< Ezekiyel 5 >

1 “Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi ka kuma yi amfani da shi kamar rezan mai aski don askin kanka da gemunka. Sa’an nan ka ɗauki ma’auni ka kuma raba gashin.
“Você, filho do homem, pegue uma espada afiada. Você deve tomá-la como uma navalha de barbeiro para si mesmo e fazê-la passar por cima de sua cabeça e por cima de sua barba. Em seguida, pegue balanças para pesar e dividir o cabelo.
2 Sa’ad da kwanakin ƙawanyarka sun ƙare, sai ka ƙone kashi ɗaya bisa uku na gashin da wuta a cikin birnin. Ka ɗauki kashi ɗaya bisa uku ka yayyanka shi da takobi kewaye da birnin. Ka kuma watsar da kashi ɗaya bisa uku a iska. Gama zan fafare su da takobin da aka zāre.
Uma terceira parte você queimará no fogo no meio da cidade, quando os dias do cerco forem cumpridos. Você pegará uma terceira parte, e golpeará com a espada em torno dela. Uma terceira parte você se espalhará ao vento, e eu desembainharei uma espada atrás deles.
3 Amma ka ɗibi gashi kaɗan ka daure a shafin rigarka.
Você pegará um pequeno número destes e os amarrará nas dobras de seu manto.
4 Har yanzu, ka ɗibi kaɗan na waɗannan ka zuba su cikin wuta su kuma ƙone. Wuta zai bazu daga nan zuwa dukan gidan Isra’ila.
Destes, novamente, você pegará e os lançará no meio do fogo, e os queimará no fogo. Dela sairá um fogo em toda a casa de Israel.
5 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Urushalima ce wannan, wadda na kafa a tsakiyar al’ummai, da ƙasashe kewaye da ita a ko’ina.
“O Senhor Javé diz: “Esta é Jerusalém. Eu a coloquei no meio das nações, e os países estão ao redor dela”.
6 Duk da haka cikin muguntarta ta yi tayarwa a kan dokokina da ƙa’idodina fiye da al’ummai da ƙasashe kewaye da ita. Ta ƙi dokokina ba tă kuwa bi ƙa’idodina ba.
Ela se rebelou contra minhas ordenanças ao fazer mal mais do que as nações, e contra meus estatutos mais do que os países que estão ao seu redor; pois eles rejeitaram minhas ordenanças, e quanto aos meus estatutos, eles não entraram nelas”.
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce kin yi ƙin ji fiye da al’umman da suke kewaye da ke ba ki kuma bi ƙa’idodina ko ki kiyaye dokokina ba. Ba ki ma dace da matsayin al’umman da suke kewaye da ke ba.
“Portanto, o Senhor Javé diz: 'Porque sois mais turbulento do que as nações que vos rodeiam, e não tendes andado nos meus estatutos, nem guardado as minhas ordenanças, nem seguido as ordenanças das nações que vos rodeiam;
8 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Ni kaina ina gāba da ke, Urushalima, kuma zan hukunta ki a gaban al’ummai.
portanto, o Senhor Javé diz: 'Eis que eu, eu mesmo, estou contra vós; e executarei juízos entre vós à vista das nações'.
9 Saboda dukan gumakan banƙyamarki, zan yi abin da ban taɓa yi ba, ba kuwa zan ƙara yinsa ba.
Farei em vós aquilo que não fiz, e que já não farei nada parecido, por causa de todas as vossas abominações.
10 Saboda haka a cikinki ubanni za su ci’ya’yansu,’ya’ya kuma za su ci ubanninsu. Zan hukunta ki zan kuma watsar da dukan waɗanda suke tsira da suke naki a iska.
Portanto, os pais comerão os filhos dentro de vocês, e os filhos comerão os pais deles. Executarei juízos sobre vocês; e espalharei todo o que resta de vocês a todos os ventos.
11 Saboda haka muddin ina a raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin kin ƙazantar da wuri mai tsarkina da dukan mugayen siffofinki da kuma ayyukanki masu banƙyama, ni kaina zan janye alherina; ba zan ji tausayinki ko in haƙura da ke ba.
Portanto, enquanto eu viver”, diz o Senhor Javé, “certamente, porque contaminastes meu santuário com todas as vossas coisas detestáveis, e com todas as vossas abominações, portanto, também eu vos diminuirei”. Meu olho não me poupará e não terei piedade”.
12 Kashi ɗaya bisa uku na mutanenki za su mutu da annoba ko su mutu da yunwa a cikinki; kashi ɗaya bisa uku takobi ne zai kashe su a waje da katangarki; kashi ɗaya bisa uku kuma zan watsar a iska in kuma fafare su da takobin da aka zāre.
Uma terceira parte de vocês morrerá com a peste, e eles serão consumidos pela fome dentro de vocês. Uma terceira parte cairá pela espada ao seu redor. Uma terceira parte espalharei a todos os ventos, e desembainharei uma espada atrás deles.
13 “Sa’an nan ne fushina zai huce hasalata a kanki kuma ta lafa, in kuma wartsake. Kuma sa’ad da na zuba fushina a kansu, a sa’an nan ne za su san cewa Ni Ubangiji na yi magana a cikin fushin kishina a kansu.
“'Assim, minha raiva será consumada, e farei descansar minha ira contra eles, e serei confortado. Eles saberão que eu, Yahweh, falei com meu zelo, quando eu tiver realizado minha ira sobre eles.
14 “Zan mai da ki kufai da kuma abin dariya a cikin al’ummai kewaye da ke, a gaban dukan waɗanda suke wucewa.
“'Além disso, farei de você uma desolação e uma reprovação entre as nações que estão ao seu redor, à vista de todos os que passam por você.
15 Za ki zama abin dariya da abin ba’a, kashedi da abin banrazana ga al’ummai kewaye da ke sa’ad da na hukunta ki cikin fushi da cikin hasala da kuma tsawatawa mai zafi. Ni Ubangiji na faɗa.
Portanto, será uma reprovação e um escárnio, uma instrução e um espanto, para as nações que estão ao seu redor, quando eu executar juízos sobre você com raiva e com ira, e com repreensões iradas - eu, Iavé, o disse -
16 Sa’ad da na harbe ki da mugayen kibiyoyina da kuma kibiyoyi masu hallakarwa na yunwa, zan yi harbi don in kashe ki. Zan kawo ƙarin yunwa a kanki in kuma yanke tanadin abincinki.
quando eu enviar sobre eles as flechas malignas da fome que são para destruição, que eu enviarei para destruí-lo. Aumentarei a fome em você e quebrarei seu bastão de pão.
17 Zan aika da yunwa da namun jeji a kanki, za su kuma bar ku ba’ya’ya. Annoba da zub da jini za su ratsa cikinki, zan kuma kawo takobi a kanki. Ni Ubangiji na faɗa.”
enviarei sobre vocês a fome e os animais malignos, e eles os despojarão. A peste e o sangue passarão por vocês. Eu trarei a espada sobre vocês. Eu, Yahweh, a falei”.

< Ezekiyel 5 >