< Ezekiyel 7 >
1 Maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
And it came [the] word of Yahweh to me saying.
2 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa wa ƙasar Isra’ila, “‘Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo a kan kusurwoyi huɗu na ƙasar.
And you O son of humankind thus he says [the] Lord Yahweh to [the] land of Israel an end it has come the end on ([the] four *Q(K)*) [the] corners of the land.
3 Ƙarshe yanzu yana a kanki. Zan fashe fushina a kanki. Zan shari’anta ki bisa ga halinki in sāka miki kuma saboda dukan ayyukan banƙyamar da kika yi.
Now the end [is] on you and I will send forth anger my on you and I will judge you according to ways your and I will requite to you all abominations your.
4 Ba zan dube ki da tausayi; ko in ƙyale ki ba. Tabbatacce zan sāka miki saboda halinki da kuma ayyukanki masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji.’
And not it will look with compassion eye my on you and not I will show pity for ways your to you I will requite and abominations your in midst of you they will be and you will know that I [am] Yahweh.
5 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Masifa! Masifar da ba a taɓa gani ba tana zuwa.
Thus he says [the] Lord Yahweh calamity one calamity there! [it is] coming.
6 Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo! Ya farka a kanki. Ga shi, ya zo!
An end it has come it has come the end it has awakened against you there! [it is] coming.
7 Ƙaddara ta auko miki, ya ke wadda ke zama cikin ƙasar. Lokaci ya yi, rana ta gabato; akwai fargaba, ba farin ciki ba, a kan duwatsu.
It has come doom to you O inhabitant of the land it has come the time [is] near the day confusion and not a shout of joy mountains.
8 Ina gab da fasa hasalata a kanki in kuma aukar da fushina a kanki; zan shari’anta ke bisa ga halinki in kuma sāka miki saboda dukan ayyukanki masu banƙyama.
Now from near [future] I will pour out rage my on you and I will complete anger my on you and I will judge you according to ways your and I will requite to you all abominations your.
9 Ba zan dube ki da tausayi ko in ƙyale ke ba; zan sāka miki bisa ga halinki da kuma ayyukan masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji wanda yake bugunki.
And not it will look with compassion eye my and not I will show pity according to ways your to you I will requite and abominations your in midst of you they will be and you will know that I Yahweh [am] striking.
10 “‘Ga shi ranar ta zo! Ta iso! Ƙaddararki ta keto, sandar ta yi toho, girman kai ya yi fure!
There! the day there! [it is] coming it has gone forth doom it has blossomed the rod it has budded arrogance.
11 Rikici ya yi girma ya zama sandar da za a hukunta mugunta; babu wani daga cikin mutanen da za a bari, babu wani dukiyarsu da za a bari, babu wani abin amfani.
Violence - it has arisen to a rod of wickedness not any of them and not any of multitude their and not any of noise their and not distinction [is] among them.
12 Lokaci ya yi! Ranar ta gabato! Kada mai saya ya yi farin ciki ko kuwa mai sayarwa ya yi baƙin ciki, gama hasala tana a kan dukan jama’a.
It has come the time it has arrived the day the buyer may not he rejoice and the seller may not he mourn for anger [is] against all multitude its.
13 Mai sayarwa ba zai mayar da ƙasar da ya sayar tuntuni ba muddin dukansu suna da rai, gama ba za a sauya wahayin da ya shafi dukan jama’a ba. Saboda zunubansu, babu ɗayansu da zai adana ransa.
For the seller to the thing sold not he will return and still [is] in life life their for [the] vision concerning all multitude its not it will turn back and anyone in iniquity his life his not they will strengthen themselves.
14 “‘Ko da yake suna busa ƙaho suna kuma shirya kome, ba wanda zai tafi yaƙi, gama hasalata tana a kan dukan jama’a.
They have given a blast on the trumpet and to prepare everything and there not [is one who] goes to the battle for anger my [is] against all multitude its.
15 A waje takobi ne, a ciki annoba ne da yunwa; waɗanda suke fili za su mutu ta wurin takobi, waɗanda kuma suke cikin birni yunwa da annoba za su cinye su.
The sword [is] on the outside and pestilence and famine [are] from inside [the one] who [is] in the open country by the sword he will die and [the one] who [is] in the city famine and pestilence it will consume him.
16 Duk waɗanda suka tsira suka tsere za su kasance a cikin duwatsu, suna kuka kamar kurciyoyin kwaruruka, kowanne saboda zunubansa.
And they will escape escapees their and they will be to the mountains like [the] doves of the valleys all of them moaning everyone for own iniquity his.
17 Kowane hannu zai raunana, kowace gwiwa kuma za tă zama marar ƙarfi kamar ruwa.
All the pairs of hands they will drop and all knees they will go water.
18 Za su sa tufafin makoki su kuma rufu da fargaba. Fuskokinsu kuma za su rufu da kunya a kuma aske kawunansu.
And they will gird themselves sackcloth and it will cover them shuddering and [will be] to every face shame and [will be] on all heads their baldness.
19 “‘Za su zubar da azurfarsu a tituna, zinariyarsu kuma za tă zama ƙazantacciyar aba. Azurfarsu da zinariyarsu ba za su iya cetonsu a ranar hasalar Ubangiji ba. Ba za su ƙosar da yunwansu ko su cika cikinsu da shi ba, gama su ne sanadin tuntuɓensu cikin zunubi.
Silver their in the streets they will throw and gold their an impure thing it will become silver their and gold their not it will be able to deliver them in [the] day of [the] fury of Yahweh appetite their not they will satisfy and inward parts their not they will fill for [the] stumbling block of iniquity their it has become.
20 Sun yi fariya kyan kayan adonsu suka kuma yi amfani da su don su yi gumakansu masu banƙyama, da ƙazantattun abubuwa.
And [the] beauty of ornament[s] its into pride he has made it and [the] images of abominations their detestable things their they have made with it there-fore I will make it for them into an impure thing.
21 Zan ba da su duka kamar ganima ga baƙi da kuma kamar abin da aka washe ga mugayen duniya, za su kuma ƙazantar da su.
And I will give it in [the] hand of the strangers to spoil and to [the] wicked [people] of the earth to plunder (and they will profane it. *Q(K)*)
22 Zan juye fuskata daga gare su, za su kuwa ƙazantar da wurina mai daraja;’yan fashi za su shiga su kuma ƙazantar da shi.
And I will turn around face my from them and they will profane treasured [place] my and they will go in it robbers and they will profane it.
23 “‘Ka shirya sarƙoƙi, domin ƙasar ta cika da alhakin jini, birnin kuma ya cika da rikici.
Make the chain for the land it is full judgment of blood and the city it is full violence.
24 Zan kawo al’ummai mafi mugunta su mallaki gidajenku; zan kawo ƙarshen fariyar masu ƙarfi, Wurare Masu Tsarkinsu za su ƙazantu.
And I will bring [the] evil of nations and they will take possession of houses their and I will put an end to [the] pride of mighty [ones] and they will be profaned sanctuaries their.
25 Sa’ad da wahala ta zo, za su nemi salama, amma ba za su same ta ba.
Anguish it has come and they will seek peace and not.
26 Masifa a kan masifa za su zo, jita-jita kuma a kan jita-jita. Za su yi ƙoƙarin samun wahayi daga annabi; koyarwar doka ta wurin firist za tă ɓace, kamar yadda shawarar dattawa za tă ɓace.
Disaster to disaster it will come and report to report it will be and they will seek a vision from a prophet and instruction it will be lost from [the] priest and counsel from elders.
27 Sarki zai yi makoki, yerima zai fid da zuciya, hannuwan mutanen ƙasar kuma za su yi rawa. Zan sāka musu bisa ga ayyukansu, zan kuma hukunta su bisa ga ma’auninsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
The king he will mourn and [the] prince he will wear desolation and [the] hands of [the] people of the land they will be terrified from way their I will deal with them and by judgments their I will judge them and they will know that I [am] Yahweh.