< Ezekiyel 46 >

1 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a rufe ƙofa ta fili na can cikin da take fuskantar gabas ranaku shida na aiki, amma a ranar Asabbaci da kuma a ranar ganin Sabuwar Wata a buɗe ta.
“‘This is [also] what [I], Yahweh the Lord, declare: The east entryway of the inner courtyard must be shut during the six days in which people work each week, but on the Sabbath days and on the days when there is a new moon, that entryway must [remain] open until that evening.
2 Sarki zai shiga daga waje ta shirayin hanyar shiga yă tsaya a madogarar ƙofa. Firistoci za su miƙa hadayarsa ta ƙonawa da hadayunsa na salama. Zai yi sujada a madogarar ƙofar hanyar shiga sa’an nan ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da yamma.
The king must enter the courtyard through the entry room of the entryway, and stand alongside the entry post. [Then] the priests must sacrifice the animal that the king brought to be completely [on the altar], and also his offering to maintain fellowship with me. The king must worship me at the entrance of the entryway, and then he must go out. [After he leaves], the entryway will not be shut until that evening.
3 A Asabbatai da kuma a Sabuwar Wata mutanen ƙasar za su yi sujada a gaban Ubangiji a mashigin wannan hanyar shiga.
On the Sabbath days and on the [days when there is a] new moon, the people must worship [me] at the entrance of the entryway.
4 Hadaya ta ƙonawar da sarki ya kawo wa Ubangiji a ranar Asabbaci’yan raguna shida ne da rago guda, dukansu marasa lahani.
The offering that the king brings to be completely burned on the Sabbath day must be six lambs and one ram, all with no defects.
5 Hadayar garin da aka bayar tare da ragon efa guda ne, hadayar garin da’yan ragunan yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
The offering [that he gives] with the ram must be a bushel of grain, and the grain [that he offers] with the lambs should be as much as he desires to offer, along with (1 gallon/3.8 liters) of [olive] oil for each bushel [of grain].
6 A ranar Sabuwar Wata zai miƙa ɗan bijimi,’yan raguna guda shida da kuma rago guda, dukansu marasa lahani.
[Then] each day that there is a new moon, he must offer a young bull, six lambs and a ram, all with no defects.
7 Zai tanada a matsayin hadaya ta gari, efa guda tare da bijimi, efa guda tare da’yan raguna, da kuma’yan raguna yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
He must [also] provide one bushel of grain with the bull, one bushel of grain with the ram, and as much grain as he wants with the lambs, along with one quart/liter of [olive] oil with each bushel [of grain].
8 Sa’ad da sarki zai shiga, zai shiga ta shirayin hanyar shiga, zai kuma fita ta nan.
When the king enters [the temple area], he must enter through the entry room of the entryway, and he must go out through that same entry room [when he leaves].
9 “‘Sa’ad da mutanen ƙasar suka zo gaban Ubangiji a ƙayyadaddun bukukkuwa, duk wanda ya shiga ta ƙofar arewa don yă yi sujada sai ya fita ta ƙofar kudu; kuma duk wanda ya shiga ta ƙofar kudu sai ya fita ta ƙofar arewa. Ba wanda zai koma ta ƙofar da ya shiga, amma kowa zai fita a ƙofar ɗaura da wadda ya shiga.
When the Israeli people come to worship me at the festivals that I have appointed, those who enter the temple area through the north entryway must go out through the south entryway. And those who enter through the south entryway must go out through the north entryway. People must not go out through the entryway through which they entered; they must go out through the opposite entryway.
10 Sarki zai kasance a cikinsu, zai shiga sa’ad da suke shiga ya kuma fita sa’ad da suka fita.
The king must go in when the other people go in, and go out when the people go out.
11 “‘A bukukkuwa da ƙayyadaddun bukukkuwa, hadaya ta gari zai zama efa tare da bijimi, efa da rago, da kuma’yan raguna da ya ga dama, haɗe da kwalabar mai.
During the festivals and sacred feasts, the king must present a bushel of grain along with each bull or ram, and as much grain as he wants to bring, along with the lambs and (1 gallon/3.8 liters) of olive oil with each bushel of grain.
12 Sa’ad da sarki ya ba da hadaya ta yardar rai ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa ce ko hadayun salama ne, sai a buɗe masa ƙofar da take fuskantar gabas. Zai miƙa hadayarsa ta ƙonawa ko hadayarsa ta salama yadda yakan yi a ranar Asabbaci. Sa’an nan ya fita, bayan kuma ya fita, sai a rufe ƙofar.
When the king gives an offering that is not required, either one to be completely burned [on the altar] or an offering to maintain fellowship with [me, Yahweh, the entryway on the east side of the courtyard] must be opened for him. Then he must present those offerings like he does on the Sabbath days. Then he must go out, and after he goes out, the entryway must be shut.
13 “‘Kullum za ku tanada ɗan rago bana ɗaya marar lahani don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji; kowace safiya za ku tanada shi.
Every day, during the morning, someone must provide a one-year-old lamb with no defects to be an offering to me that will be completely burned.
14 Tare da shi za ku tanada hadaya ta gari kowace safiya, da ya haɗa da kashi ɗaya bisa shida na efa tare da kashi ɗaya bisa uku na mai ga garin da aka cuɗa. Miƙawar wannan hadaya ta gari ga Ubangiji dawwammamiyar farilla ce.
Someone must also provide each morning an offering of flour. It must be one sixth of a bushel of flour mixed with one quart/liter of [olive] oil. These offerings of flour and olive oil to must be presented [to me], Yahweh, each day.
15 Saboda haka za a tanada ɗan rago da hadaya ta gari da kuma mai kowace safiya don hadaya ta ƙonawa ta kullum.
The lamb and the offering of flour and [olive] oil must be presented to me every morning, to be completely burned on the altar.
16 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa in sarkin ya ba wa ɗaya daga cikin’ya’yansa kyauta daga gādonsa, zai kuwa zama na zuriyar; zai kuwa zama mallakarsu ta wurin gādo.
This is what I, Yahweh the Lord, declare: If the king gives some of his land to one of his sons, to belong to him permanently, it will then belong to his son’s descendants forever.
17 In kuma ya ba wa ɗaya daga cikin bayinsa kyauta daga gadonsa, bawan zai iya riƙe shi sai shekarar’yantarwa; sa’an nan ya mayar wa sarkin. Gādon sarki na’ya’yansa maza ne kaɗai; na su ne.
However, if he gives some of his land to one of his servants, the servant is allowed to keep that land until the Year of Celebration. Then the king will own it again; the king’s land must belong to his descendants forever.
18 Kada sarki ya ƙwace gādon mutane, yana korinsu daga mallakarsu. Zai ba wa’ya’yansa maza gādonsu daga cikin mallakarsa, don kada a raba wani daga mutanena da mallakarsa.’”
The king must not take any land that the people own and force them to live somewhere else. The land that he gives to his sons must be from his own property, [not from anyone else’s property], in order that none of my people will be forced to leave his own property.’”
19 Sa’an nan mutumin ya fitar da ni ta ƙofar shiga a gefen ƙofar zuwa tsarkakakkun ɗakuna waɗanda suke fuskantar arewa, waɗanda suke na firistoci, ya kuma nuna mini wani wuri daga can ƙurewar yamma.
Then, [in the vision], the man [who was showing the temple area to me] brought me through the entrance alongside the entryway and led me to the sacred rooms on the north side, the rooms that the priests used, and he showed me a place at the western end [of those rooms].
20 Ya ce mini, “Wannan shi ne wurin da firistoci za su dafa hadaya don laifi, da hadaya don zunubi, a nan ne kuma za su toya hadaya ta gari, domin kada su kai su a filin da yake waje, su tsarkake mutane.”
He said to me, “This is the place where the priests must cook the meat of the offerings that people bring in order to no longer be guilty for having sinned, and offerings for their sins, and where they will bake bread made with the flour brought to be offerings. [They will cook those things in their rooms] in order to avoid bringing them into the outer courtyard [to cook them there], lest someone [be punished because of] touching them.”
21 Sa’an nan ya kawo ni filin da yake waje ya kuma bi da ni kewaye da kusurwoyi huɗunsa, na kuma ga kowace kusurwa na wani fili.
Then the man brought me to the outer courtyard and led me to its four corners. In each corner I saw an enclosed area;
22 A kusurwoyi huɗu na filin da yake waje akwai waɗansu filaye a haɗe, tsawonsu kamu arba’in fāɗinsu kuwa kamu talatin; kowane fili a kusurwoyi huɗun nan girmansu ɗaya ne.
each of those areas was (70 feet/21.2 meters) long and (52-1/2 feet/15.9 meters) wide.
23 Kewaye da cikin kowane filin huɗun nan akwai ginin dutse, da murhu da aka gina a kewaye a ƙarƙashin ginin.
Around the inside of each of those enclosed areas was a stone ledge, with places to make fires all around under each ledge.
24 Sai ya ce mini, “Waɗannan su ne ɗakunan dahuwa inda masu hidima a haikali za su dafa hadayun da jama’a.”
The man said to me, “These are the kitchens where [the descendants of Levi] who work in the temple must cook the sacrifices that the people bring.”

< Ezekiyel 46 >