< Ezekiyel 6 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
La Palabra de Yavé vino a mí:
2 “Ɗan mutum, ka kafa idonka a kan duwatsun Isra’ila; ka yi annabci a kansu
Hijo de hombre, pon tu rostro hacia las montañas de Israel y profetiza contra ellas:
3 ka ce, ‘Ya ku duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa duwatsu da tuddai, ga rafuffuka da kuma kwaruruka. Ina shirin kawo takobi a kanku, kuma zan hallaka masujadanku.
Montañas de Israel, oigan la Palabra de ʼAdonay Yavé. ʼAdonay Yavé dice esto a las montañas y colinas, a los arroyos y a los valles: Ciertamente Yo mismo envío una espada sobre ustedes para destruir sus lugares altos.
4 Za a ragargaza bagadanku a kuma farfasa bagadanku na ƙone turare; zan kuma kashe mutanenku a gaban gumakanku.
Sus altares serán desolados y sus quemaderos de incienso serán destruidos. Caerán sus asesinados delante de sus ídolos.
5 Zan shimfiɗa gawawwakin Isra’ilawa a gaban gumakansu, in kuma watsar da ƙasusuwanku kewaye da bagadanku.
Echaré los cadáveres de los hijos de Israel delante de sus ídolos y esparciré sus huesos alrededor de sus altares.
6 Duk inda kuke zama, garuruwa za su zama kango, za a kuma ragargaza masujadai, saboda bagadanku su rurrushe su zama kango, a kuma farfasa gumakanku su lalace, za a rurrushe bagadan ƙone turarenku, a kuma shafe dukan abin da kuka yi.
Las ciudades serán asoladas en todos los lugares donde vivan. Los lugares altos serán asolados hasta que queden arruinados, sus quemaderos de incienso destruidos, sus ídolos quebrados y destruidos, y sus imágenes del sol destruidas. Sus obras serán deshechas.
7 Za a kashe mutanenku a cikinku, za ku kuwa sani ni ne Ubangiji.
Los asesinados caerán entre ustedes. Y sabrán que Yo soy Yavé.
8 “‘Amma zan bar waɗansu, gama waɗansunku za su tsere wa takobi sa’ad da aka watsar da ku a cikin ƙasashe da al’ummai.
Pero cuando sean esparcidos por los países dejaré un remanente que escape de la espada de otras naciones.
9 Sa’an nan a cikin al’ummai inda aka kai ku zaman bauta, waɗanda suka a tsere za su tuna da ni, yadda raina ya ɓaci ta wurin zukatansu marasa imani, waɗanda suka rabu da ni, da kuma ta wurin idanunsu, waɗanda suka yi sha’awace-sha’awacen gumakansu. Za su ji ƙyamar kansu saboda mugayen abubuwan da suka aikata.
Entonces los que de ustedes escapen se acordarán de Mí en las naciones a las cuales sean llevados cautivos. Porque Yo fui quebrantado por su corazón adúltero que se apartó de Mí, y por sus ojos que se prostituyeron tras sus ídolos. Ellos se aborrecerán a sí mismos a causa de las maldades que cometieron, por todas sus repugnancias.
10 Za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji; ba a banza na ce zan kawo musu wannan masifa ba.
Entonces sabrán que Yo soy Yavé. No dije en vano que les haría este mal.
11 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ku tafa hannuwanku tare ku kuma taka ƙafafunku ku yi ihu ku ce, “Kaito!” Saboda dukan mugaye da kuma abubuwan banƙyama na gidan Isra’ila, gama za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba.
ʼAdonay Yavé dice: Bate tus manos, pisotea y dí: ¡Ay, por causa de todas las graves repugnancias de la Casa de Israel, caerán por la espada, la hambruna y la pestilencia!
12 Wanda yake da nisa zai mutu da annoba, shi da yake kusa kuma zai mutu ta takobi, wanda kuma ya tsira aka kuma bari zai mutu da yunwa. Ta haka zan aukar da fushina a kansu.
El que esté lejos morirá de pestilencia. El que esté cerca caerá a espada. El que esté vivo y sitiado morirá de hambre. De esta manera desahogaré mi furor sobre ellos.
13 Za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da gawawwakin mutanensu suna kwance a kusa da gumakansu da kewaye da bagadansu, a kowane kan tudu mai tsawo da kuma a kan dukan kan duwatsu, a ƙarƙashin kowane inuwar itace da kuma kowane oak mai ganye, wuraren da suke ƙone turare masu ƙanshi wa dukan gumakansu.
Entonces ustedes sabrán que Yo soy Yavé, cuando sus asesinados queden tendidos en medio de sus ídolos alrededor de sus altares, sobre toda colina elevada y en todas las cumbres de las montañas, y debajo de todo árbol frondoso y todo roble espeso, lugares donde ofrecieron aroma agradable a sus ídolos.
14 Zan kuma miƙa hannuna a kansu in mai da ƙasarsu kango daga hamadan Dibila, a duk inda suke zama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
Por tanto extenderé mi mano contra ellos en todas sus moradas. En todos los lugares donde vivan, desde el desierto hasta Dibla, dejaré la tierra en desolación y asolamiento. Y sabrán que Yo soy Yavé.

< Ezekiyel 6 >