< Ezekiyel 46 >

1 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a rufe ƙofa ta fili na can cikin da take fuskantar gabas ranaku shida na aiki, amma a ranar Asabbaci da kuma a ranar ganin Sabuwar Wata a buɗe ta.
Ovako veli Gospod Gospod: vrata unutrašnjega trijema, koja gledaju na istok, neka su zatvorena u šest dana težatnijeh, a u subotu neka se otvoraju, i na dan mladine neka se otvoraju.
2 Sarki zai shiga daga waje ta shirayin hanyar shiga yă tsaya a madogarar ƙofa. Firistoci za su miƙa hadayarsa ta ƙonawa da hadayunsa na salama. Zai yi sujada a madogarar ƙofar hanyar shiga sa’an nan ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da yamma.
I knez neka doðe kroz trijem od vrata spoljašnjih, i neka stane kod dovratnika, a sveštenici neka prinesu njegovu žrtvu paljenicu i žrtvu zahvalnu, i on pokloniv se na pragu neka otide, a vrata da se ne zatvoraju do veèera.
3 A Asabbatai da kuma a Sabuwar Wata mutanen ƙasar za su yi sujada a gaban Ubangiji a mashigin wannan hanyar shiga.
I narod zemaljski neka se poklanja Gospodu na istijem vratima u subote i na mladine.
4 Hadaya ta ƙonawar da sarki ya kawo wa Ubangiji a ranar Asabbaci’yan raguna shida ne da rago guda, dukansu marasa lahani.
A žrtva paljenica, što æe prinositi knez Gospodu subotom, biæe šest jaganjaca zdravijeh i ovan zdrav;
5 Hadayar garin da aka bayar tare da ragon efa guda ne, hadayar garin da’yan ragunan yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
A dar efa na ovna, a na jaganjce dar koliko mu ruka može, i in ulja na efu;
6 A ranar Sabuwar Wata zai miƙa ɗan bijimi,’yan raguna guda shida da kuma rago guda, dukansu marasa lahani.
A o mladini da bude junac zdrav, i šest jaganjaca i ovan, sve zdravo;
7 Zai tanada a matsayin hadaya ta gari, efa guda tare da bijimi, efa guda tare da’yan raguna, da kuma’yan raguna yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
I dar da prinese efu na junca i efu na ovna, a na jaganjce koliko mu može ruka, i ulja in na efu.
8 Sa’ad da sarki zai shiga, zai shiga ta shirayin hanyar shiga, zai kuma fita ta nan.
A knez kad ide, neka ide kroz trijem od vrata, i istijem putem neka odlazi.
9 “‘Sa’ad da mutanen ƙasar suka zo gaban Ubangiji a ƙayyadaddun bukukkuwa, duk wanda ya shiga ta ƙofar arewa don yă yi sujada sai ya fita ta ƙofar kudu; kuma duk wanda ya shiga ta ƙofar kudu sai ya fita ta ƙofar arewa. Ba wanda zai koma ta ƙofar da ya shiga, amma kowa zai fita a ƙofar ɗaura da wadda ya shiga.
A kad narod zemaljski dohodi pred Gospoda o praznicima, ko uðe na sjeverna vrata da se pokloni, neka izlazi na južna vrata; a ko uðe na južna vrata, neka izlazi na sjeverna vrata; neka se ne vraæa na vrata na koja uðe, nego neka izlazi na ona koja su nasuprot.
10 Sarki zai kasance a cikinsu, zai shiga sa’ad da suke shiga ya kuma fita sa’ad da suka fita.
A knez s njima neka ulazi kad oni ulaze, i neka izlazi kad oni izlaze.
11 “‘A bukukkuwa da ƙayyadaddun bukukkuwa, hadaya ta gari zai zama efa tare da bijimi, efa da rago, da kuma’yan raguna da ya ga dama, haɗe da kwalabar mai.
I o praznicima i o svetkovinama dar neka je efa na junca, i efa na ovna, a na jaganjce koliko mu ruka dade, a ulja in na efu.
12 Sa’ad da sarki ya ba da hadaya ta yardar rai ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa ce ko hadayun salama ne, sai a buɗe masa ƙofar da take fuskantar gabas. Zai miƙa hadayarsa ta ƙonawa ko hadayarsa ta salama yadda yakan yi a ranar Asabbaci. Sa’an nan ya fita, bayan kuma ya fita, sai a rufe ƙofar.
A kad knez prinosi dragovoljnu žrtvu, paljenicu ili zahvalnu, od svoje volje Gospodu, tada neka mu se otvore vrata koja gledaju na istok, i neka prinese žrtvu svoju paljenicu i zahvalnu, kako èini subotom; potom neka izide, i vrata neka se zatvore kad izide.
13 “‘Kullum za ku tanada ɗan rago bana ɗaya marar lahani don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji; kowace safiya za ku tanada shi.
I prinosi svaki dan Gospodu na žrtvu paljenicu jagnje od godine zdravo; svako jutro prinosi ga.
14 Tare da shi za ku tanada hadaya ta gari kowace safiya, da ya haɗa da kashi ɗaya bisa shida na efa tare da kashi ɗaya bisa uku na mai ga garin da aka cuɗa. Miƙawar wannan hadaya ta gari ga Ubangiji dawwammamiyar farilla ce.
I dodaj na nj dar svako jutro šestinu efe i ulja treæinu ina, da se pokropi bijelo brašno; to je vazdašnji dar Gospodu uredbom vjeènom.
15 Saboda haka za a tanada ɗan rago da hadaya ta gari da kuma mai kowace safiya don hadaya ta ƙonawa ta kullum.
I tako neka prinose jagnje i dar i ulje svako jutro, žrtvu paljenicu svagdašnju.
16 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa in sarkin ya ba wa ɗaya daga cikin’ya’yansa kyauta daga gādonsa, zai kuwa zama na zuriyar; zai kuwa zama mallakarsu ta wurin gādo.
Ovako veli Gospod Gospod: ako knez da dar kome sinu svom od svojega našljedstva, neka bude sinovima njegovijem, njihovo je dostojanje.
17 In kuma ya ba wa ɗaya daga cikin bayinsa kyauta daga gadonsa, bawan zai iya riƙe shi sai shekarar’yantarwa; sa’an nan ya mayar wa sarkin. Gādon sarki na’ya’yansa maza ne kaɗai; na su ne.
Ako li da dar od svojega našljedstva kome sluzi svojemu, neka mu bude do godine oprosne, a onda neka se vrati knezu, jer je njegovo našljedstvo, sinovima njegovijem neka bude.
18 Kada sarki ya ƙwace gādon mutane, yana korinsu daga mallakarsu. Zai ba wa’ya’yansa maza gādonsu daga cikin mallakarsa, don kada a raba wani daga mutanena da mallakarsa.’”
I knez da ne uzima narodu ništa od našljedstva tjerajuæi ih s njihova našljedstva; od svojega dostojanja neka daje sinovima svojim našljedstvo da se ne razgoni moj narod, niko sa svojega našljedstva.
19 Sa’an nan mutumin ya fitar da ni ta ƙofar shiga a gefen ƙofar zuwa tsarkakakkun ɗakuna waɗanda suke fuskantar arewa, waɗanda suke na firistoci, ya kuma nuna mini wani wuri daga can ƙurewar yamma.
Potom me odvede kroz ulaz koji je pokraj vrata u svete klijeti sveštenièke koje gledaju na sjever, i gle, ondje bijaše neko mjesto u dnu prema zapadu.
20 Ya ce mini, “Wannan shi ne wurin da firistoci za su dafa hadaya don laifi, da hadaya don zunubi, a nan ne kuma za su toya hadaya ta gari, domin kada su kai su a filin da yake waje, su tsarkake mutane.”
I reèe mi: ovo je mjesto gdje æe sveštenici variti prinos za krivicu i za grijeh, gdje æe peæi dar da ne iznose u spoljašnji trijem i narod posveæuju.
21 Sa’an nan ya kawo ni filin da yake waje ya kuma bi da ni kewaye da kusurwoyi huɗunsa, na kuma ga kowace kusurwa na wani fili.
Tada me izvede u spoljašnji trijem, i provede me u èetiri ugla od trijema, i gle, u svakom uglu od trijema bijaše trijem.
22 A kusurwoyi huɗu na filin da yake waje akwai waɗansu filaye a haɗe, tsawonsu kamu arba’in fāɗinsu kuwa kamu talatin; kowane fili a kusurwoyi huɗun nan girmansu ɗaya ne.
U èetiri ugla od trijema bijahu trijemovi s dimnjacima, u dužinu od èetrdeset lakata, a u širinu od trideset lakata, sva èetiri na uglovima bijahu jedne mjere.
23 Kewaye da cikin kowane filin huɗun nan akwai ginin dutse, da murhu da aka gina a kewaye a ƙarƙashin ginin.
U njima èetirma bješe zid unaokolo, a pod tijem zidom bijahu ognjišta svuda unaokolo.
24 Sai ya ce mini, “Waɗannan su ne ɗakunan dahuwa inda masu hidima a haikali za su dafa hadayun da jama’a.”
I reèe mi: ovo su kuhinje, gdje æe žrtve narodne kuhati koji služe domu.

< Ezekiyel 46 >