< Ezekiyel 43 >

1 Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da take fuskantar gabas,
Zatem me je privedel k velikim vratom, celó velikim vratom, ki gledajo proti vzhodu.
2 sai na ga ɗaukakar Allah na Isra’ila tana tahowa daga gabas. Muryarsa ta yi kamar rurin ruwaye masu gudu, ƙasa kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.
In glej, slava Izraelovega Boga je prišla po poti od vzhoda, in njegov glas je bil podoben hrupu mnogih vodá, in zemlja je zasijala z njegovo slavo.
3 Wahayin da na gani ya yi kamar wahayin da na gani sa’ad da ya zo don yă hallaka birnin, kamar kuma wahayin da na gani kusa da Kogin Kebar, na kuwa fāɗi rubda ciki.
In to je bilo glede na videz videnja, ki sem ga videl, celó glede na videnje, ki sem ga videl, ko sem prišel, da uničim mesto; in videnja so bila podobna videnju, ki sem ga videl pri reki Kebár; in padel sem na svoj obraz.
4 Ɗaukakar Ubangiji ta shiga haikali ta ƙofar da take fuskantar gabas.
Gospodova slava je prišla v hišo po poti velikih vrat, katerih pročelje je proti vzhodu.
5 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin fili na can ciki, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
Tako me je duh vzel gor in me privedel na notranji dvor; in, glej, Gospodova slava je napolnila hišo.
6 Yayinda mutumin yana tsaye kusa da ni, na ji wani yana magana da ni daga cikin haikalin.
Slišal sem ga, kako mi govori iz hiše; in poleg mene je stal mož.
7 Ya ce, “Ɗan mutum, wannan shi ne kursiyina da wurin tafin ƙafafuna. A nan ne zan zauna a cikin Isra’ilawa har abada. Gidan Isra’ila ba zai ƙara ɓata sunana mai tsarki ba, ko su ko sarakunansu, ta wurin karuwanci da gumakan da ba su da rai, sarakunansu a masujadan kan tudu.
Rekel mi je: »Človeški sin, prostor mojega prestola in kraj za podplate mojih stopal, kjer bom na veke prebival v sredi Izraelovih otrok in mojega svetega imena Izraelova hiša ne bo več omadeževala, niti oni, niti njihovi kralji s svojim vlačugarstvom, niti s trupli svojih kraljev na svojih visokih krajih.
8 Sa’ad da suka sa madogarar ƙofarsu kusa da madogarar ƙofata, da katanga kawai a tsakanina da su, sun ɓata sunana mai tsarki ta wurin ayyukansu masu banƙyama. Saboda haka na hallaka su cikin fushina.
V njihovi postavitvi njihovega praga ob mojih pragovih in njihovega podboja ob mojih podbojih in zidom med menoj in njimi, so celo omadeževali moje sveto ime s svojimi ogabnostmi, ki so jih zagrešili. Zatorej sem jih použil v svoji jezi.
9 Yanzu bari su kawar da karuwancinsu da gumakansu waɗanda ba su da rai na sarakunansu daga gabana, zan kuwa zauna a cikinsu har abada.
Torej naj odstranijo svoje vlačugarstvo in trupla svojih kraljev daleč od mene in jaz bom prebival v njihovi sredi na veke.
10 “Ɗan mutum, ka bayyana haikalin ga mutanen Isra’ila, don su ji kunya saboda zunubansu. Bari su yi la’akari da fasalin,
Ti, človeški sin, pokaži Izraelovi hiši, da jih bo lahko sram njihovih krivičnosti in naj izmerijo vzorec.
11 kuma in suka ji kunyar abubuwan da suka aikata, sai ka sanar musu fasalin haikalin da shirye-shiryensa, ƙofofinsa na shiga da fita, dukan fasalinsa da dukan ƙa’idodinsa da dokokinsa. Ka rubuta waɗannan a gabansu saboda su yi aminci da fasalinsa su kuma kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
Če se bodo sramovali vsega, kar so storili, jim pokaži obliko hiše, njen slog, njene izhode, njene vhode, vse njene oblike, vse njene odredbe, vse njene oblike in vse njene postave, in zapiši jih v njihovem pogledu, da se bodo lahko držali njene celotne oblike in vseh njenih odredb in jih izpolnjevali.«
12 “Wannan ita ce dokar haikalin. Dukan filin da yake kewaye a kan dutsen, zai zama wuri mafi tsarki. Dokar haikalin ke nan.
To je postava hiše: ›Na vrhu gore bo njena celotna meja naokrog najsvetejšega.‹ Glej, to je postava hiše.«
13 “Waɗannan su ne aune-aunen bagade a tsawon kamu, wannan kamu shi ne kamun tafin hannu. Zurfin magudanar ruwansa kamu ɗaya ne fāɗinsa kuma kamu ɗaya, tare da da’ira kamun tafi ɗaya kewaye da gefensa. Wannan kuma shi ne tsayin bagaden.
In to so mere oltarja po komolcih: ›Komolec je komolec in širina roke; celo dno bo komolec in širina komolca in njena meja ob njenem robu naokrog bo pedenj in to bo višji kraj oltarja.
14 Daga lambatun da yake a ƙasa har zuwa ƙaramin mahaɗin da yake ƙasa wanda ya kewaye bagade, tsayinsa kamu biyu ne, fāɗinsa kuma kamu guda. Daga ƙaramin mahaɗi zuwa babban mahaɗin wanda ya kewaye bagade, zai zama kamu huɗu, fāɗinsa kuwa kamu ɗaya.
Od dna na tleh, celó do spodnjega podzidka, bo dva komolca in širina en komolec; in od manjšega podzidka celó do večjega podzidka, bo štiri komolce in širina en komolec.
15 Murhun bagaden kamu huɗu ne, akwai ƙahoni guda huɗu sun miƙe sama daga murhun.
Tako bo oltar štiri komolce; in od oltarja in navzgor bodo štirje rogovi.
16 Murhun bagaden murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha biyu, fāɗinsa kuma kamu goma sha biyu.
Oltar bo dvanajst komolcev dolg, dvanajst širok, kvadraten v svojih štirih oglih.
17 Gefen bisa ma murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha huɗu fāɗinsa kuma kamu goma huɗu, da da’ira da yake da fāɗin rabin kamu da magudanan ruwa kamu guda kewaye. Matakan bagaden suna fuskantar gabas.”
Podzidek bo štirinajst komolcev dolg in štirinajst širok v svojih štirih oglih; in rob okoli njega bo pol komolca; in njegovo dno bo komolec naokrog; in njegove stopnice bodo gledale proti vzhodu.
18 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa waɗannan su ne za su zama ƙa’idodi don yin hadaya ta ƙonawa da yayyafawar jini a kan bagaden sa’ad da aka gina shi.
Rekel mi je: »Človeški sin, tako govori Gospod Bog: ›To so odredbe oltarja na dan, ko ga bodo naredili, da bodo na njem darovali žgalne daritve in da bodo na njem škropili kri.
19 Za ka ba da ɗan bijimi a matsayin hadaya ta ƙonawa ga firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, na iyalin Zadok, waɗanda suke zuwa kusa don hidima a gabana, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Duhovnikom Lévijevcem, ki bodo od Cadókovega semena, ki pristopajo k meni, da bi mi služili, ‹ govori Gospod Bog, ›boš dal mladega bikca za daritev za greh.
20 Za ka ɗibi jininsa ka zuba shi a ƙahoni huɗu na bagaden a gefen bisa da kuma kewaye da da’irar, ta haka za ka tsarkake bagaden ka kuma yi kafara dominsa.
Vzel boš od njegove krvi in jo nanesel na štiri njegove rogove in na štiri vogle podzidka in na rob naokoli. Tako ga boš očistil in prečistil.
21 Za ka ɗauki bijimi na hadaya don zunubi ka ƙone shi a sashen da aka shirya na haikalin a wani wuri waje da wuri mai tsarki.
Vzel boš tudi bikca daritve za greh in zažgal ga bo na določenem prostoru hiše, zunaj svetišča.
22 “A rana ta biyu za ka miƙa bunsuru marar lahani domin hadaya don zunubi, za a kuma tsarkake bagaden yadda aka yi da bijimin.
Na drugi dan boš daroval kozlička od koz, brez pomanjkljivosti, za daritev za greh; in očistili bodo oltar, kakor so ga očistili z bikcem.
23 Sa’ad da ka gama tsarkake shi, sai ka miƙa ɗan bijimi da kuma rago daga cikin garke, dukansu marasa lahani.
Ko narediš konec njegovemu očiščevanju, boš daroval mladega bikca, brez pomanjkljivosti in ovna iz tropa, brez pomanjkljivosti.
24 Za ka miƙa su a gaban Ubangiji, firistoci kuma za su barbaɗe gishiri a kansu su kuma miƙa su kamar hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
Daroval ju boš pred Gospodom in duhovniki bodo nanje vrgli sol in darovali jih bodo za žgalno daritev Gospodu.
25 “Kwana bakwai za ka tanada bunsuru kullum domin hadaya don zunubi; za ka kuma tanada ɗan bijimi da rago daga garke, dukansu marasa lahani.
Sedem dni boš vsak dan pripravljal kozla za daritev za greh. Pripravljali bodo tudi mladega bikca in ovna iz tropa, brez pomanjkljivosti.
26 Kwana bakwai za su yi kafara saboda bagaden su kuma tsarkake shi; ta haka za su keɓe shi.
Sedem dni bodo očiščevali oltar in ga prečiščevali in se uméščali.
27 A ƙarshen waɗannan kwanaki, daga rana ta takwas zuwa gaba, firistoci za su miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kan bagade. Sa’an nan zan karɓe ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Ko se ti dnevi iztečejo, bo tako, da bodo na osmi dan in tako naprej, duhovniki pripravljali vaše žgalne daritve na oltarju in vaše mirovne daritve; in jaz vas bom sprejel, ‹ govori Gospod Bog.«

< Ezekiyel 43 >