< Ezekiyel 7 >
1 Maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
And the word of the Lord came unto me, saying,
2 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa wa ƙasar Isra’ila, “‘Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo a kan kusurwoyi huɗu na ƙasar.
And thou, son of man, thus hath said the Lord Eternal concerning the land of Israel, There is an end! the end is coming over the four corners of the land.
3 Ƙarshe yanzu yana a kanki. Zan fashe fushina a kanki. Zan shari’anta ki bisa ga halinki in sāka miki kuma saboda dukan ayyukan banƙyamar da kika yi.
Now cometh the end over thee, and I will let loose my anger against thee, and will judge thee according to thy ways, and I will lay upon thee all thy abominations.
4 Ba zan dube ki da tausayi; ko in ƙyale ki ba. Tabbatacce zan sāka miki saboda halinki da kuma ayyukanki masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji.’
And my eye shall not show pity upon thee, and I will not spare thee; for thy own ways will I lay upon thee, and thy abominations shall come in the midst of thee: and ye shall know that I am the Lord.
5 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Masifa! Masifar da ba a taɓa gani ba tana zuwa.
Thus hath said the Lord Eternal, An evil, a peculiar evil, behold, is coming.
6 Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo! Ya farka a kanki. Ga shi, ya zo!
An end is coming, there is coming the end: it waketh up against thee; behold, [the evil] cometh.
7 Ƙaddara ta auko miki, ya ke wadda ke zama cikin ƙasar. Lokaci ya yi, rana ta gabato; akwai fargaba, ba farin ciki ba, a kan duwatsu.
The evil decree is come against thee, O thou inhabitant of the land: the time is come, near is the day of tumult, and not the joyful call on the mountains.
8 Ina gab da fasa hasalata a kanki in kuma aukar da fushina a kanki; zan shari’anta ke bisa ga halinki in kuma sāka miki saboda dukan ayyukanki masu banƙyama.
Now will I in a short time pour out my fury over thee, and I will let out all my anger against thee, and I will judge thee according to thy ways, and I will lay upon thee all thy abominations.
9 Ba zan dube ki da tausayi ko in ƙyale ke ba; zan sāka miki bisa ga halinki da kuma ayyukan masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji wanda yake bugunki.
And my eye shall not show pity, and I will not spare: according to thy ways will I lay [evil] on thee, and thy abominations shall come in the midst of thee: and ye shall know that I am the Lord that smiteth.
10 “‘Ga shi ranar ta zo! Ta iso! Ƙaddararki ta keto, sandar ta yi toho, girman kai ya yi fure!
Behold the day, behold, it is coming; the evil decree is gone forth; the staff hath blossomed, presumption hath budded;
11 Rikici ya yi girma ya zama sandar da za a hukunta mugunta; babu wani daga cikin mutanen da za a bari, babu wani dukiyarsu da za a bari, babu wani abin amfani.
The violence is grown up into the staff of wickedness: nothing is left of them, and nothing of their multitude, and nothing of theirs; and there shall be no lamenting for them.
12 Lokaci ya yi! Ranar ta gabato! Kada mai saya ya yi farin ciki ko kuwa mai sayarwa ya yi baƙin ciki, gama hasala tana a kan dukan jama’a.
The time is coming, the day occurreth; let the buyer not rejoice, and let the seller not mourn; for wrath is against all her multitude.
13 Mai sayarwa ba zai mayar da ƙasar da ya sayar tuntuni ba muddin dukansu suna da rai, gama ba za a sauya wahayin da ya shafi dukan jama’a ba. Saboda zunubansu, babu ɗayansu da zai adana ransa.
For the seller shall not return to that which is sold, although their soul were yet alive; for the vision is against all her multitude; no one shall return; but the soul of every one is fastened to his iniquity, they do not strengthen themselves [to repent].
14 “‘Ko da yake suna busa ƙaho suna kuma shirya kome, ba wanda zai tafi yaƙi, gama hasalata tana a kan dukan jama’a.
They have blown the cornet, every one maketh himself ready; but no one goeth to the battle; for my wrath is against all her multitude.
15 A waje takobi ne, a ciki annoba ne da yunwa; waɗanda suke fili za su mutu ta wurin takobi, waɗanda kuma suke cikin birni yunwa da annoba za su cinye su.
The sword is without, and the pestilence and the famine are within: he that is in the field shall die by the sword; and he that is in the city, him shall famine and pestilence devour.
16 Duk waɗanda suka tsira suka tsere za su kasance a cikin duwatsu, suna kuka kamar kurciyoyin kwaruruka, kowanne saboda zunubansa.
But they that escape of them shall escape, and they shall be on the mountains like the doves of the valleys, all of which are moaning, every one in his iniquity.
17 Kowane hannu zai raunana, kowace gwiwa kuma za tă zama marar ƙarfi kamar ruwa.
All hands become feeble, and all knees go into water.
18 Za su sa tufafin makoki su kuma rufu da fargaba. Fuskokinsu kuma za su rufu da kunya a kuma aske kawunansu.
And people gird themselves with sackcloth, and shuddering covereth them: and upon all faces there is shame, and upon all their heads there is baldness.
19 “‘Za su zubar da azurfarsu a tituna, zinariyarsu kuma za tă zama ƙazantacciyar aba. Azurfarsu da zinariyarsu ba za su iya cetonsu a ranar hasalar Ubangiji ba. Ba za su ƙosar da yunwansu ko su cika cikinsu da shi ba, gama su ne sanadin tuntuɓensu cikin zunubi.
Their silver shall they cast into the streets, and their gold shall be as though it were unclean: their silver and their gold shall not be able to deliver them on the day of the wrath of the Lord; they shall not satisfy their souls, and not fill their bowels; because it was the stumbling-block for their iniquity.
20 Sun yi fariya kyan kayan adonsu suka kuma yi amfani da su don su yi gumakansu masu banƙyama, da ƙazantattun abubuwa.
And as for the beauty of his ornament, which he had instituted for [their] pride: even therein did they make the images of their abominations, their detestable things; therefore have I rendered it unclean for them.
21 Zan ba da su duka kamar ganima ga baƙi da kuma kamar abin da aka washe ga mugayen duniya, za su kuma ƙazantar da su.
And I will give it up into the hands of the strangers for a prey, and to the wicked of the earth for a spoil: and they shall pollute it.
22 Zan juye fuskata daga gare su, za su kuwa ƙazantar da wurina mai daraja;’yan fashi za su shiga su kuma ƙazantar da shi.
And I will turn away my face from them, and they shall pollute my place where I dwelt in secret; and therein shall barbarians enter and pollute it.
23 “‘Ka shirya sarƙoƙi, domin ƙasar ta cika da alhakin jini, birnin kuma ya cika da rikici.
Make chains; for the land is full of blood-guiltiness, and the city is full of violence.
24 Zan kawo al’ummai mafi mugunta su mallaki gidajenku; zan kawo ƙarshen fariyar masu ƙarfi, Wurare Masu Tsarkinsu za su ƙazantu.
Therefore will I bring the worst of nations, and they shall take possession of their houses: I will also cause the pride of the mighty to cease; and their holy places shall be polluted.
25 Sa’ad da wahala ta zo, za su nemi salama, amma ba za su same ta ba.
Destruction cometh: and they will seek peace, but there shall be none.
26 Masifa a kan masifa za su zo, jita-jita kuma a kan jita-jita. Za su yi ƙoƙarin samun wahayi daga annabi; koyarwar doka ta wurin firist za tă ɓace, kamar yadda shawarar dattawa za tă ɓace.
Mishap shall come upon mishap, and report shall be spread upon report: and then will they seek a vision from the prophet; but the law shall be lost from the priest, and counsel from the ancients.
27 Sarki zai yi makoki, yerima zai fid da zuciya, hannuwan mutanen ƙasar kuma za su yi rawa. Zan sāka musu bisa ga ayyukansu, zan kuma hukunta su bisa ga ma’auninsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
The king shall mourn, and the prince shall be clothed with distress, and the hands of the people of the land shall be powerless: after their way will I do unto them, and according to their own manners will I judge them; and they shall know that I am the Lord.