< Ezekiyel 5 >

1 “Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi ka kuma yi amfani da shi kamar rezan mai aski don askin kanka da gemunka. Sa’an nan ka ɗauki ma’auni ka kuma raba gashin.
Et toi, fils de l'homme, prends avec toi un glaive plus tranchant que le rasoir d'un barbier; achète-le pour toi, et passe-le sur ta tête et sur ton menton; tu prendras ensuite des poids et une balance; puis tu sépareras ta barbe et tes cheveux.
2 Sa’ad da kwanakin ƙawanyarka sun ƙare, sai ka ƙone kashi ɗaya bisa uku na gashin da wuta a cikin birnin. Ka ɗauki kashi ɗaya bisa uku ka yayyanka shi da takobi kewaye da birnin. Ka kuma watsar da kashi ɗaya bisa uku a iska. Gama zan fafare su da takobin da aka zāre.
Tu en brûleras dans le feu un quart, au milieu de la ville, pendant que s'accompliront les jours du siège; tu en prendras un autre quart pour le brûler dans son enceinte; puis, avec le glaive, tu couperas le troisième quart autour de ses murailles; enfin tu jetteras au vent le dernier quart, que je poursuivrai à coups d'épée nue.
3 Amma ka ɗibi gashi kaɗan ka daure a shafin rigarka.
Et tu prendras quelque peu de poils, et tu les attacheras au bord de ton manteau.
4 Har yanzu, ka ɗibi kaɗan na waɗannan ka zuba su cikin wuta su kuma ƙone. Wuta zai bazu daga nan zuwa dukan gidan Isra’ila.
Et tu en prendras encore, et tu les jetteras au milieu du feu, et tu les brilleras dans le feu; il en sortira une flamme, et tu diras à toute la maison d'Israël:
5 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Urushalima ce wannan, wadda na kafa a tsakiyar al’ummai, da ƙasashe kewaye da ita a ko’ina.
Voici ce que dit le Seigneur: C'est là Jérusalem; je l'ai placée, elle et son territoire, au milieu des nations.
6 Duk da haka cikin muguntarta ta yi tayarwa a kan dokokina da ƙa’idodina fiye da al’ummai da ƙasashe kewaye da ita. Ta ƙi dokokina ba tă kuwa bi ƙa’idodina ba.
Et tu diras mes ordonnances à cette ville coupable entre toutes les nations, et mes préceptes aux peuples de son territoire; car ils ont répudié mes ordonnances, et ils n'ont point marché selon mes voies;
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce kin yi ƙin ji fiye da al’umman da suke kewaye da ke ba ki kuma bi ƙa’idodina ko ki kiyaye dokokina ba. Ba ki ma dace da matsayin al’umman da suke kewaye da ke ba.
À cause de cela, voici ce que dit le Seigneur: En punition de ce que les nations qui vous entourent ont été pour vous une occasion de péché; de ce que vous n'avez point cheminé selon mes préceptes, que vous n'avez point exécuté mes lois, mais que vous avez suivi celles des nations qui vous entourent;
8 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Ni kaina ina gāba da ke, Urushalima, kuma zan hukunta ki a gaban al’ummai.
À cause de cela, ainsi parle le Seigneur: Voilà que je suis contre toi, et au milieu de toi j'exécuterai mon jugement devant les nations.
9 Saboda dukan gumakan banƙyamarki, zan yi abin da ban taɓa yi ba, ba kuwa zan ƙara yinsa ba.
Et je ferai en toi des choses que je n'ai jamais faites, et telles que je n'en ferai jamais de semblables pour punir toutes tes abominations.
10 Saboda haka a cikinki ubanni za su ci’ya’yansu,’ya’ya kuma za su ci ubanninsu. Zan hukunta ki zan kuma watsar da dukan waɗanda suke tsira da suke naki a iska.
À cause de cela, les pères mangeront leurs enfants au milieu de toi, et les enfants mangeront leurs pères; et j'exécuterai en toi mon jugement, et je disperserai tes restes à tous les vents.
11 Saboda haka muddin ina a raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin kin ƙazantar da wuri mai tsarkina da dukan mugayen siffofinki da kuma ayyukanki masu banƙyama, ni kaina zan janye alherina; ba zan ji tausayinki ko in haƙura da ke ba.
À cause de cela, par ma vie, dit le Seigneur, en punition de ce que par toutes tes abominations tu as souillé mes choses saintes, je te répudierai; et mon œil sera sans pitié, et moi je serai sans miséricorde.
12 Kashi ɗaya bisa uku na mutanenki za su mutu da annoba ko su mutu da yunwa a cikinki; kashi ɗaya bisa uku takobi ne zai kashe su a waje da katangarki; kashi ɗaya bisa uku kuma zan watsar a iska in kuma fafare su da takobin da aka zāre.
Le quart des tiens périra par la peste; le quart périra par la famine au milieu de toi; le quart sera jeté par moi à tous les vents; le quart périra autour de toi par le glaive; et je les poursuivrai à coups d'épée nue.
13 “Sa’an nan ne fushina zai huce hasalata a kanki kuma ta lafa, in kuma wartsake. Kuma sa’ad da na zuba fushina a kansu, a sa’an nan ne za su san cewa Ni Ubangiji na yi magana a cikin fushin kishina a kansu.
Et ma colère et ma fureur s'assouvira contre eux, et tu connaîtras que moi, le Seigneur, j'ai parlé dans ma jalousie, pendant que j'assouvissais ma colère contre eux.
14 “Zan mai da ki kufai da kuma abin dariya a cikin al’ummai kewaye da ke, a gaban dukan waɗanda suke wucewa.
Et à la vue de tous les passants, je ferai un désert de toi et de tes filles qui entourent ton enceinte.
15 Za ki zama abin dariya da abin ba’a, kashedi da abin banrazana ga al’ummai kewaye da ke sa’ad da na hukunta ki cikin fushi da cikin hasala da kuma tsawatawa mai zafi. Ni Ubangiji na faɗa.
Et tu seras gémissante et digne de pitié au milieu des nations qui t'entourent, pendant que j'exécuterai sur toi mon jugement en me vengeant de toi selon ma colère.
16 Sa’ad da na harbe ki da mugayen kibiyoyina da kuma kibiyoyi masu hallakarwa na yunwa, zan yi harbi don in kashe ki. Zan kawo ƙarin yunwa a kanki in kuma yanke tanadin abincinki.
Moi, le Seigneur, j'ai parlé, et quand je lancerai contre eux les traits de la faim, ils seront en défaillance, et je briserai le soutien de leur pain;
17 Zan aika da yunwa da namun jeji a kanki, za su kuma bar ku ba’ya’ya. Annoba da zub da jini za su ratsa cikinki, zan kuma kawo takobi a kanki. Ni Ubangiji na faɗa.”
Et j'enverrai contre toi la famine et les bêtes farouches, et je me vengerai de toi, et la peste et le sang passeront sur toi, et je promènerai sur toi le glaive autour de ton enceinte. Moi, le Seigneur, j'ai parlé.

< Ezekiyel 5 >