< Ezekiyel 7 >

1 Maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
Och Herrans ord skedde till mig, och sade:
2 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa wa ƙasar Isra’ila, “‘Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo a kan kusurwoyi huɗu na ƙasar.
Du menniskobarn, detta säger Herren Herren om Israels land: Änden kommer, änden kommer öfver alla fyra landsens ändar.
3 Ƙarshe yanzu yana a kanki. Zan fashe fushina a kanki. Zan shari’anta ki bisa ga halinki in sāka miki kuma saboda dukan ayyukan banƙyamar da kika yi.
Nu kommer änden öfver dig; ty jag skall sända mina grymhet öfver dig, och skall döma dig såsom du förtjent hafver, och skall gifva dig hvad all din styggelse tillhörer.
4 Ba zan dube ki da tausayi; ko in ƙyale ki ba. Tabbatacce zan sāka miki saboda halinki da kuma ayyukanki masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji.’
Mitt öga skall intet skona dig, eller se öfver med dig; utan jag skall gifva dig såsom du förtjent hafver, och din styggelse skola komma ibland dig, att I förnimma skolen, att jag är Herren.
5 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Masifa! Masifar da ba a taɓa gani ba tana zuwa.
Detta säger Herren Herren: Si, en olycka kommer efter den andra.
6 Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo! Ya farka a kanki. Ga shi, ya zo!
Änden kommer, änden kommer, han stöter uppå dig; si, han kommer.
7 Ƙaddara ta auko miki, ya ke wadda ke zama cikin ƙasar. Lokaci ya yi, rana ta gabato; akwai fargaba, ba farin ciki ba, a kan duwatsu.
Han går allaredo upp, och kommer fram öfver dig, du landsens inbyggare; tiden kommer, jämmerdagen är hardt när, då intet sjungande på bergomen är.
8 Ina gab da fasa hasalata a kanki in kuma aukar da fushina a kanki; zan shari’anta ke bisa ga halinki in kuma sāka miki saboda dukan ayyukanki masu banƙyama.
Nu då jag snarliga gjuta mina grymhet öfver dig, och fullkomna mina vrede uppå dig, och döma dig såsom du förtjent hafver, och gifva dig hvad all din styggelse tillhörer.
9 Ba zan dube ki da tausayi ko in ƙyale ke ba; zan sāka miki bisa ga halinki da kuma ayyukan masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji wanda yake bugunki.
Mitt öga skall intet skona dig, eller se öfver med dig; utan jag skall gifva dig såsom du förtjent hafver, och din styggelse skola komma ibland dig, att I förnimma skolen, att jag är Herren som eder slår.
10 “‘Ga shi ranar ta zo! Ta iso! Ƙaddararki ta keto, sandar ta yi toho, girman kai ya yi fure!
Si dagen, si, han kommer, han kommer fram; riset blomstras, och den stolte grönskas.
11 Rikici ya yi girma ya zama sandar da za a hukunta mugunta; babu wani daga cikin mutanen da za a bari, babu wani dukiyarsu da za a bari, babu wani abin amfani.
Tyrannen hafver upprest sig till ett ris öfver de ogudaktiga; så att intet af dem, eller af deras folk, eller af deras hop skall någon tröst få.
12 Lokaci ya yi! Ranar ta gabato! Kada mai saya ya yi farin ciki ko kuwa mai sayarwa ya yi baƙin ciki, gama hasala tana a kan dukan jama’a.
Derföre kommer tiden, dagen nalkas; köparen fröjde sig intet, och säljaren sörje intet; ty vreden kommer öfver alla deras rikedomar.
13 Mai sayarwa ba zai mayar da ƙasar da ya sayar tuntuni ba muddin dukansu suna da rai, gama ba za a sauya wahayin da ya shafi dukan jama’a ba. Saboda zunubansu, babu ɗayansu da zai adana ransa.
Derföre skall säljaren intet mer sköta om sitt sålda gods, ty den som lefver, han skall hafva det; förty Prophetien om all deras rikedom skall intet tillbakagå; derföre förhärde sig ingen i sina missgerning, genom sina rikedomar.
14 “‘Ko da yake suna busa ƙaho suna kuma shirya kome, ba wanda zai tafi yaƙi, gama hasalata tana a kan dukan jama’a.
Låter man blåsa i basunen, och tillreda all ting, der varder dock ingen till slags utdragandes; ty min grymhet går öfver allt hans folk.
15 A waje takobi ne, a ciki annoba ne da yunwa; waɗanda suke fili za su mutu ta wurin takobi, waɗanda kuma suke cikin birni yunwa da annoba za su cinye su.
Ute på gatomen går svärdet, i husomen går pestilentie och hunger; den på markene är, han måste dö genom svärd; men den i stadenom är, honom skall hunger och pestilentie uppfräta.
16 Duk waɗanda suka tsira suka tsere za su kasance a cikin duwatsu, suna kuka kamar kurciyoyin kwaruruka, kowanne saboda zunubansa.
Och de som undfly af dem, de måste vara på bergomen, och lika som dufvor i dalomen, hvilke alle tillsammans qvida, hvar och en för sina missgernings skull.
17 Kowane hannu zai raunana, kowace gwiwa kuma za tă zama marar ƙarfi kamar ruwa.
Alla händer skola nederfalla, och all knä skola vara ostadig som vatten.
18 Za su sa tufafin makoki su kuma rufu da fargaba. Fuskokinsu kuma za su rufu da kunya a kuma aske kawunansu.
Och de skola kläda sig i säcker, och med fruktan öfvergjutne varda, och all ansigte jämmerliga utse, och all hufvud skola kullot varda.
19 “‘Za su zubar da azurfarsu a tituna, zinariyarsu kuma za tă zama ƙazantacciyar aba. Azurfarsu da zinariyarsu ba za su iya cetonsu a ranar hasalar Ubangiji ba. Ba za su ƙosar da yunwansu ko su cika cikinsu da shi ba, gama su ne sanadin tuntuɓensu cikin zunubi.
De skola kasta sitt silfver ut uppå gatorna, och sitt guld akta såsom träck; ty deras silfver och guld skall intet kunna hjelpa dem, på Herrans vredes dag; och skola dock intet kunna mätta sina själ deraf, eller fylla sin buk deraf; ty det hafver varit dem en förargelse, till deras missgerningar.
20 Sun yi fariya kyan kayan adonsu suka kuma yi amfani da su don su yi gumakansu masu banƙyama, da ƙazantattun abubuwa.
Af sin ädla klenodier der de högfärd med bedrefvo, hafva de sin grufvelses och styggelses beläte gjort, derföre skall jag göra dem det till orenlighet;
21 Zan ba da su duka kamar ganima ga baƙi da kuma kamar abin da aka washe ga mugayen duniya, za su kuma ƙazantar da su.
Och skall gifva det främmandom i händer, att de det bortröfva skola, och dem ogudaktigom på jordene till ett byte, att de skola ohelga det.
22 Zan juye fuskata daga gare su, za su kuwa ƙazantar da wurina mai daraja;’yan fashi za su shiga su kuma ƙazantar da shi.
Jag skall vända mitt ansigte derifrå, att de ju min skatt väl ohelga skola; ja röfvare skola komma deröfver, och ohelga det.
23 “‘Ka shirya sarƙoƙi, domin ƙasar ta cika da alhakin jini, birnin kuma ya cika da rikici.
Gör en gård omkring dem; ty landet är fullt med blodskulder, och staden full med öfvervåld.
24 Zan kawo al’ummai mafi mugunta su mallaki gidajenku; zan kawo ƙarshen fariyar masu ƙarfi, Wurare Masu Tsarkinsu za su ƙazantu.
Så skall jag låta komma de argesta ibland Hedningarna, att de skola taga deras hus in; och skall göra en ända på de väldigas högfärd, och ohelga deras kyrkor.
25 Sa’ad da wahala ta zo, za su nemi salama, amma ba za su same ta ba.
Uppryckaren kommer; så skola de frid söka, och han skall intet vara der.
26 Masifa a kan masifa za su zo, jita-jita kuma a kan jita-jita. Za su yi ƙoƙarin samun wahayi daga annabi; koyarwar doka ta wurin firist za tă ɓace, kamar yadda shawarar dattawa za tă ɓace.
En olycka skall komma efter den andra, ett rykte öfver det andra; så skola de då söka ena syn när Prophetanom; men der skall hvarken lagen mer vara när Prestenom, eller råd när de gamla.
27 Sarki zai yi makoki, yerima zai fid da zuciya, hannuwan mutanen ƙasar kuma za su yi rawa. Zan sāka musu bisa ga ayyukansu, zan kuma hukunta su bisa ga ma’auninsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
Konungen skall vara bedröfvad, och Förstarna skola sorgeliga klädde vara, och folkens händer i landena skola förtviflada vara: Jag skall så ställa mig med dem, såsom de lefvat hafva, och skall döma dem, såsom de förtjent hafva, att de skola förnimma, att jag är Herren.

< Ezekiyel 7 >