar kishi yake tsaye.
And he put forth the form of a hand, and took me by a lock of my head. And the spirit lifted me up between the earth and the heaven, and brought me, in the visions of God, to Jerusalem, to the door of the inner gate, that looketh toward the north, where stood the idol of jealousy, which provoketh to jealousy.
4 A can gabana kuwa ga ɗaukakar Allah na Isra’ila, kamar a wahayin da na gani a fili.
And behold, the glory of the God of Israel was there, according to the vision which I saw in the plain.
5 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, duba waje arewa.” Sai na duba, a mashigin arewa na ƙofar bagaden kuwa na ga wannan gunki na tsokanar kishi.
Then said he to me, Son of man, lift up thine eyes toward the north! And I lifted up my eyes toward the north, and behold, northward from the gate of the altar was this idol of jealousy, at the entrance.
6 Ya kuma ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da suke yi, abubuwan banƙyamar da gidan Isra’ila ke yi a nan, abubuwan da za su kore ni daga wuri mai tsarkina? Amma za ka ga abubuwan da suka ma fi banƙyama.”
And he said to me: Son of man, seest thou what they do? Great are the abominations which the house of Israel commit here, that I should go far off from my sanctuary. But thou shalt yet again see great abominations.
7 Sa’an nan ya kawo ni mashigin filin. Na duba, na kuma ga rami a bango.
And he brought me to the door of the court, and I looked, and behold, a hole in the wall.
8 Ya ce mini, “Ɗan mutum, yanzu ka haƙa cikin bangon.” Da na haƙa cikin bangon sai na ga ƙofar shiga a can.
And he said to me, Son of man, break now through the wall. And when I had broken through the wall, behold, a door.
9 Sai ya ce mini, “Shiga ka ga mugaye da kuma abubuwa banƙyamar da suke yi a can.”
And he said to me, Go in, and behold the wicked abominations which they practise here.
10 Na kuwa shiga na duba, sai na ga zāne-zāne ko’ina a bangon na kowane irin abubuwa masu rarrafe da kuma dabbobi masu ƙazanta da dukan gumakan gidan Isra’ila.
So I went in and saw, and behold, every form of creeping things, and of abominable beasts, and all the idols of the house of Israel, portrayed upon the wall round about.
11 A gabansu ga dattawa saba’in na gidan Isra’ila tsaye a cikinsu, Ya’azaniya ɗan Shafan kuwa yana tsaye a cikinsu. Kowa yana da farantin ƙona turare a hannunsa, tulin hayaƙin turare mai ƙanshi ya tunnuƙe zuwa sama.
And there stood before them seventy men of the elders of the house of Israel, Jaazaniah, the son of Shaphan, standing in the midst of them, with every man his censer in his hand; and a thick cloud of incense went up.
12 Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga abin da dattawan gidan Isra’ila suke yi a cikin duhu, kowa yana a ɗakin tsafin gunkinsa? Suna cewa, ‘Ubangiji ba ya ganinmu; Ubangiji ya yashe ƙasar.’”
Then said he to me: Son of man, seest thou what the elders of the house of Israel do in the dark, each one in his image-chamber? For they say, “Jehovah seeth us not; Jehovah hath forsaken the land.”
13 Ya kuma ce, “Za ka gan su suna yin abubuwan da suka fi waɗannan banƙyama.”
And he said to me, Thou shalt yet again see the great abominations which they practise.
14 Sa’an nan ya kawo ni mashigin arewa na ƙofar gidan Ubangiji, sai na ga mata zaune a can, suna makokin Tammuz.
Then he brought me to the entrance of the gate of the house of Jehovah, which was toward the north, and behold, there sat women, weeping for Thammuz.
15 Ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan? Za ka ga abubuwan da suke masu banƙyama fiye da wannan.”
And he said to me, Seest thou this, O son of man? Thou shalt yet again see greater abominations than these.
16 Sa’an nan ya kawo ni cikin fili na cikin gidan Ubangiji, a can kuwa a ƙofar haikali, tsakanin shirayi da bagade, akwai kamar mutum ashirin da biyar. Suka ba haikalin Ubangiji baya suna fuskanta wajen gabas, suna rusuna wa rana a gabas.
And he brought me into the inner court of the house of Jehovah, and behold, at the entrance of the temple of Jehovah, between the porch and the altar, were about five and twenty men, with their backs toward the temple of Jehovah, and their faces toward the east; and they bowed themselves eastward toward the sun.
17 Ya ce mini, “Ka ga wannan, ɗan mutum? Ƙaramin abu ne gidan Yahuda su yi abubuwan banƙyamar da suke yi a nan? Dole ne su cika ƙasar da rikici su kuma ci gaba da tsokane ni in yi fushi? Dube su suna tsokanata!
And he said to me: Seest thou, O son of man? Is it a light thing to the house of Judah, that they commit the abominations which they commit here, that they fill the land with violence, and continually provoke me to anger? And behold, they put the blanch to their nostrils.
18 Saboda haka zan hukunta su cikin fushi; Ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba. Ko da yake suna ihu a kunnuwana, ba zan saurare su ba.”
Therefore will I also deal with them in fury; mine eye shall not spare, neither will I have pity; and though they cry in mine ears with a loud voice, yet will I not hear them.

< Ezekiyel 8 >