< Ezekiyel 47 >

1 Mutumin ya komo da ni zuwa mashigin haikalin, sai na kuwa ga ruwa yana malalowa daga ƙarƙashin madogarar ƙofar haikalin wajen gabas (gama haikalin yana fuskantar gabas). Ruwan yana malalowa daga ƙarƙashin gefen kudun haikalin, kudu da bagaden.
Et il me conduisit sous les portiques du temple; et là de l'eau sortait de la cour et coulait à l'orient; car la façade du temple regardait l'orient, et l'eau descendait à droite au midi de l'autel.
2 Sai ya fitar da ni ta ƙofar arewa ya kewaye da ni ta waje zuwa ƙofar da take waje mai fuskantar gabas, ruwan kuwa yana malalowa daga wajen kudu.
Et il me fit sortir par le chemin de la porte de l'aquilon; et il me fit tourner par le chemin extérieur jusqu'à la porte du parvis qui regarde l'orient, et voilà que l'eau coulait du côté droit,
3 Yayinda mutumin ya yi wajen gabas da karan awo a hannunsa, sai ya auna kamu dubu ya kuma bi da ni ta ruwan da zurfinsa ya kama ni a idon ƙafa.
Dans la direction qu'avait prise l'homme en sortant, et devant lui; or il tenait à la main son cordeau, et il mesura mille coudées, et il traversa l'eau, cette eau qui jaillissait de la cour.
4 Ya auna wani kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa ya kai ni gwiwa. Ya sāke auna kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa kama ni a gindi.
Et il mesura mille coudées, et il traversa l'eau, et il en eut jusqu'aux cuisses. Et il mesura mille coudées, et il traversa l'eau, et il en eut jusqu'aux reins.
5 Ya auna wani kamu dubu, amma a yanzu ruwan ya zama kogin da ban iya hayewa ba, domin ruwan ya taso ya kuma yi zurfin da ya isa a yi iyo a ciki, kogin da ba za a iya hayewa ba.
Et il mesura mille coudées, et il ne put traverser, parce que l'eau débordait comme un torrent infranchissable.
6 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan?” Sa’an nan ya komo da ni zuwa bakin kogin.
Et il me dit: As-tu vu, fils de l'homme? et il me guida, et il me ramena sur la rive du fleuve
7 Sa’ad da na iso can, sai na ga itatuwa masu yawa a kowane gefen kogin.
Par laquelle je pouvais revenir. Et voilà qu'il y avait sur les deux rives du fleuve une grande multitude d'arbres.
8 Sai ya ce mini, “Wannan ruwa yana malalowa zuwa yankin gabas ya kuma gangaro zuwa cikin Araba, inda zai shiga Teku. Sa’ad da ya shiga cikin Tekun sai ruwan a can ya zama mai daɗi.
Et il me dit: Cette eau sort de la Galilée, qui est vers l'Orient, puis elle descend vers l'Arabie, et va jusqu'à la mer, jusqu'à l'eau qui en sort, et elle assainira toutes les eaux.
9 Tarin halittu masu rai za su rayu a duk inda ruwan ya malalo. Za a kasance da kifi masu yawa, domin wannan ruwa yana malalowa a can yana kuma mai da ruwan gishiri yă zama ruwa mai daɗi; saboda haka duk inda ruwan ya malalo, kome zai rayu.
Et ceci arrivera: toute âme de créature vivant et se mourant sur tout lieu où ce fleuve passera, vivra; et il y aura là une multitude de poissons, parce que l'eau y sera venue; et où sera passé le fleuve tout être sera sain, et il vivra, et il vivra en ce lieu.
10 Masunta za su tsaya a gaɓar; daga En Gedi zuwa En Eglayim, za a kasance da wuraren jefa abin kamun kifi. Za a sami kifayen iri-iri, kamar kifaye Bahar Rum.
Et il y viendra des pêcheurs depuis Engaddi jusqu'à Engallim; et le long de ce fleuve ils feront sécher leurs filets; et ses poissons seront, comme ceux de la grande mer, en grande multitude.
11 Amma fadamun da tafkunan ba za su zama masu daɗi ba; za a bar su a gishirinsu.
Et à son embouchure et dans ses détours, et dans ses débordements, ses eaux ne seront point assainies; on s'en servira pour en tirer le sel.
12 ’Ya’yan itatuwa na kowane iri za su yi girma a kowane gefen kogin. Ganyayensu ba su bushe ba, ba kuwa za su fasa yin’ya’ya ba. Kowane wata za su ba da’ya’ya domin ruwa daga wuri mai tsarki yana malalo musu.’Ya’yansu za su zama abinci, ganyayensu kuma za su zama magani.”
Et tout arbre fruitier croîtra au bord du fleuve sur ses deux rives; nul n'y dépérira et n'y manquera de fruits; dès sa première pousse, il produira, parce que les eaux qui l'arrosent sortent du lieu saint; et ses fruits seront bons à manger, et ses feuilles rendront la santé.
13 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Waɗannan su ne iyakokin da za ku raba ƙasar gādo cikin kabilan Isra’ila goma sha biyu, da rabo biyu don Yusuf.
Voici ce que dit le Seigneur: Je vais vous indiquer les limites de cette terre que vous vous partagerez au cordeau, entre les douze tribus des fils d'Israël.
14 Za ku raba ta daidai a cikinsu. Gama na ɗaga hannu na rantse zan ba da ita ga kakanninku, wannan ƙasa za tă zama gādonku.
Et dans ce partage chacun aura autant que son frère, de cette terre sur laquelle j'ai levé la main pour la donner à vos pères; et elle sera votre héritage.
15 “Wannan ce za tă zama iyakar ƙasa. “A wajen arewa za tă fara daga Bahar Rum ta hanyar Hetlon ta wuce Lebo Hamat zuwa Zedad,
Et voici les limites de cette terre à l'aquilon: depuis la grande mer, qui s'y enfonce et forme un golfe à l'entrée d'Émaseldam
16 Berota da Sibrayim (wadda take a iyaka tsakanin Damaskus da Hamat), har zuwa Hazer-Hattikon, wadda take a iyakar Hauran.
Maabthéras, Hébraméliam, entre les confins de Damas et ceux d'Emath, le val de Saunan; le tout au-dessus des confins de l'Anranitide.
17 Iyakar za tă miƙe daga teku zuwa Hazar-Enon, ta iyakar Damaskus, da iyakar Hamat a arewa. Wannan ita ce iyakar a wajen arewa.
Voilà les limites depuis la mer; depuis le val d'Enan, ce sont les confins de Damas et les limites du côté de l'aquilon.
18 A wajen gabas iyakar za tă kama tsakanin Hauran da Damaskus, ta bi ta Urdun tsakanin Gileyad da ƙasar Isra’ila, zuwa tekun gabas har zuwa Tamar. Wannan ita ce iyakar a wajen gabas.
Celles du côté du levant passeront entre la Loranitide, Damas, la Galaaditide, et entre la terre d'Israël; le Jourdain les limitera vers la mer qui est au levant de la ville des Palmiers. Voilà les limites à l'orient.
19 A wajen kudu za tă fara daga Tamar har zuwa ruwan Meriba Kadesh, sa’an nan ta bi Rafin Masar zuwa Bahar Rum. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
Celles du midi et du sud-ouest s'étendront de Théman et de la ville des Palmiers, jusqu'aux eaux de Barimoth-Cadès, d'où elles rejoindront la grande mer.
20 A wajen yamma, Bahar Rum ne zai zama iyakar zuwa wani wuri ɗaura da Lebo Hamat. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
Telle est la limite du. sud et du sud-ouest; celle de l'occident est la grande mer elle-même; elle va jusqu'au golfe d'Emath; telle est la limite vers la mer d'Émath.
21 “Za ku rarraba wannan ƙasa a tsakaninku bisa ga kabilan Isra’ila.
Et vous partagerez pour eux cette terre entre les tribus d'Israël.
22 Za ku raba ta kamar gādo wa kanku da kuma wa baƙin da suka zauna a cikinku waɗanda suke da’ya’ya. Za ku ɗauka su kamar’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa; za su yi gādo tare da ku a cikin kabilan Isra’ila.
Vous les partagerez au sort, pour vous et pour les étrangers qui résident parmi vous, et qui ont eu des enfants au milieu de vous; et ils seront pour vous comme des indigènes au milieu des fils d'Israël. Ils mangeront avec vous les fruits de votre héritage au milieu des fils d'Israël.
23 A duk kabilar da baƙon yake zama, a can za ku ba shi gādonsa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Et dans la tribu où se trouveront des prosélytes, vous leur donnerez un héritage, dit le Seigneur Dieu.

< Ezekiyel 47 >