< Ezekiyel 5 >

1 “Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi ka kuma yi amfani da shi kamar rezan mai aski don askin kanka da gemunka. Sa’an nan ka ɗauki ma’auni ka kuma raba gashin.
“Also, you human, [when you start doing those things, ] take a sharp sword and use it like [SIM] a razor to shave your head and your beard. Then put the hair that you shaved off on scales, and divide the [into three equal parts].
2 Sa’ad da kwanakin ƙawanyarka sun ƙare, sai ka ƙone kashi ɗaya bisa uku na gashin da wuta a cikin birnin. Ka ɗauki kashi ɗaya bisa uku ka yayyanka shi da takobi kewaye da birnin. Ka kuma watsar da kashi ɗaya bisa uku a iska. Gama zan fafare su da takobin da aka zāre.
When the time during [you will symbolize that] the city will be [by enemy troops] ends, put a third of the hair inside [drawing of the] city and burn it. Take another third of the hair, [scatter it] all [the drawing of] the city, and then strike it with your sword. That will symbolize that I will strike the people of Jerusalem [their enemies’] swords. Then allow the wind to scatter the other third of the hair. That will symbolize [even if they flee from the city], I will [cause their enemies to] pursue them and attack them with swords.
3 Amma ka ɗibi gashi kaɗan ka daure a shafin rigarka.
Take a few of your hairs and tuck them into the folds of your robe.
4 Har yanzu, ka ɗibi kaɗan na waɗannan ka zuba su cikin wuta su kuma ƙone. Wuta zai bazu daga nan zuwa dukan gidan Isra’ila.
Then take a few of those hairs, throw them into the fire, and burn them up. [That will symbolize that] a fire will spread from Jerusalem [and destroy things] throughout Israel.
5 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Urushalima ce wannan, wadda na kafa a tsakiyar al’ummai, da ƙasashe kewaye da ita a ko’ina.
This is what [I, ] Yahweh the Lord, say: ‘[drawing will represent] Jerusalem, [the city which] I have set in the center of the nations, with [other] countries around it.
6 Duk da haka cikin muguntarta ta yi tayarwa a kan dokokina da ƙa’idodina fiye da al’ummai da ƙasashe kewaye da ita. Ta ƙi dokokina ba tă kuwa bi ƙa’idodina ba.
But the wicked people of Jerusalem rebelled against [obeying] my commands, and [they show that] they are more wicked than the people of the surrounding countries. They rejected my laws and refused to obey my commands.’
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce kin yi ƙin ji fiye da al’umman da suke kewaye da ke ba ki kuma bi ƙa’idodina ko ki kiyaye dokokina ba. Ba ki ma dace da matsayin al’umman da suke kewaye da ke ba.
Therefore, this is what I, Yahweh the Lord, say: ‘You people of Jerusalem have been more rebellious than the people of the nations around you; you have not obeyed any of my laws [DOU]. You have not even obeyed the laws of the nations around you!’
8 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Ni kaina ina gāba da ke, Urushalima, kuma zan hukunta ki a gaban al’ummai.
Therefore, this is [I, ] Yahweh the Lord, say: ‘I am opposed to [you people of] Jerusalem. I will punish you, and the [people of other] nations will see it happen.
9 Saboda dukan gumakan banƙyamarki, zan yi abin da ban taɓa yi ba, ba kuwa zan ƙara yinsa ba.
Because of all your detestable [idols], I will punish [people of Jerusalem] like I have never done before and will never do again.
10 Saboda haka a cikinki ubanni za su ci’ya’yansu,’ya’ya kuma za su ci ubanninsu. Zan hukunta ki zan kuma watsar da dukan waɗanda suke tsira da suke naki a iska.
As a result, parents among you will eat their children, and children will eat their [because there will be nothing else to eat]. I will punish you [severely], and I will cause those who will still be alive to be scattered in all directions [IDM].’
11 Saboda haka muddin ina a raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin kin ƙazantar da wuri mai tsarkina da dukan mugayen siffofinki da kuma ayyukanki masu banƙyama, ni kaina zan janye alherina; ba zan ji tausayinki ko in haƙura da ke ba.
Therefore, I, Yahweh the Lord, declare that as surely as I am alive, because you have polluted my temple with all your disgusting [statues of idols] and by the other detestable things that you do, I will no longer bless you. I will not pity [you] or act mercifully [toward you].
12 Kashi ɗaya bisa uku na mutanenki za su mutu da annoba ko su mutu da yunwa a cikinki; kashi ɗaya bisa uku takobi ne zai kashe su a waje da katangarki; kashi ɗaya bisa uku kuma zan watsar a iska in kuma fafare su da takobin da aka zāre.
One-third of your people will die inside the city because of the plagues [they will experience] or by (famine/lack of food). One-third of your people will be killed [your enemies’] swords outside the city. And one-third I will cause to be scattered in all directions; [your enemies] will [still] pursue you and kill you with their swords.
13 “Sa’an nan ne fushina zai huce hasalata a kanki kuma ta lafa, in kuma wartsake. Kuma sa’ad da na zuba fushina a kansu, a sa’an nan ne za su san cewa Ni Ubangiji na yi magana a cikin fushin kishina a kansu.
Then I will no longer be angry with you; I will stop punishing [MTY] you after I have gotten revenge on you. And when I stop punishing you, you will know that I, Yahweh, have spoken to you because I have been very strongly concerned [what you have done].
14 “Zan mai da ki kufai da kuma abin dariya a cikin al’ummai kewaye da ke, a gaban dukan waɗanda suke wucewa.
I will cause your [city] to be a ruins, with the result that [people of other] nations that are around you will pass by and see it and sneer at you.
15 Za ki zama abin dariya da abin ba’a, kashedi da abin banrazana ga al’ummai kewaye da ke sa’ad da na hukunta ki cikin fushi da cikin hasala da kuma tsawatawa mai zafi. Ni Ubangiji na faɗa.
They will make fun of you and taunt you. When I severely punish you because of my being very angry [DOU] with you, they will be horrified and they will be warned. [That will surely happen because] I, Yahweh, have said it.
16 Sa’ad da na harbe ki da mugayen kibiyoyina da kuma kibiyoyi masu hallakarwa na yunwa, zan yi harbi don in kashe ki. Zan kawo ƙarin yunwa a kanki in kuma yanke tanadin abincinki.
When I cut off your food supply and cause there to be more famine, [it will be as though] [MET] I am shooting at you with my arrows that will destroy you.
17 Zan aika da yunwa da namun jeji a kanki, za su kuma bar ku ba’ya’ya. Annoba da zub da jini za su ratsa cikinki, zan kuma kawo takobi a kanki. Ni Ubangiji na faɗa.”
I will cause you to experience a famine, and I will send wild beasts to attack you and your children, and [all] your children will be killed. You will experience plagues and wars, and I will cause [your enemies] to attack you with their swords. [That will surely happen because] I, Yahweh, have said it.”

< Ezekiyel 5 >