< Ezekiyel 46 >
1 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a rufe ƙofa ta fili na can cikin da take fuskantar gabas ranaku shida na aiki, amma a ranar Asabbaci da kuma a ranar ganin Sabuwar Wata a buɗe ta.
Assim diz o Senhor Jehovah: A porta do átrio interior, que olha para o oriente, estará fechada os seis dias que são de trabalho; porém no dia de sábado ela se abrirá; também no dia da lua nova se abrirá.
2 Sarki zai shiga daga waje ta shirayin hanyar shiga yă tsaya a madogarar ƙofa. Firistoci za su miƙa hadayarsa ta ƙonawa da hadayunsa na salama. Zai yi sujada a madogarar ƙofar hanyar shiga sa’an nan ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da yamma.
E o príncipe entrará pelo caminho do vestíbulo da porta, por fora, e estará em pé na hombreira da porta; e os sacerdotes prepararão o seu holocausto, e os seus sacrifícios pacíficos, e ele se prostrará no umbral da porta, e sairá; porém a porta não se fechará até à tarde.
3 A Asabbatai da kuma a Sabuwar Wata mutanen ƙasar za su yi sujada a gaban Ubangiji a mashigin wannan hanyar shiga.
E o povo da terra se prostrará à entrada da mesma porta, nos sábados e nas luas novas, diante do Senhor.
4 Hadaya ta ƙonawar da sarki ya kawo wa Ubangiji a ranar Asabbaci’yan raguna shida ne da rago guda, dukansu marasa lahani.
E o holocausto, que o príncipe oferecerá ao Senhor, será, no dia de sábado, seis cordeiros sem mancha e um carneiro sem mancha.
5 Hadayar garin da aka bayar tare da ragon efa guda ne, hadayar garin da’yan ragunan yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
E a oferta de manjares será um epha para cada carneiro; e para cada cordeiro, a oferta de manjares será um dom da sua mão; e de azeite um hin para cada epha.
6 A ranar Sabuwar Wata zai miƙa ɗan bijimi,’yan raguna guda shida da kuma rago guda, dukansu marasa lahani.
Mas no dia da lua nova será um bezerro, sem mancha; e seis cordeiros e um carneiro, eles serão sem mancha.
7 Zai tanada a matsayin hadaya ta gari, efa guda tare da bijimi, efa guda tare da’yan raguna, da kuma’yan raguna yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
E preparará por oferta de manjares um epha para o bezerro e um epha para o carneiro, mas para os cordeiros, conforme o que alcançar a sua mão; e um hin de azeite para um epha.
8 Sa’ad da sarki zai shiga, zai shiga ta shirayin hanyar shiga, zai kuma fita ta nan.
E, quando entrar o príncipe, entrará pelo caminho do vestíbulo da porta, e sairá pelo mesmo caminho.
9 “‘Sa’ad da mutanen ƙasar suka zo gaban Ubangiji a ƙayyadaddun bukukkuwa, duk wanda ya shiga ta ƙofar arewa don yă yi sujada sai ya fita ta ƙofar kudu; kuma duk wanda ya shiga ta ƙofar kudu sai ya fita ta ƙofar arewa. Ba wanda zai koma ta ƙofar da ya shiga, amma kowa zai fita a ƙofar ɗaura da wadda ya shiga.
Mas, quando vier o povo da terra perante a face do Senhor nas solenidades, aquele que entrar pelo caminho da porta do norte, para adorar, sairá pelo caminho da porta do sul; e aquele que entrar pelo caminho da porta do sul sairá pelo caminho da porta do norte: não tornará pelo caminho da porta por onde entrou, mas sairá pela outra que está oposta.
10 Sarki zai kasance a cikinsu, zai shiga sa’ad da suke shiga ya kuma fita sa’ad da suka fita.
E o príncipe no meio deles entrará, quando eles entrarem, e, saindo eles, sairão todos.
11 “‘A bukukkuwa da ƙayyadaddun bukukkuwa, hadaya ta gari zai zama efa tare da bijimi, efa da rago, da kuma’yan raguna da ya ga dama, haɗe da kwalabar mai.
E nas festas e nas solenidades será a oferta de manjares um epha para o bezerro, e um epha para o carneiro, mas para os cordeiros um dom da sua mão; e de azeite um hin para um epha.
12 Sa’ad da sarki ya ba da hadaya ta yardar rai ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa ce ko hadayun salama ne, sai a buɗe masa ƙofar da take fuskantar gabas. Zai miƙa hadayarsa ta ƙonawa ko hadayarsa ta salama yadda yakan yi a ranar Asabbaci. Sa’an nan ya fita, bayan kuma ya fita, sai a rufe ƙofar.
E, quando o príncipe fizer oferta voluntária de holocaustos, ou de sacrifícios pacíficos, por oferta voluntária ao Senhor, então lhe abrirão a porta que olha para o oriente, e fará o seu holocausto e os seus sacrifícios pacíficos, como houver feito no dia de sábado; e sairá, e se fechará a porta depois dele sair
13 “‘Kullum za ku tanada ɗan rago bana ɗaya marar lahani don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji; kowace safiya za ku tanada shi.
E prepararás um cordeiro dum ano sem mancha, em holocausto ao Senhor, cada dia: todas as manhãs o prepararás.
14 Tare da shi za ku tanada hadaya ta gari kowace safiya, da ya haɗa da kashi ɗaya bisa shida na efa tare da kashi ɗaya bisa uku na mai ga garin da aka cuɗa. Miƙawar wannan hadaya ta gari ga Ubangiji dawwammamiyar farilla ce.
E, por oferta de manjares farás juntamente com ele, todas as manhãs, a sexta parte dum epha, e de azeite a terça parte dum hin, para sovar a flor de farinha; por oferta de manjares para o Senhor, em estatutos perpétuos e contínuos.
15 Saboda haka za a tanada ɗan rago da hadaya ta gari da kuma mai kowace safiya don hadaya ta ƙonawa ta kullum.
Assim prepararão o cordeiro, e a oferta de manjares, e o azeite, todas as manhãs, em holocausto contínuo.
16 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa in sarkin ya ba wa ɗaya daga cikin’ya’yansa kyauta daga gādonsa, zai kuwa zama na zuriyar; zai kuwa zama mallakarsu ta wurin gādo.
Assim diz o Senhor Jehovah: Quando o príncipe der um presente da sua herança a algum de seus filhos, isto será para seus filhos: será possessão deles por herança.
17 In kuma ya ba wa ɗaya daga cikin bayinsa kyauta daga gadonsa, bawan zai iya riƙe shi sai shekarar’yantarwa; sa’an nan ya mayar wa sarkin. Gādon sarki na’ya’yansa maza ne kaɗai; na su ne.
Porém, dando ele um presente da sua herança a algum dos seus servos, será deste até ao ano da liberdade; então tornará para o príncipe, porque herança dele é; seus filhos, eles a herdarão.
18 Kada sarki ya ƙwace gādon mutane, yana korinsu daga mallakarsu. Zai ba wa’ya’yansa maza gādonsu daga cikin mallakarsa, don kada a raba wani daga mutanena da mallakarsa.’”
E o príncipe não tomará nada da herança do povo, para os defraudar da sua possessão: da sua possessão deixará herança a seus filhos, para que o meu povo não seja espalhado, cada um da sua possessão.
19 Sa’an nan mutumin ya fitar da ni ta ƙofar shiga a gefen ƙofar zuwa tsarkakakkun ɗakuna waɗanda suke fuskantar arewa, waɗanda suke na firistoci, ya kuma nuna mini wani wuri daga can ƙurewar yamma.
Depois disto me trouxe pela entrada que estava ao lado da porta, às câmaras santas dos sacerdotes, que olhavam para o norte; e eis que ali estava um lugar em ambos os lados, para a banda do ocidente.
20 Ya ce mini, “Wannan shi ne wurin da firistoci za su dafa hadaya don laifi, da hadaya don zunubi, a nan ne kuma za su toya hadaya ta gari, domin kada su kai su a filin da yake waje, su tsarkake mutane.”
E ele me disse: Este é o lugar onde os sacerdotes cozerão o sacrifício pela culpa, e o sacrifício pelo pecado, e onde cozerão a oferta de manjares, para que a não tragam ao átrio exterior para santificarem o povo.
21 Sa’an nan ya kawo ni filin da yake waje ya kuma bi da ni kewaye da kusurwoyi huɗunsa, na kuma ga kowace kusurwa na wani fili.
Então me levou para fora, para o átrio exterior, e me fez passar às quatro esquinas do átrio: e eis que em cada esquina do átrio havia outro átrio.
22 A kusurwoyi huɗu na filin da yake waje akwai waɗansu filaye a haɗe, tsawonsu kamu arba’in fāɗinsu kuwa kamu talatin; kowane fili a kusurwoyi huɗun nan girmansu ɗaya ne.
Nas quatro esquinas do átrio havia outros átrios com chaminés de quarenta côvados de comprimento e de trinta de largura: estas quatro esquinas tinham uma mesma medida.
23 Kewaye da cikin kowane filin huɗun nan akwai ginin dutse, da murhu da aka gina a kewaye a ƙarƙashin ginin.
E um muro havia ao redor delas, ao redor das quatro: e havia cozinhas feitas por baixo dos muros ao redor.
24 Sai ya ce mini, “Waɗannan su ne ɗakunan dahuwa inda masu hidima a haikali za su dafa hadayun da jama’a.”
E me disse: Estas são as casas dos cozinheiros, onde os ministros da casa cozerão o sacrifício do povo.