< Ezekiyel 6 >
1 Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
A message from the Lord came to me that said,
2 “Ɗan mutum, ka kafa idonka a kan duwatsun Isra’ila; ka yi annabci a kansu
“Son of man, face towards of Israel's mountains and prophesy against them.
3 ka ce, ‘Ya ku duwatsun Isra’ila, ku ji maganar Ubangiji Mai Iko Duka. Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce wa duwatsu da tuddai, ga rafuffuka da kuma kwaruruka. Ina shirin kawo takobi a kanku, kuma zan hallaka masujadanku.
Tell them: Mountains of Israel, listen to the message from the Lord God! This is what the Lord God says to the mountains and the hills, to the gorges and the valleys: I'm going to attack you and destroy your high places.
4 Za a ragargaza bagadanku a kuma farfasa bagadanku na ƙone turare; zan kuma kashe mutanenku a gaban gumakanku.
Your pagan altars will be torn down, and your incense altars will be smashed to pieces. I will kill your idol worshipers right in front of their idols.
5 Zan shimfiɗa gawawwakin Isra’ilawa a gaban gumakansu, in kuma watsar da ƙasusuwanku kewaye da bagadanku.
I will put the dead bodies of you Israelites in front of your idols and scatter your bones around your altars.
6 Duk inda kuke zama, garuruwa za su zama kango, za a kuma ragargaza masujadai, saboda bagadanku su rurrushe su zama kango, a kuma farfasa gumakanku su lalace, za a rurrushe bagadan ƙone turarenku, a kuma shafe dukan abin da kuka yi.
Everywhere you live, the towns will be turned into rubble and the high places torn down. Your altars will be demolished and defiled. Your idols will be smashed and completely destroyed. Your incense altars will be knocked down, and all that you made will be ruined.
7 Za a kashe mutanenku a cikinku, za ku kuwa sani ni ne Ubangiji.
People will be killed all throughout your country. Then you will know that I am the Lord.
8 “‘Amma zan bar waɗansu, gama waɗansunku za su tsere wa takobi sa’ad da aka watsar da ku a cikin ƙasashe da al’ummai.
However, I will let some of you survive and scatter you among the different nations and countries.
9 Sa’an nan a cikin al’ummai inda aka kai ku zaman bauta, waɗanda suka a tsere za su tuna da ni, yadda raina ya ɓaci ta wurin zukatansu marasa imani, waɗanda suka rabu da ni, da kuma ta wurin idanunsu, waɗanda suka yi sha’awace-sha’awacen gumakansu. Za su ji ƙyamar kansu saboda mugayen abubuwan da suka aikata.
Once they are they are there as prisoners in the nations, then the survivors will remember me. They will realize how sad they made me by their spiritual adultery as they deserted me with their eyes full of lust as they worshiped idols. They will hate themselves for the evil things they did, for all their disgusting sins.
10 Za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji; ba a banza na ce zan kawo musu wannan masifa ba.
Then they will know that I am the Lord, and that I was not pretending when I warned them about bringing this disaster upon them.
11 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce ku tafa hannuwanku tare ku kuma taka ƙafafunku ku yi ihu ku ce, “Kaito!” Saboda dukan mugaye da kuma abubuwan banƙyama na gidan Isra’ila, gama za su mutu ta wurin takobi, yunwa da annoba.
This is what the Lord God says: Hit yourself with your hands, stomp your feet, and shout out ‘Oh no!’ Do this because of all the terrible wickedness of the people of Israel. They are going to die by the sword and famine and disease.
12 Wanda yake da nisa zai mutu da annoba, shi da yake kusa kuma zai mutu ta takobi, wanda kuma ya tsira aka kuma bari zai mutu da yunwa. Ta haka zan aukar da fushina a kansu.
Those living far away will die from of disease, those who are close by will be killed by the sword, and those who are left will die of starvation. This is how I will express my anger towards them.
13 Za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da gawawwakin mutanensu suna kwance a kusa da gumakansu da kewaye da bagadansu, a kowane kan tudu mai tsawo da kuma a kan dukan kan duwatsu, a ƙarƙashin kowane inuwar itace da kuma kowane oak mai ganye, wuraren da suke ƙone turare masu ƙanshi wa dukan gumakansu.
Then you will know that I am the Lord—when the idol worshipers lie dead among their idols and altars on the top of every hill and mountain, and under every green tree and large oak. These were the pagan shrines where they offered sweet-smelling incense to all their idols.
14 Zan kuma miƙa hannuna a kansu in mai da ƙasarsu kango daga hamadan Dibila, a duk inda suke zama. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’”
I'm going to lift up my hand to punish them. In every place they live I will make their country a wasteland, all the way from the desert in the south to Diblah in the north. Then they will know that I am the Lord.”