< Ezekiyel 47 >
1 Mutumin ya komo da ni zuwa mashigin haikalin, sai na kuwa ga ruwa yana malalowa daga ƙarƙashin madogarar ƙofar haikalin wajen gabas (gama haikalin yana fuskantar gabas). Ruwan yana malalowa daga ƙarƙashin gefen kudun haikalin, kudu da bagaden.
And he brought back me to [the] entrance of the house and there! waters [were] going out from under [the] threshold of the house east-ward for [the] face of the house [was] east and the waters [were] going down from under from [the] side of the house south from [the] south of the altar.
2 Sai ya fitar da ni ta ƙofar arewa ya kewaye da ni ta waje zuwa ƙofar da take waje mai fuskantar gabas, ruwan kuwa yana malalowa daga wajen kudu.
And he brought out me [the] way of [the] gate north-ward and he brought round me [the] way of [the] outside to [the] gate of the outside [the] way which faces east and there! waters [were] trickling from the side south.
3 Yayinda mutumin ya yi wajen gabas da karan awo a hannunsa, sai ya auna kamu dubu ya kuma bi da ni ta ruwan da zurfinsa ya kama ni a idon ƙafa.
When went out the man east and a measuring-line [was] in hand his and he measured out a thousand by the cubit and he made pass me in the waters waters of ankles.
4 Ya auna wani kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa ya kai ni gwiwa. Ya sāke auna kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa kama ni a gindi.
And he measured out a thousand [cubits] and he made pass me in the waters waters knees and he measured out a thousand [cubits] and he made pass through me waters of loins.
5 Ya auna wani kamu dubu, amma a yanzu ruwan ya zama kogin da ban iya hayewa ba, domin ruwan ya taso ya kuma yi zurfin da ya isa a yi iyo a ciki, kogin da ba za a iya hayewa ba.
And he measured out a thousand [cubits] a river which not I was able to pass through for they had risen the waters waters of swimming a river which not it was passed through.
6 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan?” Sa’an nan ya komo da ni zuwa bakin kogin.
And he said to me ¿ do you see O son of humankind and he led me and he brought back me [the] bank of the river.
7 Sa’ad da na iso can, sai na ga itatuwa masu yawa a kowane gefen kogin.
When had returned I and there! [was] to [the] bank of the river tree[s] many very from this and from this.
8 Sai ya ce mini, “Wannan ruwa yana malalowa zuwa yankin gabas ya kuma gangaro zuwa cikin Araba, inda zai shiga Teku. Sa’ad da ya shiga cikin Tekun sai ruwan a can ya zama mai daɗi.
And he said to me the waters these [are] going out to the territory eastern and they will go down to the Arabah and they will go the sea towards to the sea those [which] were brought out (and they will be healed *Q(k)*) the waters.
9 Tarin halittu masu rai za su rayu a duk inda ruwan ya malalo. Za a kasance da kifi masu yawa, domin wannan ruwa yana malalowa a can yana kuma mai da ruwan gishiri yă zama ruwa mai daɗi; saboda haka duk inda ruwan ya malalo, kome zai rayu.
And it will be every creature living - which it swarms to every where it will go there two rivers it will live and it will be the fish many very for they have gone there towards the waters these so they may be healed and it will live every where it will go there towards the river.
10 Masunta za su tsaya a gaɓar; daga En Gedi zuwa En Eglayim, za a kasance da wuraren jefa abin kamun kifi. Za a sami kifayen iri-iri, kamar kifaye Bahar Rum.
And it will be (they have stood *Q(K)*) at it fishermen from En Gedi and to En-eglaim a spreading place for nets they will be to kind its it will be fish their like [the] fish of the sea great many very.
11 Amma fadamun da tafkunan ba za su zama masu daɗi ba; za a bar su a gishirinsu.
(Swamps its *Q(K)*) and marshes its and not they will be healed to salt they will be given.
12 ’Ya’yan itatuwa na kowane iri za su yi girma a kowane gefen kogin. Ganyayensu ba su bushe ba, ba kuwa za su fasa yin’ya’ya ba. Kowane wata za su ba da’ya’ya domin ruwa daga wuri mai tsarki yana malalo musu.’Ya’yansu za su zama abinci, ganyayensu kuma za su zama magani.”
And at the river it will grow up on bank its from this - and from this - every tree of food not it will wither leafage its and not it will be finished fruit its to months its it will bear early fruit for waters its from the sanctuary they [are] coming out (and it will be *Q(K)*) fruit its for food and leafage its [will be] for healing.
13 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Waɗannan su ne iyakokin da za ku raba ƙasar gādo cikin kabilan Isra’ila goma sha biyu, da rabo biyu don Yusuf.
Thus he says [the] Lord Yahweh this [is the] boundary which you will give as possession the land to two [plus] ten [the] tribes of Israel Joseph measured portions.
14 Za ku raba ta daidai a cikinsu. Gama na ɗaga hannu na rantse zan ba da ita ga kakanninku, wannan ƙasa za tă zama gādonku.
And you will divide as possession it each like brother his which I lifted up hand my to give it to ancestors your and it will fall the land this to you an inheritance.
15 “Wannan ce za tă zama iyakar ƙasa. “A wajen arewa za tă fara daga Bahar Rum ta hanyar Hetlon ta wuce Lebo Hamat zuwa Zedad,
And this [is] [the] boundary of the land to [the] side of north-ward from the sea great the direction of Hethlon Lebo Zedad towards.
16 Berota da Sibrayim (wadda take a iyaka tsakanin Damaskus da Hamat), har zuwa Hazer-Hattikon, wadda take a iyakar Hauran.
Hamath - Berothah Sibraim which [is] between [the] territory of Damascus and between [the] territory of Hamath Hazer-hattikon which [is] to [the] border of Hauran.
17 Iyakar za tă miƙe daga teku zuwa Hazar-Enon, ta iyakar Damaskus, da iyakar Hamat a arewa. Wannan ita ce iyakar a wajen arewa.
And it will be [the] boundary from the sea Hazar Enan [the] border of Damascus and north - north-ward and [the] territory of Hamath and [the] side of [the] north.
18 A wajen gabas iyakar za tă kama tsakanin Hauran da Damaskus, ta bi ta Urdun tsakanin Gileyad da ƙasar Isra’ila, zuwa tekun gabas har zuwa Tamar. Wannan ita ce iyakar a wajen gabas.
And [will be the] side of [the] east from between Hauran and from between Damascus and from between Gilead and from between [the] land of Israel the Jordan from [the] border to the sea eastern Tamar and [the] side east-ward.
19 A wajen kudu za tă fara daga Tamar har zuwa ruwan Meriba Kadesh, sa’an nan ta bi Rafin Masar zuwa Bahar Rum. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
And [the] side of [the] south south-ward [will be] from Tamar to [the] waters of Meribath Kadesh [the] wadi to the sea great and [the] side of south-ward south-ward.
20 A wajen yamma, Bahar Rum ne zai zama iyakar zuwa wani wuri ɗaura da Lebo Hamat. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
And [the] side of [the] west [is] the sea great from [the] border to opposite Lebo Hamath this [is the] side of [the] west.
21 “Za ku rarraba wannan ƙasa a tsakaninku bisa ga kabilan Isra’ila.
And you will divide the land this for yourselves to [the] tribes of Israel.
22 Za ku raba ta kamar gādo wa kanku da kuma wa baƙin da suka zauna a cikinku waɗanda suke da’ya’ya. Za ku ɗauka su kamar’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa; za su yi gādo tare da ku a cikin kabilan Isra’ila.
And it will be you will make fall it an inheritance for yourselves and for the sojourners who sojourn in midst of you who they have fathered children in midst of you and they will be to you like [the] native-born among [the] people of Israel with you they will fall an inheritance in among [the] tribes of Israel.
23 A duk kabilar da baƙon yake zama, a can za ku ba shi gādonsa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And it will be in the tribe which he has sojourned the sojourner with it there you will give [him] inheritance his [the] utterance of [the] Lord Yahweh.