< Ezekiyel 5 >
1 “Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki takobi mai kaifi ka kuma yi amfani da shi kamar rezan mai aski don askin kanka da gemunka. Sa’an nan ka ɗauki ma’auni ka kuma raba gashin.
Og du, Menneskesøn, tag dig et skarpt Sværd, brug det som Ragekniv og lad det gaa over dit Hoved og dit Skæg; tag dig saa en Vægtskaal og del Haaret.
2 Sa’ad da kwanakin ƙawanyarka sun ƙare, sai ka ƙone kashi ɗaya bisa uku na gashin da wuta a cikin birnin. Ka ɗauki kashi ɗaya bisa uku ka yayyanka shi da takobi kewaye da birnin. Ka kuma watsar da kashi ɗaya bisa uku a iska. Gama zan fafare su da takobin da aka zāre.
En Tredjedel skal du brænde i et Baal midt i Byen, naar Belejringens Dage er omme; en Tredjedel skal du tage og slaa den med Sværdet rundt om Byen; og en Tredjedel skal du sprede for Vinden; saa drager jeg Sværdet bag dem.
3 Amma ka ɗibi gashi kaɗan ka daure a shafin rigarka.
Derefter skal du tage lidt deraf og svøbe det ind i din Kappeflig;
4 Har yanzu, ka ɗibi kaɗan na waɗannan ka zuba su cikin wuta su kuma ƙone. Wuta zai bazu daga nan zuwa dukan gidan Isra’ila.
og deraf skal du atter tage noget og kaste det midt ind i Ilden og brænde det. Og du skal sige til hele Israels Hus:
5 “Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Urushalima ce wannan, wadda na kafa a tsakiyar al’ummai, da ƙasashe kewaye da ita a ko’ina.
Saa siger den Herre HERREN: Dette er Jerusalem; jeg satte det midt iblandt Folkene, omgivet af lande.
6 Duk da haka cikin muguntarta ta yi tayarwa a kan dokokina da ƙa’idodina fiye da al’ummai da ƙasashe kewaye da ita. Ta ƙi dokokina ba tă kuwa bi ƙa’idodina ba.
Men det var gudløst og genstridigt mod mine Lovbud mere end Folkene og mod mine Vedtægter mere end Landene rundt om; thi de lod haant om mine Lovbud og vandrede ikke efter mine Vedtægter.
7 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce kin yi ƙin ji fiye da al’umman da suke kewaye da ke ba ki kuma bi ƙa’idodina ko ki kiyaye dokokina ba. Ba ki ma dace da matsayin al’umman da suke kewaye da ke ba.
Derfor, saa siger den Herre HERREN: Fordi I var mere genstridige end Folkene rundt om og ikke vandrede efter mine Vedtægter eller holdt mine Lovbud, men gjorde efter de omboende Folks Lovbud,
8 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce Ni kaina ina gāba da ke, Urushalima, kuma zan hukunta ki a gaban al’ummai.
derfor, saa siger den Herre HERREN: Se, jeg kommer over dig og holder Dom i din Midte for Folkenes Øjne.
9 Saboda dukan gumakan banƙyamarki, zan yi abin da ban taɓa yi ba, ba kuwa zan ƙara yinsa ba.
For alle dine Vederstyggeligheders Skyld vil jeg gøre med dig, hvad jeg aldrig har gjort og aldrig vil gøre Mage til.
10 Saboda haka a cikinki ubanni za su ci’ya’yansu,’ya’ya kuma za su ci ubanninsu. Zan hukunta ki zan kuma watsar da dukan waɗanda suke tsira da suke naki a iska.
Derfor skal Fædre æde deres Børn i din Midte og Børn deres Fædre; jeg holder Dom over dig, og alle, som er til Rest i dig, spreder jeg for alle Vinde.
11 Saboda haka muddin ina a raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin kin ƙazantar da wuri mai tsarkina da dukan mugayen siffofinki da kuma ayyukanki masu banƙyama, ni kaina zan janye alherina; ba zan ji tausayinki ko in haƙura da ke ba.
Derfor, saa sandt jeg lever, lyder det fra den Herre HERREN: Sandelig, fordi du gjorde min Helligdom uren med alle dine væmmelige Guder og Vederstyggeligheder, vil jeg ogsaa støde dig fra mig uden Medynk eller Skaansel.
12 Kashi ɗaya bisa uku na mutanenki za su mutu da annoba ko su mutu da yunwa a cikinki; kashi ɗaya bisa uku takobi ne zai kashe su a waje da katangarki; kashi ɗaya bisa uku kuma zan watsar a iska in kuma fafare su da takobin da aka zāre.
En Tredjedel af dig skal dø af Pest og omkomme af Hunger i din Midte, en Tredjedel skal falde for Sværdet rundt om dig, og en Tredjedel spreder jeg for alle Vinde og drager Sværdet bag dem.
13 “Sa’an nan ne fushina zai huce hasalata a kanki kuma ta lafa, in kuma wartsake. Kuma sa’ad da na zuba fushina a kansu, a sa’an nan ne za su san cewa Ni Ubangiji na yi magana a cikin fushin kishina a kansu.
Min Vrede skal udtømme sig, og jeg vil køle min Harme paa dem og tage Hævn, saa de skal kende at jeg, HERREN, har talet i min Nidkærhed, naar jeg udtømmer min Vrede over dem.
14 “Zan mai da ki kufai da kuma abin dariya a cikin al’ummai kewaye da ke, a gaban dukan waɗanda suke wucewa.
Jeg gør dig til en Grushob og til Spot blandt Folkene rundt om, for Øjnene af enhver, som drager forbi.
15 Za ki zama abin dariya da abin ba’a, kashedi da abin banrazana ga al’ummai kewaye da ke sa’ad da na hukunta ki cikin fushi da cikin hasala da kuma tsawatawa mai zafi. Ni Ubangiji na faɗa.
Du skal blive til Spot og Haan, til Advarsel og Rædsel for Folkene rundt om, naar jeg holder Dom over dig i Vrede og Harme og harm fuld Revselse. Jeg, HERREN, har talet!
16 Sa’ad da na harbe ki da mugayen kibiyoyina da kuma kibiyoyi masu hallakarwa na yunwa, zan yi harbi don in kashe ki. Zan kawo ƙarin yunwa a kanki in kuma yanke tanadin abincinki.
Naar jeg sender Hungerens onde Pile mod eder, og de, som jeg sender for at ødelægge eder, volder Ødelæggelse, og jeg lader Hungeren tage til, da sønderbryder jeg Brødets Støttestav for eder
17 Zan aika da yunwa da namun jeji a kanki, za su kuma bar ku ba’ya’ya. Annoba da zub da jini za su ratsa cikinki, zan kuma kawo takobi a kanki. Ni Ubangiji na faɗa.”
og sender Hunger over eder og Rovdyr, som skal affolke dig; Pest og Blodsudgydelse skal hjemsøge dig, og jeg bringer Sværd over dig. Jeg, HERREN, har talet.