< Ezekiyel 44 >

1 Sai mutumin ya komo da ni zuwa ƙofar waje na wuri mai tsarki, wadda take fuskantar gabas, tana kuwa a rufe.
Puis il me ramena au chemin de la porte extérieure du Sanctuaire, laquelle regardait l'Orient, et elle était fermée.
2 Ubangiji ya ce mini, “Wannan ƙofar za tă kasance a rufe. Ba za a buɗe ta ba; ba wanda zai shiga ta wurinta. Za tă kasance a rufe domin Ubangiji, Allah na Isra’ila, ya shiga ta wurinta.
Et l'Eternel me dit: cette porte-ci sera fermée, [et] ne sera point ouverte, et personne n'y passera, parce que l'Eternel le Dieu d'Israël est entré par cette porte; elle sera donc fermée.
3 Sarki kansa ne kaɗai zai zauna a hanyar shiga don yă ci a gaban Ubangiji. Zai shiga ta hanyar shirayin hanyar shiga yă kuma fita a wannan hanya.”
[Elle sera] pour le Prince: le Prince sera le seul qui s'y assiéra pour manger devant l'Eternel; il entrera par le chemin de l'allée de cette porte-là, et sortira par le même chemin.
4 Sa’an nan mutumin ya kawo ni ta hanyar ƙofar arewa zuwa gaban haikali. Na duba na kuma ga ɗaukakar Ubangiji tana cika haikalin Ubangiji, sai na fāɗi rubda ciki.
Et il me fit revenir par le chemin de la porte du Septentrion jusque sur le devant de la maison, et je regardai, et voici, la gloire de l'Eternel avait rempli la maison de l'Eternel, et je me prosternai sur ma face.
5 Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, ka lura sosai, ka saurara sosai ka kuma mai da hankali ga kome da na faɗa maka game da dukan ƙa’idodi game da haikalin Ubangiji. Ka lura sosai da ƙofar shigar haikali da kuma dukan ƙofofin wuri mai tsarki.
Alors l'Eternel me dit: fils d'homme, applique ton cœur, et regarde de tes yeux, et écoute de tes oreilles tout ce dont je te vais parler, touchant toutes les ordonnances et toutes les lois qui concernent la maison de l'Eternel: applique ton cœur à ce qui concerne l'entrée de la maison par toutes les sorties du Sanctuaire.
6 Faɗa wa’yan tawayen gidan Isra’ila, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ayyukan banƙyamarku sun isa haka, ya gidan Isra’ila!
Tu diras donc à [ceux qui sont extrêmement] rebelles, [savoir] à la maison d'Israël: ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: maison d'Israël! Qu'il vous suffise qu'entre toutes vos abominations,
7 Ban da dukan sauran ayyukanku na banƙyama, kun kawo baƙi marasa kaciya a zuciya da jiki a wurina mai tsarki, kun kuma ƙazantar da haikalina yayinda kuke miƙa mini abinci, kitse da kuma jini, kun kuma karya alkawarina.
Vous ayez fait entrer les enfants de l'étranger, qui étaient incirconcis de cœur, et incirconcis de chair, pour être dans mon Sanctuaire, afin de profaner ma maison, quand vous avez offert ma viande, [savoir] la graisse et le sang, et ils ont enfreint mon alliance, outre toutes vos [autres] abominations.
8 A maimakon yin ayyukanku bisa ga abubuwana masu tsarki, kun sa waɗansu su lura da wurina mai tsarki.
Et vous n'avez point donné ordre que mes choses saintes fussent observées, mais vous avez établi comme il vous a plu dans mon Sanctuaire, des gens pour y être les gardes des choses que j'avais commandé de garder.
9 Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba baƙo marar kaciya a zuciya da jiki da zai shiga wurina mai tsarki, kai, har ma da baƙin da suke zama a cikin Isra’ila.
Ainsi a dit le Seigneur l'Eternel: pas un de tous ceux qui seront enfants d'étranger, incirconcis de cœur, et incirconcis de chair, n'entrera dans mon Sanctuaire, même pas un d'entre tous les enfants d'étranger, qui seront parmi les enfants d'Israël.
10 “‘Lawiyawan da suka yi nesa da ni sa’ad da Isra’ila suka kauce da kuma waɗanda suka karkata daga gare ni suka bi gumakansu, dole su ɗauki alhakin zunubinsu.
Mais les Lévites qui se sont éloignés de moi, lorsque Israël s'est égaré, et qui se sont égarés de moi pour suivre leurs idoles, porteront [la peine de] leur iniquité.
11 Za su iya yin hidima a wurina mai tsarki, suna lura da ƙofofin haikali suna kuma hidima a cikinsu; za su iya yankan hadayun ƙonawa da sadaka don mutane su kuma tsaya a gaban mutane su yi musu hidima.
Toutefois ils seront employés dans mon Sanctuaire aux charges qui sont vers les portes de la maison, et ils feront le service de la maison; ils égorgeront pour le peuple [les bêtes pour] l'holocauste, et [pour] les [autres] sacrifices, [et] se tiendront [prêts] devant lui pour le servir.
12 Amma domin sun yi musu hidima a gaban gumakansu suka sa gidan Isra’ila ya yi zunubi, saboda haka na ɗaga hannu na rantse cewa dole su ɗauki alhakin zunubinsu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Parce qu'ils les ont servis [se présentant] devant leurs idoles, et qu'ils ont été une occasion de chute dans le crime à la maison d'Israël, à cause de cela j'ai levé ma main [en jurant] contre eux, dit le Seigneur l'Eternel, qu'ils porteront [la peine de] leur iniquité.
13 Ba za su yi kusa don su yi hidima kamar firistoci ko su zo kusa da abubuwana masu tsarki ko hadayuna mafi tsarki ba; dole su sha kunya saboda ayyukansu na banƙyama.
Tellement qu'ils n'approcheront plus de moi pour m'exercer la sacrificature, ni pour approcher d'aucune de mes choses saintes aux lieux les plus saints, mais ils porteront leur confusion et leurs abominations, lesquelles ils ont commises.
14 Duk da haka zan sa su su lura da ayyukan haikali da kuma dukan ayyukan da za a yi a cikinsa.
C'est pourquoi je les établirai pour avoir la garde de la maison pour tout son service, et pour tout ce qui s'y fait.
15 “‘Amma firistoci, waɗanda suke Lawiyawa kuma zuriyar Zadok waɗanda suka yi aminci ta wurin yin ayyukansu a wurina mai tsarki sa’ad da Isra’ilawa suka kauce daga gare ni, su ne za su zo kusa don hidima a gabana; za su tsaya a gabana don miƙa hadayun kitse da jini, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Mais quant aux Sacrificateurs Lévites, enfants de Tsadok, qui ont soigneusement administré ce qu'il fallait faire dans mon Sanctuaire, lorsque les enfants d'Israël se sont éloignés de moi, ceux-là s'approcheront de moi pour faire mon service, et se tiendront devant moi pour m'offrir la graisse et le sang, dit le Seigneur l'Eternel.
16 Su ne kaɗai za su shiga wurina mai tsarki; su ne kaɗai za su zo kusa da teburina don yin hidima a gabana su kuma yi hidimata.
Ceux-là entreront dans mon Sanctuaire, et ceux-là s'approcheront de ma table, pour faire mon service, et ils administreront soigneusement ce que j'ai ordonné de faire.
17 “‘Sa’ad da suka shiga ƙofofin fili na can ciki, dole su sa tufafin lilin; kada su sa wani rigar da aka yi da ulu yayinda suke hidima a ƙofofin fili na can ciki da cikin haikali.
Et il arrivera que quand ils entreront aux portes des parvis intérieurs, ils se vêtiront de robes de lin; et il n'y aura point de laine sur eux pendant qu'ils feront le service aux portes des parvis intérieurs et dans le Temple.
18 Za su naɗa rawunan lilin a kawunansu, su kuma sa wandunan lilin. Kada su sa wani abin da zai sa su yi zuffa.
Ils auront des ornements de lin sur leur tête, et des caleçons de lin sur leurs reins, [et] ne se ceindront point à l'endroit où l'on sue.
19 Sa’ad da suka fita daga haikali zuwa fili na waje inda mutane suke, sai su tuɓe rigunan da suka yi hidima da su su bar su a tsarkakan ɗakuna, su sa waɗansu riguna, don kada su tsarkake mutane ta wurin rigunansu.
Mais quand ils sortiront au parvis extérieur, au parvis, [dis-je], extérieur, vers le peuple, ils se dévêtiront de leurs habits, avec lesquels ils font le service, et les poseront dans les chambres saintes, et se revêtiront d'autres habits, afin qu'ils ne sanctifient point le peuple avec leurs habits.
20 “‘Ba za su aske kawunansu ko su bar gashin kansu ya yi tsayi ba, amma sai su sausaye gashin kansu.
Ils ne se raseront point la tête, ni ne laisseront point croître leurs cheveux, mais simplement ils tondront leurs têtes.
21 Kada firist ya sha ruwan inabi sa’ad da zai shiga fili na can ciki.
Pas un des Sacrificateurs ne boira du vin, quand ils entreront au parvis intérieur.
22 Kada su auri gwauruwa ko macen da aka sāke; za su auri budurwai ne kaɗai na Isra’ilawa ko gwaurayen firistoci.
Ils ne prendront point pour femme une veuve, ni une répudiée; mais ils prendront des vierges, de la race de la maison d'Israël, ou une veuve qui soit veuve d'un Sacrificateur.
23 Za su koyar da mutanena bambanci tsakanin tsarki da rashin tsarki su kuma nuna musu yadda za su bambanta marar tsarki da mai tsarki.
Et ils enseigneront à mon peuple la différence qu'il y a entre la chose sainte et la chose profane, et leur feront entendre la différence qu'il y a entre ce qui est souillé et ce qui est net.
24 “‘A duk wani rashin jituwa, firistoci za su zama alƙalai su kuma yanke magana bisa ga farillaina. Za su kiyaye dokokina da ƙa’idodina a dukan ƙayyadaddun bukukkuwana, su kuma kiyaye Asabbataina da tsarki.
Et quand il surviendra quelque procès, ils assisteront au jugement, et jugeront suivant les lois que j'ai données; et ils garderont mes lois et mes statuts dans toutes mes solennités, et ils sanctifieront mes Sabbats.
25 “‘Firist ba zai ƙazantar da kansa ta wurin zuwa kusa da gawa ba; amma, in gawar mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ko ɗansa ko’yarsa, ko ɗan’uwansa ko’yar’uwarsa ce, to, ba zai ƙazantar da kansa ba.
[Pas un des Sacrificateurs] n'entrera vers le corps mort d'aucun homme, de peur d'en être souillé, si ce n'est que ce soit pour leur père, pour leur mère, pour leur fils, pour leur fille, pour leur frère, et pour leur sœur qui n'aura point eu de mari.
26 Bayan ya tsarkaka, dole yă jira har kwana bakwai.
Et après que chacun d'eux se sera purifié, on lui comptera sept jours;
27 A ranar da ya shiga fili na can ciki na wuri mai tsarki don hidima a wuri mai tsarki, zai miƙa hadaya don zunubi saboda kansa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Et le jour qu'il entrera aux lieux saints, [savoir] au parvis intérieur pour faire le service aux lieux saints, il offrira un [sacrifice pour] son péché, dit le Seigneur l'Eternel.
28 “‘Ni ne kaɗai zan zama abin gādon da firistoci za su kasance da shi. Kada ka ba su wani mallaka a Isra’ila; zan zama mallakarsu.
Et cela leur sera pour héritage. Ce sera moi qui serai leur héritage, car vous ne leur donnerez aucune possession en Israël, et ce sera moi qui serai leur possession.
29 Za su ci hadaya ta gari, hadaya don zunubi da hadaya don laifi; da kuma kowane keɓaɓɓen abu a Isra’ila da za a ba wa Ubangiji zai zama nasu.
Ils mangeront donc les gâteaux et [ce qui s'offrira pour] le péché, et [ce qui s'offrira pour] le délit; et tout interdit en Israël leur appartiendra.
30 Mafi kyau na nunan farinku da kuma dukan kyautanku na musamman za su zama na firistoci. Za ku ba su rabo na fari na ɓarzajjen hatsinku saboda albarka ta kasance a gidanku.
Et les prémices de tout ce qui est produit le premier en toutes choses, et de tout ce qui sera présenté en offrande élevée de toutes choses, d'entre toutes vos offrandes élevées, appartiendront aux Sacrificateurs; vous donnerez aussi les prémices de vos pâtes aux Sacrificateurs, afin qu'ils fassent reposer la bénédiction sur la maison de chacun de vous.
31 Firistoci ba za su ci mushen tsuntsu ko na dabba ba, ba kuwa za su ci waɗanda namun jeji suka kashe ba.
Les Sacrificateurs ne mangeront point de chair d'aucune bête morte d'elle-même, ni rien de déchiré, soit oiseau, soit bête à quatre pieds.

< Ezekiyel 44 >