< Ezekiyel 46 >

1 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a rufe ƙofa ta fili na can cikin da take fuskantar gabas ranaku shida na aiki, amma a ranar Asabbaci da kuma a ranar ganin Sabuwar Wata a buɗe ta.
Thus saith the Lord Jehovah: The gate of the inner court, that looketh toward the east, shall be shut the six working-days; but on the sabbath it shall be opened, and on the day of the new moon it shall be opened.
2 Sarki zai shiga daga waje ta shirayin hanyar shiga yă tsaya a madogarar ƙofa. Firistoci za su miƙa hadayarsa ta ƙonawa da hadayunsa na salama. Zai yi sujada a madogarar ƙofar hanyar shiga sa’an nan ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da yamma.
And the prince shall enter by the way of the porch of the outer gate, and shall stand by the post of the gate, and the priests shall present his burnt-offerings, and his peace-offerings, and he shall worship at the threshold of the gate; then he shall go forth; but the gate shall not be shut until the evening.
3 A Asabbatai da kuma a Sabuwar Wata mutanen ƙasar za su yi sujada a gaban Ubangiji a mashigin wannan hanyar shiga.
Likewise the people of the land shall worship at the door of this gate before Jehovah on the sabbaths and on the new moons.
4 Hadaya ta ƙonawar da sarki ya kawo wa Ubangiji a ranar Asabbaci’yan raguna shida ne da rago guda, dukansu marasa lahani.
And the burnt-offering, which the prince shall offer to Jehovah on the sabbath-day, shall be six lambs without blemish, and a ram without blemish.
5 Hadayar garin da aka bayar tare da ragon efa guda ne, hadayar garin da’yan ragunan yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
And the flour-offering shall be an ephah for a ram; and the flour-offering for the lambs as much as he is disposed to give; and a hin of oil to an ephah.
6 A ranar Sabuwar Wata zai miƙa ɗan bijimi,’yan raguna guda shida da kuma rago guda, dukansu marasa lahani.
And in the day of the new moon there shall be a young bullock without blemish, and six lambs and a ram; they shall be without blemish.
7 Zai tanada a matsayin hadaya ta gari, efa guda tare da bijimi, efa guda tare da’yan raguna, da kuma’yan raguna yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
And he shall present, as a flour-offering, an ephah for a bullock, and an ephah for a ram, and for the lambs as much as he is able to give; and a hin of oil to an ephah.
8 Sa’ad da sarki zai shiga, zai shiga ta shirayin hanyar shiga, zai kuma fita ta nan.
And when the prince shall enter, he shall go in by the way of the porch of that gate, and he shall go forth by the way thereof.
9 “‘Sa’ad da mutanen ƙasar suka zo gaban Ubangiji a ƙayyadaddun bukukkuwa, duk wanda ya shiga ta ƙofar arewa don yă yi sujada sai ya fita ta ƙofar kudu; kuma duk wanda ya shiga ta ƙofar kudu sai ya fita ta ƙofar arewa. Ba wanda zai koma ta ƙofar da ya shiga, amma kowa zai fita a ƙofar ɗaura da wadda ya shiga.
But when the people of the land come before Jehovah in the solemn feasts, he that entereth by the way of the north gate to worship shall go out by the way of the south gate; and he that entereth by the way of the south gate shall go forth by the way of the north gate; he shall not return by the way of the gate by which he entered, but shall go forth over against it.
10 Sarki zai kasance a cikinsu, zai shiga sa’ad da suke shiga ya kuma fita sa’ad da suka fita.
And the prince shall go in in the midst of them when they go in, and when they go forth shall he go forth.
11 “‘A bukukkuwa da ƙayyadaddun bukukkuwa, hadaya ta gari zai zama efa tare da bijimi, efa da rago, da kuma’yan raguna da ya ga dama, haɗe da kwalabar mai.
And in the feasts and in the solemn assemblies the flour-offering shall be an ephah for a bullock, and an ephah for a ram, and for the lambs what he is disposed to give; and a hin of oil to an ephah.
12 Sa’ad da sarki ya ba da hadaya ta yardar rai ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa ce ko hadayun salama ne, sai a buɗe masa ƙofar da take fuskantar gabas. Zai miƙa hadayarsa ta ƙonawa ko hadayarsa ta salama yadda yakan yi a ranar Asabbaci. Sa’an nan ya fita, bayan kuma ya fita, sai a rufe ƙofar.
And when the prince shall present a free-will burnt-offering or a free-will thank-offering to Jehovah, the gate that looketh toward the east shall be opened for him, and he shall present his burnt-offering, or his thank-offering, as he was wont to do on the sabbath-day; then he shall go forth, and the gate shall be shut after he hath gone forth.
13 “‘Kullum za ku tanada ɗan rago bana ɗaya marar lahani don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji; kowace safiya za ku tanada shi.
And thou shalt present for a burnt-offering daily to Jehovah a lamb that is a year old without blemish; every morning shalt thou present it.
14 Tare da shi za ku tanada hadaya ta gari kowace safiya, da ya haɗa da kashi ɗaya bisa shida na efa tare da kashi ɗaya bisa uku na mai ga garin da aka cuɗa. Miƙawar wannan hadaya ta gari ga Ubangiji dawwammamiyar farilla ce.
And thou shalt present with it every morning a flour-offering, the sixth part of an ephah, and the third part of a hin of oil to moisten the fine flour, for a flour-offering to Jehovah, by a perpetual statute continually.
15 Saboda haka za a tanada ɗan rago da hadaya ta gari da kuma mai kowace safiya don hadaya ta ƙonawa ta kullum.
Thus shall they prepare the lamb, and the flour-offering, and the oil, every morning, for a continual burnt-offering.
16 “‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa in sarkin ya ba wa ɗaya daga cikin’ya’yansa kyauta daga gādonsa, zai kuwa zama na zuriyar; zai kuwa zama mallakarsu ta wurin gādo.
Thus saith the Lord Jehovah: If the prince give a gift to any of his sons, the inheritance thereof shall belong to his sons; it shall be their possession by inheritance.
17 In kuma ya ba wa ɗaya daga cikin bayinsa kyauta daga gadonsa, bawan zai iya riƙe shi sai shekarar’yantarwa; sa’an nan ya mayar wa sarkin. Gādon sarki na’ya’yansa maza ne kaɗai; na su ne.
But if he give a gift of his inheritance to one of his servants, it shall be his to the year of liberty, when it shall return to the prince. But his inheritance given to his sons shall be theirs.
18 Kada sarki ya ƙwace gādon mutane, yana korinsu daga mallakarsu. Zai ba wa’ya’yansa maza gādonsu daga cikin mallakarsa, don kada a raba wani daga mutanena da mallakarsa.’”
And the prince shall not take of the people's inheritance, to thrust them out of their possession; but he shall give an inheritance to his sons out of his own possession; that no one of my people may be driven from his possession.
19 Sa’an nan mutumin ya fitar da ni ta ƙofar shiga a gefen ƙofar zuwa tsarkakakkun ɗakuna waɗanda suke fuskantar arewa, waɗanda suke na firistoci, ya kuma nuna mini wani wuri daga can ƙurewar yamma.
Then he brought me through the entry, which was at the side of the gate, into the holy rooms for the priests, which looked toward the north; and behold, there was a place behind toward the west.
20 Ya ce mini, “Wannan shi ne wurin da firistoci za su dafa hadaya don laifi, da hadaya don zunubi, a nan ne kuma za su toya hadaya ta gari, domin kada su kai su a filin da yake waje, su tsarkake mutane.”
And he said to me: This is the place where the priests shall boil the trespass-offering, and the sin-offering, and bake the flour-offering; that they may not bear them into the outer court, and so sanctify the people.
21 Sa’an nan ya kawo ni filin da yake waje ya kuma bi da ni kewaye da kusurwoyi huɗunsa, na kuma ga kowace kusurwa na wani fili.
Then he brought me forth into the outer court, and caused me to pass by the four corners of the court; and behold, there was a court in every corner of the court.
22 A kusurwoyi huɗu na filin da yake waje akwai waɗansu filaye a haɗe, tsawonsu kamu arba’in fāɗinsu kuwa kamu talatin; kowane fili a kusurwoyi huɗun nan girmansu ɗaya ne.
In the four corners of the court were covered courts forty cubits long, and thirty broad; these four corners were of one measure.
23 Kewaye da cikin kowane filin huɗun nan akwai ginin dutse, da murhu da aka gina a kewaye a ƙarƙashin ginin.
And there was in them a wall round about, even round about the four; and boiling-places were made under the walls round about.
24 Sai ya ce mini, “Waɗannan su ne ɗakunan dahuwa inda masu hidima a haikali za su dafa hadayun da jama’a.”
Then said he to me, These are the places of them that boil, where the ministers of the house shall boil the sacrifice of the people.

< Ezekiyel 46 >