< Ezekiyel 6 >

1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
و کلام خداوند بر من نازل شده، گفت:۱
2 “Ɗan mutum, ka kafa idonka a kan duwatsun Isra’ila; ka yi annabci a kansu
«ای پسر انسان نظر خود را بر کوههای اسرائیل بدوز و درباره آنها نبوت کن.۲
3 ka ce, ‘Ya ku duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa duwatsu da tuddai, ga rafuffuka da kuma kwaruruka. Ina shirin kawo takobi a kanku, kuma zan hallaka masujadanku.
و بگو: ای کوههای اسرائیل کلام خداوند یهوه را بشنوید! خداوند یهوه به کوهها و تلها و وادیها و دره هاچنین می‌فرماید: اینک من شمشیری بر شمامی آورم و مکان های بلند شما را خراب خواهم کرد.۳
4 Za a ragargaza bagadanku a kuma farfasa bagadanku na ƙone turare; zan kuma kashe mutanenku a gaban gumakanku.
و مذبح های شما منهدم و تمثالهای شمسی شما شکسته خواهد شد و کشتگان شمارا پیش بتهای شما خواهم‌انداخت. و لاشهای بنی‌اسرائیل را پیش بتهای ایشان خواهم گذاشت و استخوانهای شما را گرداگرد مذبح های شما خواهم پاشید.۴
5 Zan shimfiɗa gawawwakin Isra’ilawa a gaban gumakansu, in kuma watsar da ƙasusuwanku kewaye da bagadanku.
۵
6 Duk inda kuke zama, garuruwa za su zama kango, za a kuma ragargaza masujadai, saboda bagadanku su rurrushe su zama kango, a kuma farfasa gumakanku su lalace, za a rurrushe bagadan ƙone turarenku, a kuma shafe dukan abin da kuka yi.
و در جمیع مساکن شما شهرهاخراب و مکان های بلند ویران خواهد شد تا آنکه مذبح های شما خراب و ویران شود و بتهای شماشکسته و نابود گردد و تمثالهای شمسی شمامنهدم و اعمال شمامحو شود.۶
7 Za a kashe mutanenku a cikinku, za ku kuwa sani ni ne Ubangiji.
و چون کشتگان شما در میان شما بیفتند، آنگاه خواهی دانست که من یهوه هستم.۷
8 “‘Amma zan bar waɗansu, gama waɗansunku za su tsere wa takobi sa’ad da aka watsar da ku a cikin ƙasashe da al’ummai.
اما بقیتی نگاه خواهم داشت. وچون در میان کشورها پراکنده شوید، بقیه السیف شما در میان امت‌ها ساکن خواهند شد.۸
9 Sa’an nan a cikin al’ummai inda aka kai ku zaman bauta, waɗanda suka a tsere za su tuna da ni, yadda raina ya ɓaci ta wurin zukatansu marasa imani, waɗanda suka rabu da ni, da kuma ta wurin idanunsu, waɗanda suka yi sha’awace-sha’awacen gumakansu. Za su ji ƙyamar kansu saboda mugayen abubuwan da suka aikata.
ونجات‌یافتگان شما در میان امت‌ها در جایی که ایشان را به اسیری برده‌اند مرا یاد خواهند داشت. چونکه دل زناکار ایشان را که از من دور شده است خواهم شکست و چشمان ایشان را که در عقب بتهای ایشان زنا کرده است - پس خویشتن را به‌سبب اعمال زشتی که در همه رجاسات خودنموده‌اند مکروه خواهند داشت.۹
10 Za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji; ba a banza na ce zan kawo musu wannan masifa ba.
و خواهنددانست که من یهوه هستم و عبث نگفتم که این بلارا بر ایشان وارد خواهم آورد.»۱۰
11 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ku tafa hannuwanku tare ku kuma taka ƙafafunku ku yi ihu ku ce, “Kaito!” Saboda dukan mugaye da kuma abubuwan banƙyama na gidan Isra’ila, gama za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba.
خداوند یهوه چنین می‌گوید: «به‌دست خود بزن و پای خود را بر زمین بکوب و بگو: وای بر تمامی رجاسات و شریر خاندان اسرائیل زیراکه به شمشیر و قحط و وباخواهد افتاد.۱۱
12 Wanda yake da nisa zai mutu da annoba, shi da yake kusa kuma zai mutu ta takobi, wanda kuma ya tsira aka kuma bari zai mutu da yunwa. Ta haka zan aukar da fushina a kansu.
آنکه دور باشد به وبا خواهد مرد و آنکه نزدیک است به شمشیر خواهد افتادو آنکه باقی‌مانده و درمحاصره باشد از گرسنگی خواهد مرد و من حدت خشم خود را بر ایشان به اتمام خواهم رسانید.۱۲
13 Za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da gawawwakin mutanensu suna kwance a kusa da gumakansu da kewaye da bagadansu, a kowane kan tudu mai tsawo da kuma a kan dukan kan duwatsu, a ƙarƙashin kowane inuwar itace da kuma kowane oak mai ganye, wuraren da suke ƙone turare masu ƙanshi wa dukan gumakansu.
و خواهید دانست که من یهوه هستم، هنگامی که کشتگان ایشان در میان بتهای ایشان به اطراف مذبح های ایشان، بر هر تل بلند و برقله های تمام کوهها و زیر هر درخت سبز و زیر هر بلوط کشن، در جایی که هدایای خوشبو برای همه بتهای خود می‌گذرانیدند یافت خواهند شد.۱۳
14 Zan kuma miƙa hannuna a kansu in mai da ƙasarsu kango daga hamadan Dibila, a duk inda suke zama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
و دست خود را بر ایشان دراز کرده، زمین را درتمام مسکن های ایشان خرابتر و ویرانتر از بیابان دبله خواهم ساخت. پس خواهند دانست که من یهوه هستم.»۱۴

< Ezekiyel 6 >