< Ezekiyel 47 >
1 Mutumin ya komo da ni zuwa mashigin haikalin, sai na kuwa ga ruwa yana malalowa daga ƙarƙashin madogarar ƙofar haikalin wajen gabas (gama haikalin yana fuskantar gabas). Ruwan yana malalowa daga ƙarƙashin gefen kudun haikalin, kudu da bagaden.
The man took me back to the Temple entrance. I saw water coming out from under the threshold of the Temple and flowing east (because the Temple faced east). The water was coming from under the south side of the Temple and ran south of the altar.
2 Sai ya fitar da ni ta ƙofar arewa ya kewaye da ni ta waje zuwa ƙofar da take waje mai fuskantar gabas, ruwan kuwa yana malalowa daga wajen kudu.
Then he took me out through the north gate and led me around the outside to the outer gate that faced east. I saw water was trickling out from the south side of the gate.
3 Yayinda mutumin ya yi wajen gabas da karan awo a hannunsa, sai ya auna kamu dubu ya kuma bi da ni ta ruwan da zurfinsa ya kama ni a idon ƙafa.
The man walked east holding a measuring line He measured a thousand cubits and led me through the water which came up to my ankles.
4 Ya auna wani kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa ya kai ni gwiwa. Ya sāke auna kamu dubu ya kuma bi da ni a ruwan da zurfinsa kama ni a gindi.
He measured another thousand cubits and led me through water which came up to my knees. He measured another thousand cubits and led me through water that came up to my waist.
5 Ya auna wani kamu dubu, amma a yanzu ruwan ya zama kogin da ban iya hayewa ba, domin ruwan ya taso ya kuma yi zurfin da ya isa a yi iyo a ciki, kogin da ba za a iya hayewa ba.
He measured another thousand cubits, but this was a river I couldn't cross. The water had risen so high you could swim in it. It was a river that couldn't be crossed on foot.
6 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ka ga wannan?” Sa’an nan ya komo da ni zuwa bakin kogin.
“Son of man, have you observed all this?” he asked. Then he took me back to the riverbank.
7 Sa’ad da na iso can, sai na ga itatuwa masu yawa a kowane gefen kogin.
When I got there, I saw a large number of trees on both sides of the river.
8 Sai ya ce mini, “Wannan ruwa yana malalowa zuwa yankin gabas ya kuma gangaro zuwa cikin Araba, inda zai shiga Teku. Sa’ad da ya shiga cikin Tekun sai ruwan a can ya zama mai daɗi.
He told me, “This water flows out into the land to the east and into the Arabah. When it arrives at the Dead Sea, it turns the saltwater fresh.
9 Tarin halittu masu rai za su rayu a duk inda ruwan ya malalo. Za a kasance da kifi masu yawa, domin wannan ruwa yana malalowa a can yana kuma mai da ruwan gishiri yă zama ruwa mai daɗi; saboda haka duk inda ruwan ya malalo, kome zai rayu.
There will be many animals and fish wherever the river flows. Because the river turns the saltwater fresh wherever it flows, everything will be able to live there.
10 Masunta za su tsaya a gaɓar; daga En Gedi zuwa En Eglayim, za a kasance da wuraren jefa abin kamun kifi. Za a sami kifayen iri-iri, kamar kifaye Bahar Rum.
Fishermen will stand on the shore of the Dead Sea. They will be able to spread their nets from En-gedi to En-eglaim and catch many kinds of fish. There will be plenty of fish just like the Mediterranean Sea.
11 Amma fadamun da tafkunan ba za su zama masu daɗi ba; za a bar su a gishirinsu.
However, the marshes and swampy areas won't become fresh; they will remain salty.
12 ’Ya’yan itatuwa na kowane iri za su yi girma a kowane gefen kogin. Ganyayensu ba su bushe ba, ba kuwa za su fasa yin’ya’ya ba. Kowane wata za su ba da’ya’ya domin ruwa daga wuri mai tsarki yana malalo musu.’Ya’yansu za su zama abinci, ganyayensu kuma za su zama magani.”
All types of fruit trees will grow on both sides of the river. Their leaves won't wither, and they won't fail to produce fruit. They will produce fruit every month, because the river flowing from the sanctuary comes to water them. Their fruit will be eaten as food and their leaves will be used for healing.”
13 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “Waɗannan su ne iyakokin da za ku raba ƙasar gādo cikin kabilan Isra’ila goma sha biyu, da rabo biyu don Yusuf.
This is what the Lord God says: “These are the boundaries you are to use when allocating ownership of the land to the twelve tribes of Israel (Joseph is to receive two allocations.)
14 Za ku raba ta daidai a cikinsu. Gama na ɗaga hannu na rantse zan ba da ita ga kakanninku, wannan ƙasa za tă zama gādonku.
You are to allocate the land to them equally. I held up my hand and made a solemn promise to give it to your forefathers, so this land will come to you to own and to pass on as an inheritance.
15 “Wannan ce za tă zama iyakar ƙasa. “A wajen arewa za tă fara daga Bahar Rum ta hanyar Hetlon ta wuce Lebo Hamat zuwa Zedad,
These shall be the country's boundaries: On the northern side it runs from the Mediterranean Sea along the Hethlon road and through Lebo-hamath to Zedad;
16 Berota da Sibrayim (wadda take a iyaka tsakanin Damaskus da Hamat), har zuwa Hazer-Hattikon, wadda take a iyakar Hauran.
then on to Berothah, and Sibraim on the border between Damascus and Hamath, and all the way to Hazer-hatticon, on the border of Hauran.
17 Iyakar za tă miƙe daga teku zuwa Hazar-Enon, ta iyakar Damaskus, da iyakar Hamat a arewa. Wannan ita ce iyakar a wajen arewa.
So the border is from the Mediterranean Sea to Hazar-enan, along the northern border with Damascus, with the border of Hamath to the north. This is the northern boundary.
18 A wajen gabas iyakar za tă kama tsakanin Hauran da Damaskus, ta bi ta Urdun tsakanin Gileyad da ƙasar Isra’ila, zuwa tekun gabas har zuwa Tamar. Wannan ita ce iyakar a wajen gabas.
The eastern boundary runs from Hauran and Damascus, down along the Jordan between Gilead and the land of Israel, to the Dead Sea and on to Tamar. This is the eastern boundary.
19 A wajen kudu za tă fara daga Tamar har zuwa ruwan Meriba Kadesh, sa’an nan ta bi Rafin Masar zuwa Bahar Rum. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
The southern boundary runs from Tamar to the waters of Meribath-kadesh, then along the Wadi of Egypt to the Mediterranean Sea. This is the southern boundary.
20 A wajen yamma, Bahar Rum ne zai zama iyakar zuwa wani wuri ɗaura da Lebo Hamat. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
The Mediterranean Sea is the western boundary all the way up to a location opposite Lebo-hamath. This is the western boundary.
21 “Za ku rarraba wannan ƙasa a tsakaninku bisa ga kabilan Isra’ila.
You are to allocate this land for you to own according to the tribes of Israel.
22 Za ku raba ta kamar gādo wa kanku da kuma wa baƙin da suka zauna a cikinku waɗanda suke da’ya’ya. Za ku ɗauka su kamar’yan ƙasa haifaffun Isra’ilawa; za su yi gādo tare da ku a cikin kabilan Isra’ila.
You are to allocate land to own and to pass on as an inheritance for yourselves, and for the foreigners who live among you who have children. You shall treat them in the same way as Israelites born in the country. They are to be given a land allocation to own among the Israelite tribes in the same way as you.
23 A duk kabilar da baƙon yake zama, a can za ku ba shi gādonsa,” in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Foreigners are to be allocated land to own among the tribe where they live, declares the Lord God.”