< Ezekiyel 7 >

1 Maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
Puis la parole de l'Eternel me fut [adressée], en disant:
2 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa wa ƙasar Isra’ila, “‘Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo a kan kusurwoyi huɗu na ƙasar.
Et toi, fils d'homme, [écoute]: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel à la terre d'Israël: la fin, la fin [vient] sur les quatre coins de la terre.
3 Ƙarshe yanzu yana a kanki. Zan fashe fushina a kanki. Zan shari’anta ki bisa ga halinki in sāka miki kuma saboda dukan ayyukan banƙyamar da kika yi.
Maintenant la fin vient sur toi, et j'enverrai sur toi ma colère, et je te jugerai selon ta voie, et je mettrai sur toi toutes tes abominations.
4 Ba zan dube ki da tausayi; ko in ƙyale ki ba. Tabbatacce zan sāka miki saboda halinki da kuma ayyukanki masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji.’
Et mon œil ne t'épargnera point, et je n'aurai point de compassion; mais je mettrai ta voie sur toi, et tes abominations seront au milieu de toi; et vous saurez que je suis l'Eternel.
5 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Masifa! Masifar da ba a taɓa gani ba tana zuwa.
Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: voici un mal, un seul mal qui vient.
6 Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo! Ya farka a kanki. Ga shi, ya zo!
La fin vient, la fin vient, elle se réveille contre toi; voici, [le mal] vient.
7 Ƙaddara ta auko miki, ya ke wadda ke zama cikin ƙasar. Lokaci ya yi, rana ta gabato; akwai fargaba, ba farin ciki ba, a kan duwatsu.
Le matin vient sur toi qui demeures au pays; le temps vient, le jour est près de toi; il ne sera que frayeur, et non point une invitation des montagnes à s'entre-réjouir.
8 Ina gab da fasa hasalata a kanki in kuma aukar da fushina a kanki; zan shari’anta ke bisa ga halinki in kuma sāka miki saboda dukan ayyukanki masu banƙyama.
Maintenant je répandrai bientôt ma fureur sur toi, et je consommerai ma colère sur toi, et je te jugerai selon ta voie, je mettrai sur toi toutes tes abominations.
9 Ba zan dube ki da tausayi ko in ƙyale ke ba; zan sāka miki bisa ga halinki da kuma ayyukan masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji wanda yake bugunki.
Mon œil ne t'épargnera point, et je n'aurai point de compassion, je te punirai selon ta voie, et tes abominations seront au milieu de toi; et vous saurez que je suis l'Eternel qui frappe.
10 “‘Ga shi ranar ta zo! Ta iso! Ƙaddararki ta keto, sandar ta yi toho, girman kai ya yi fure!
Voici le jour, voici il vient, le matin paraît, la verge a fleuri, la fierté a jeté des boutons.
11 Rikici ya yi girma ya zama sandar da za a hukunta mugunta; babu wani daga cikin mutanen da za a bari, babu wani dukiyarsu da za a bari, babu wani abin amfani.
La violence est crûe en verge de méchanceté; il ne restera rien d'eux, ni de leur multitude, ni de leur tumulte, et on ne les lamentera point.
12 Lokaci ya yi! Ranar ta gabato! Kada mai saya ya yi farin ciki ko kuwa mai sayarwa ya yi baƙin ciki, gama hasala tana a kan dukan jama’a.
Le temps vient, le jour est tout proche: que celui donc qui achète ne se réjouisse point, et que celui qui vend n'en mène point de deuil; car il y a une ardeur de colère sur toute la multitude de son [pays].
13 Mai sayarwa ba zai mayar da ƙasar da ya sayar tuntuni ba muddin dukansu suna da rai, gama ba za a sauya wahayin da ya shafi dukan jama’a ba. Saboda zunubansu, babu ɗayansu da zai adana ransa.
Car celui qui vend ne retournera point à ce qu'il aura vendu, quand ils seraient encore en vie; parce que la vision touchant toute la multitude de son [pays] ne sera point révoquée, et chacun [portera] la peine de son iniquité, tant qu'il vivra; ils ne reprendront jamais courage.
14 “‘Ko da yake suna busa ƙaho suna kuma shirya kome, ba wanda zai tafi yaƙi, gama hasalata tana a kan dukan jama’a.
Ils ont sonné la trompette, et ils ont tout préparé, mais il n'y a personne qui aille au combat, parce que l'ardeur de ma colère est sur toute la multitude de son [pays].
15 A waje takobi ne, a ciki annoba ne da yunwa; waɗanda suke fili za su mutu ta wurin takobi, waɗanda kuma suke cikin birni yunwa da annoba za su cinye su.
L'épée est au dehors, et la mortalité et la famine sont au dedans; celui qui sera aux champs, mourra par l'épée; et celui qui sera dans la ville, la famine et la mortalité le dévoreront.
16 Duk waɗanda suka tsira suka tsere za su kasance a cikin duwatsu, suna kuka kamar kurciyoyin kwaruruka, kowanne saboda zunubansa.
Et les réchappés d'entre eux s'enfuiront, et seront par les montagnes comme les pigeons des vallées, tous gémissants, chacun dans son iniquité.
17 Kowane hannu zai raunana, kowace gwiwa kuma za tă zama marar ƙarfi kamar ruwa.
Toutes les mains deviendront lâches, et tous les genoux se fondront en eau.
18 Za su sa tufafin makoki su kuma rufu da fargaba. Fuskokinsu kuma za su rufu da kunya a kuma aske kawunansu.
Ils se ceindront de sacs, et le tremblement les couvrira, la confusion sera sur tous leurs visages, et leurs têtes deviendront chauves.
19 “‘Za su zubar da azurfarsu a tituna, zinariyarsu kuma za tă zama ƙazantacciyar aba. Azurfarsu da zinariyarsu ba za su iya cetonsu a ranar hasalar Ubangiji ba. Ba za su ƙosar da yunwansu ko su cika cikinsu da shi ba, gama su ne sanadin tuntuɓensu cikin zunubi.
Ils jetteront leur argent par les rues, et leur or s'en ira au loin; leur argent ni leur or ne les pourront pas délivrer au jour de la grande colère de l'Eternel; ils ne rassasieront point leurs âmes, et ne rempliront point leurs entrailles, parce que leur iniquité aura été leur ruine.
20 Sun yi fariya kyan kayan adonsu suka kuma yi amfani da su don su yi gumakansu masu banƙyama, da ƙazantattun abubuwa.
II avait mis [entre eux] la noblesse de son magnifique ornement; mais ils y ont placé des images de leurs abominations, et de leurs infamies, c'est pourquoi je la leur ai exposée à être chassée au loin.
21 Zan ba da su duka kamar ganima ga baƙi da kuma kamar abin da aka washe ga mugayen duniya, za su kuma ƙazantar da su.
Et je l'ai livrée en pillage dans la main des étrangers, et en proie aux méchants de la terre, qui la profaneront.
22 Zan juye fuskata daga gare su, za su kuwa ƙazantar da wurina mai daraja;’yan fashi za su shiga su kuma ƙazantar da shi.
Je détournerai aussi ma face d'eux, et on violera mon lieu secret, et les saccageurs y entreront, et le profaneront.
23 “‘Ka shirya sarƙoƙi, domin ƙasar ta cika da alhakin jini, birnin kuma ya cika da rikici.
Fais une chaîne; car le pays est plein de crimes de meurtre, et la ville est pleine de violence.
24 Zan kawo al’ummai mafi mugunta su mallaki gidajenku; zan kawo ƙarshen fariyar masu ƙarfi, Wurare Masu Tsarkinsu za su ƙazantu.
C'est pourquoi je ferai venir les plus méchants des nations, qui possèderont leurs maisons, et je ferai cesser l'orgueil des puissants, et leurs saints lieux seront profanés.
25 Sa’ad da wahala ta zo, za su nemi salama, amma ba za su same ta ba.
La destruction vient, et ils chercheront la paix, mais il n'y en aura point.
26 Masifa a kan masifa za su zo, jita-jita kuma a kan jita-jita. Za su yi ƙoƙarin samun wahayi daga annabi; koyarwar doka ta wurin firist za tă ɓace, kamar yadda shawarar dattawa za tă ɓace.
Malheur viendra sur malheur, et il y aura rumeur sur rumeur; ils demanderont la vision aux Prophètes; la Loi périra chez le Sacrificateur, et le conseil chez les anciens.
27 Sarki zai yi makoki, yerima zai fid da zuciya, hannuwan mutanen ƙasar kuma za su yi rawa. Zan sāka musu bisa ga ayyukansu, zan kuma hukunta su bisa ga ma’auninsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
Le Roi mènera deuil, les principaux se vêtiront de désolation, et les mains du peuple du pays tomberont de frayeur; je les traiterai selon leur voie, et je les jugerai selon qu'ils l'auront mérité; et ils sauront que je suis l'Eternel.

< Ezekiyel 7 >