< Ezekiyel 46 >

1 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a rufe ƙofa ta fili na can cikin da take fuskantar gabas ranaku shida na aiki, amma a ranar Asabbaci da kuma a ranar ganin Sabuwar Wata a buɗe ta.
“‘Egemen RAB şöyle diyor: İç avlunun doğuya bakan kapısı altı çalışma günü kapalı, Şabat Günü ve Yeni Ay Günü ise açık kalacak.
2 Sarki zai shiga daga waje ta shirayin hanyar shiga yă tsaya a madogarar ƙofa. Firistoci za su miƙa hadayarsa ta ƙonawa da hadayunsa na salama. Zai yi sujada a madogarar ƙofar hanyar shiga sa’an nan ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da yamma.
Önder dışarıdan eyvana girip kapı sövesinin yanında duracak. Kâhinler onun yakmalık ve esenlik sunularını sunacaklar. Önder kapı eşiğinde tapındıktan sonra çıkıp gidecek. Kapı akşama dek açık kalacak.
3 A Asabbatai da kuma a Sabuwar Wata mutanen ƙasar za su yi sujada a gaban Ubangiji a mashigin wannan hanyar shiga.
Şabat günleri ve Yeni Ay törenlerinde ülke halkı bu kapının girişinde RAB'bin önünde tapınacak.
4 Hadaya ta ƙonawar da sarki ya kawo wa Ubangiji a ranar Asabbaci’yan raguna shida ne da rago guda, dukansu marasa lahani.
Önder Şabat Günü RAB'be sunacağı yakmalık sunu olarak kusursuz altı kuzu, bir koç sunacak.
5 Hadayar garin da aka bayar tare da ragon efa guda ne, hadayar garin da’yan ragunan yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
Koç için verilecek tahıl sunusu bir efa tahıl olacak, kuzular için verebileceği kadar tahıl sunusu sunabilir. Her efa tahıl için bir hin zeytinyağı verilecek.
6 A ranar Sabuwar Wata zai miƙa ɗan bijimi,’yan raguna guda shida da kuma rago guda, dukansu marasa lahani.
Yeni Ay Günü kusursuz bir boğa, altı kuzu ve bir koç sunacak.
7 Zai tanada a matsayin hadaya ta gari, efa guda tare da bijimi, efa guda tare da’yan raguna, da kuma’yan raguna yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
Boğa ve koç için tahıl sunusu olarak birer efa tahıl sağlayacak; kuzular için istediği kadar tahıl sağlayabilir. Her efa tahıl için bir hin zeytinyağı sağlayacak.
8 Sa’ad da sarki zai shiga, zai shiga ta shirayin hanyar shiga, zai kuma fita ta nan.
Önder içeri gireceği zaman eyvandan girecek ve aynı yoldan dışarı çıkacak.
9 “‘Sa’ad da mutanen ƙasar suka zo gaban Ubangiji a ƙayyadaddun bukukkuwa, duk wanda ya shiga ta ƙofar arewa don yă yi sujada sai ya fita ta ƙofar kudu; kuma duk wanda ya shiga ta ƙofar kudu sai ya fita ta ƙofar arewa. Ba wanda zai koma ta ƙofar da ya shiga, amma kowa zai fita a ƙofar ɗaura da wadda ya shiga.
“‘Ülke halkı bayramlarda RAB'bin önüne geldiğinde, tapınmak için Kuzey Kapısı'ndan giren Güney Kapısı'ndan çıkacak, Güney Kapısı'ndan giren Kuzey Kapısı'ndan çıkacak. Hiç kimse girdiği kapıdan çıkmayacak. Herkes girdiği kapının karşısındaki kapıdan çıkacak.
10 Sarki zai kasance a cikinsu, zai shiga sa’ad da suke shiga ya kuma fita sa’ad da suka fita.
Önder halkın arasında olacak. Halkla birlikte girecek, halkla birlikte çıkacak.
11 “‘A bukukkuwa da ƙayyadaddun bukukkuwa, hadaya ta gari zai zama efa tare da bijimi, efa da rago, da kuma’yan raguna da ya ga dama, haɗe da kwalabar mai.
“‘Bayramlarda ve kutsal günlerde boğa ve koç için tahıl sunusu olarak birer efa tahıl verecek; kuzular için verebileceği kadar tahıl sağlayabilir. Her efa tahıl için bir hin zeytinyağı verecek.
12 Sa’ad da sarki ya ba da hadaya ta yardar rai ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa ce ko hadayun salama ne, sai a buɗe masa ƙofar da take fuskantar gabas. Zai miƙa hadayarsa ta ƙonawa ko hadayarsa ta salama yadda yakan yi a ranar Asabbaci. Sa’an nan ya fita, bayan kuma ya fita, sai a rufe ƙofar.
Önder RAB'be gönülden verilen yakmalık sunular ya da esenlik sunuları sunacağı zaman doğuya bakan kapı kendisine açılacak. Yakmalık sunuları ya da esenlik sunularını Şabat Günü sunduğu gibi sunacak. Sonra dışarı çıkacak; o çıktıktan sonra kapı kapanacak.
13 “‘Kullum za ku tanada ɗan rago bana ɗaya marar lahani don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji; kowace safiya za ku tanada shi.
“‘Her gün, her sabah yakmalık sunu olarak RAB'be bir yaşında kusursuz bir kuzu sağlayacaksın.
14 Tare da shi za ku tanada hadaya ta gari kowace safiya, da ya haɗa da kashi ɗaya bisa shida na efa tare da kashi ɗaya bisa uku na mai ga garin da aka cuɗa. Miƙawar wannan hadaya ta gari ga Ubangiji dawwammamiyar farilla ce.
Bununla birlikte her sabah tahıl sunusu olarak efanın altıda biri tahıl ve ince unu ıslatmak için bir hinin üçte biri kadar zeytinyağı sağlayacaksın. Bu tahıl sunusunun RAB'be sunulması sürekli bir kural olacak.
15 Saboda haka za a tanada ɗan rago da hadaya ta gari da kuma mai kowace safiya don hadaya ta ƙonawa ta kullum.
Böylece günlük yakmalık sunu olarak her sabah kuzu, tahıl sunusu ve zeytinyağı sunulacak.’”
16 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa in sarkin ya ba wa ɗaya daga cikin’ya’yansa kyauta daga gādonsa, zai kuwa zama na zuriyar; zai kuwa zama mallakarsu ta wurin gādo.
“‘Egemen RAB şöyle diyor: Eğer önder oğullarından birine kendi mülkünden armağan ederse, bu mülk torunlarına da geçecek. Miras yoluyla bu onların mülkü olacak.
17 In kuma ya ba wa ɗaya daga cikin bayinsa kyauta daga gadonsa, bawan zai iya riƙe shi sai shekarar’yantarwa; sa’an nan ya mayar wa sarkin. Gādon sarki na’ya’yansa maza ne kaɗai; na su ne.
Önder görevlilerinden birine kendi mülkünden armağan ederse, görevli toprak parçasını özgürlük yılına dek elinde tutacak. Sonra öndere geri verecek. Önderin mirası ancak oğullarına geçebilir, onların olacak.
18 Kada sarki ya ƙwace gādon mutane, yana korinsu daga mallakarsu. Zai ba wa’ya’yansa maza gādonsu daga cikin mallakarsa, don kada a raba wani daga mutanena da mallakarsa.’”
Önder halkı mülkünden kovarak miraslarından etmemeli. Oğullarına ancak kendi mülkünden miras verebilir. Öyle ki, halkımdan hiç kimse mülkünden ayrılıp dağılmasın.’”
19 Sa’an nan mutumin ya fitar da ni ta ƙofar shiga a gefen ƙofar zuwa tsarkakakkun ɗakuna waɗanda suke fuskantar arewa, waɗanda suke na firistoci, ya kuma nuna mini wani wuri daga can ƙurewar yamma.
Bundan sonra adam beni kapı yanındaki girişten kuzeye bakan, kâhinlere ait kutsal odalara getirdi. Bana batıda bir yer gösterdi.
20 Ya ce mini, “Wannan shi ne wurin da firistoci za su dafa hadaya don laifi, da hadaya don zunubi, a nan ne kuma za su toya hadaya ta gari, domin kada su kai su a filin da yake waje, su tsarkake mutane.”
“Kâhinlerin suç sunusuyla günah sunusunun etini haşlayacakları, tahıl sunusunu pişirecekleri yer burası” dedi, “Öyle ki, bunları dış avluya çıkarıp kutsallıklarını halka geçirmesinler.”
21 Sa’an nan ya kawo ni filin da yake waje ya kuma bi da ni kewaye da kusurwoyi huɗunsa, na kuma ga kowace kusurwa na wani fili.
Daha sonra adam beni dış avluya çıkarıp sırayla avlunun dört köşesine götürdü. Avlunun her köşesinde küçük birer avlu olduğunu gördüm.
22 A kusurwoyi huɗu na filin da yake waje akwai waɗansu filaye a haɗe, tsawonsu kamu arba’in fāɗinsu kuwa kamu talatin; kowane fili a kusurwoyi huɗun nan girmansu ɗaya ne.
Dış avlunun dört köşesinde kırk arşın uzunluğunda, otuz arşın genişliğinde birer kapalı avlu vardı. Köşelerdeki avluların ölçüsü aynıydı.
23 Kewaye da cikin kowane filin huɗun nan akwai ginin dutse, da murhu da aka gina a kewaye a ƙarƙashin ginin.
Dört avlunun çevresinde de taş duvar vardı; duvarın dibinde yemek pişirmek için yerler yapılmıştı.
24 Sai ya ce mini, “Waɗannan su ne ɗakunan dahuwa inda masu hidima a haikali za su dafa hadayun da jama’a.”
Bana, “Bunlar tapınakta hizmet edenlerin halkın sunduğu kurban etini pişirecekleri mutfaklar” dedi.

< Ezekiyel 46 >