< Ezekiyel 5 >

1 “Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi ka kuma yi amfani da shi kamar rezan mai aski don askin kanka da gemunka. Sa’an nan ka ɗauki ma’auni ka kuma raba gashin.
And thou, son of man, take thee a sharp instrument, even a barber's razor, and cause it to pass upon thy head and thy beard; and take thee weighing-balances, and divide the hair.
2 Sa’ad da kwanakin ƙawanyarka sun ƙare, sai ka ƙone kashi ɗaya bisa uku na gashin da wuta a cikin birnin. Ka ɗauki kashi ɗaya bisa uku ka yayyanka shi da takobi kewaye da birnin. Ka kuma watsar da kashi ɗaya bisa uku a iska. Gama zan fafare su da takobin da aka zāre.
A third part shalt thou burn with fire in the midst of the city, when the days of the siege are fulfilled; and thou shalt take a third part and smite it round about with the sword; and a third part shalt thou scatter in the wind, and I will draw out a sword after them.
3 Amma ka ɗibi gashi kaɗan ka daure a shafin rigarka.
Thou shalt also take thereof a small number, and bind them in thy skirts.
4 Har yanzu, ka ɗibi kaɗan na waɗannan ka zuba su cikin wuta su kuma ƙone. Wuta zai bazu daga nan zuwa dukan gidan Isra’ila.
And of these again take some and cast them into the fire, and burn them in the fire. From them shall a fire come forth upon the whole house of Israel.
5 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Urushalima ce wannan, wadda na kafa a tsakiyar al’ummai, da ƙasashe kewaye da ita a ko’ina.
Thus saith the Lord Jehovah: This is Jerusalem; in the midst of the nations have I set her, and countries are round about her.
6 Duk da haka cikin muguntarta ta yi tayarwa a kan dokokina da ƙa’idodina fiye da al’ummai da ƙasashe kewaye da ita. Ta ƙi dokokina ba tă kuwa bi ƙa’idodina ba.
But she hath wickedly resisted my ordinances more than the nations, and my statutes more than the countries, that are round about her. For they have refused my ordinances, and have not walked in my statutes.
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce kin yi ƙin ji fiye da al’umman da suke kewaye da ke ba ki kuma bi ƙa’idodina ko ki kiyaye dokokina ba. Ba ki ma dace da matsayin al’umman da suke kewaye da ke ba.
Therefore thus saith the Lord Jehovah: Because ye have been rebellious more than the nations that are round about you, and have not walked in my statutes, nor kept my ordinances, but have done according to the ordinances of the nations which are round about you,
8 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Ni kaina ina gāba da ke, Urushalima, kuma zan hukunta ki a gaban al’ummai.
therefore thus saith the Lord Jehovah: Behold I, even I, am against thee, and will execute judgments against thee in the sight of the nations.
9 Saboda dukan gumakan banƙyamarki, zan yi abin da ban taɓa yi ba, ba kuwa zan ƙara yinsa ba.
I will do to thee that which I have not yet done, and the like of which I shall not do again, because of all thine iniquities.
10 Saboda haka a cikinki ubanni za su ci’ya’yansu,’ya’ya kuma za su ci ubanninsu. Zan hukunta ki zan kuma watsar da dukan waɗanda suke tsira da suke naki a iska.
Therefore the fathers shall eat the sons in the midst of thee, and the sons shall eat their fathers; and I will execute judgments in thee, and I will scatter the whole remnant of thee to all the winds.
11 Saboda haka muddin ina a raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin kin ƙazantar da wuri mai tsarkina da dukan mugayen siffofinki da kuma ayyukanki masu banƙyama, ni kaina zan janye alherina; ba zan ji tausayinki ko in haƙura da ke ba.
Therefore, as I live, saith the Lord Jehovah, because thou hast polluted my sanctuary with all thy detestable things, and with all thine abominations, therefore will I also withdraw mine eye from thee; neither will I spare, neither will I have any pity.
12 Kashi ɗaya bisa uku na mutanenki za su mutu da annoba ko su mutu da yunwa a cikinki; kashi ɗaya bisa uku takobi ne zai kashe su a waje da katangarki; kashi ɗaya bisa uku kuma zan watsar a iska in kuma fafare su da takobin da aka zāre.
A third part of thee shall die by the pestilence, or be consumed with hunger in the midst of thee; and a third part shall die by the sword round about thee; and a third part will I scatter to all the winds, and I will draw out a sword after them.
13 “Sa’an nan ne fushina zai huce hasalata a kanki kuma ta lafa, in kuma wartsake. Kuma sa’ad da na zuba fushina a kansu, a sa’an nan ne za su san cewa Ni Ubangiji na yi magana a cikin fushin kishina a kansu.
Thus shall mine anger be accomplished, and I will satiate my fury upon them, and receive satisfaction; and they shall know that I, Jehovah, have spoken it in my zeal, when I shall have accomplished my fury upon them.
14 “Zan mai da ki kufai da kuma abin dariya a cikin al’ummai kewaye da ke, a gaban dukan waɗanda suke wucewa.
Moreover, I will make thee a waste, and a reproach among the nations that are round about thee, in the sight of all that pass by.
15 Za ki zama abin dariya da abin ba’a, kashedi da abin banrazana ga al’ummai kewaye da ke sa’ad da na hukunta ki cikin fushi da cikin hasala da kuma tsawatawa mai zafi. Ni Ubangiji na faɗa.
And thou shalt be a reproach, and a reviling, and a warning, and an astonishment to the nations that are round about thee, when I shall execute judgments upon thee in anger, and in fury, and in furious rebukes; —I, Jehovah, have spoken it; —
16 Sa’ad da na harbe ki da mugayen kibiyoyina da kuma kibiyoyi masu hallakarwa na yunwa, zan yi harbi don in kashe ki. Zan kawo ƙarin yunwa a kanki in kuma yanke tanadin abincinki.
when I shall send upon you the evil arrows of famine which bring destruction, which I send to destroy you, and increase the famine upon you, and break your staff of bread.
17 Zan aika da yunwa da namun jeji a kanki, za su kuma bar ku ba’ya’ya. Annoba da zub da jini za su ratsa cikinki, zan kuma kawo takobi a kanki. Ni Ubangiji na faɗa.”
And I will send upon you famine, and evil beasts, which shall make thee childless; and pestilence and blood shall pass through thee; and the sword will I bring upon thee. I, Jehovah, have spoken it.

< Ezekiyel 5 >