< Ezekiyel 43 >

1 Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da take fuskantar gabas,
The man then brought me to the gate that opened to the east.
2 sai na ga ɗaukakar Allah na Isra’ila tana tahowa daga gabas. Muryarsa ta yi kamar rurin ruwaye masu gudu, ƙasa kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.
Behold! The glory of the God of Israel came from the east; his voice was like the sound of many waters, and the earth shone with his glory.
3 Wahayin da na gani ya yi kamar wahayin da na gani sa’ad da ya zo don yă hallaka birnin, kamar kuma wahayin da na gani kusa da Kogin Kebar, na kuwa fāɗi rubda ciki.
It was according to the appearance of the vision that I saw, according to the vision that I saw when he had come to destroy the city, and the visions were like the vision that I saw at the Kebar Canal—and I fell to my face.
4 Ɗaukakar Ubangiji ta shiga haikali ta ƙofar da take fuskantar gabas.
So the glory of Yahweh came to the house by way of the gate that opened to the east.
5 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin fili na can ciki, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
Then the Spirit lifted me up and brought me into the inner court. Behold! The glory of Yahweh was filling the house.
6 Yayinda mutumin yana tsaye kusa da ni, na ji wani yana magana da ni daga cikin haikalin.
The man was standing beside me, and I heard someone else speaking to me from the house.
7 Ya ce, “Ɗan mutum, wannan shi ne kursiyina da wurin tafin ƙafafuna. A nan ne zan zauna a cikin Isra’ilawa har abada. Gidan Isra’ila ba zai ƙara ɓata sunana mai tsarki ba, ko su ko sarakunansu, ta wurin karuwanci da gumakan da ba su da rai, sarakunansu a masujadan kan tudu.
He said to me, “Son of man, this is the place of my throne and the place for the soles of my feet, where I will live in the midst of the people of Israel forever. The house of Israel will no longer profane my holy name—they or their kings—with their faithlessness or with the corpses of their kings at their high places.
8 Sa’ad da suka sa madogarar ƙofarsu kusa da madogarar ƙofata, da katanga kawai a tsakanina da su, sun ɓata sunana mai tsarki ta wurin ayyukansu masu banƙyama. Saboda haka na hallaka su cikin fushina.
They will no longer profane my holy name by putting their threshold next to my threshold, and their gateposts next to my gateposts, with nothing but a wall between me and them. They profaned my holy name with their disgusting actions, so I consumed them with my anger.
9 Yanzu bari su kawar da karuwancinsu da gumakansu waɗanda ba su da rai na sarakunansu daga gabana, zan kuwa zauna a cikinsu har abada.
Now let them remove their faithlessness and the corpses of their kings from before me, and I will live in their midst forever.
10 “Ɗan mutum, ka bayyana haikalin ga mutanen Isra’ila, don su ji kunya saboda zunubansu. Bari su yi la’akari da fasalin,
Son of man, you yourself must tell the house of Israel about this house so they will be ashamed of their iniquities. They should think about this description.
11 kuma in suka ji kunyar abubuwan da suka aikata, sai ka sanar musu fasalin haikalin da shirye-shiryensa, ƙofofinsa na shiga da fita, dukan fasalinsa da dukan ƙa’idodinsa da dokokinsa. Ka rubuta waɗannan a gabansu saboda su yi aminci da fasalinsa su kuma kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
For if they are ashamed of all that they have done, then reveal to them the design of the house, its details, its exits, its entrances, and all its designs, all its decrees and rules. Then write this down before their eyes so they will keep to all its design and all its rules, so as to obey them.
12 “Wannan ita ce dokar haikalin. Dukan filin da yake kewaye a kan dutsen, zai zama wuri mafi tsarki. Dokar haikalin ke nan.
This is the regulation for the house: From the peak of the hill to all the surrounding border around it, it will be most holy. Behold! This is the regulation for the house.
13 “Waɗannan su ne aune-aunen bagade a tsawon kamu, wannan kamu shi ne kamun tafin hannu. Zurfin magudanar ruwansa kamu ɗaya ne fāɗinsa kuma kamu ɗaya, tare da da’ira kamun tafi ɗaya kewaye da gefensa. Wannan kuma shi ne tsayin bagaden.
These will be the measurements of the altar in cubits—that cubit being a regular cubit and a handbreadth in length. So the gutter around the altar will be a cubit deep, and its width will also be a cubit. The border around its surrounding edge will be one span. This will be the base of the altar.
14 Daga lambatun da yake a ƙasa har zuwa ƙaramin mahaɗin da yake ƙasa wanda ya kewaye bagade, tsayinsa kamu biyu ne, fāɗinsa kuma kamu guda. Daga ƙaramin mahaɗi zuwa babban mahaɗin wanda ya kewaye bagade, zai zama kamu huɗu, fāɗinsa kuwa kamu ɗaya.
From the gutter at the ground level up to the lower ledge of the altar is two cubits, and that ledge itself is one cubit in width. Then from the small ledge up to the large edge of the altar, it is four cubits, and the large edge is a cubit in width.
15 Murhun bagaden kamu huɗu ne, akwai ƙahoni guda huɗu sun miƙe sama daga murhun.
The hearth on the altar for the burnt offerings is four cubits high, and there are four horns pointing upward on the hearth.
16 Murhun bagaden murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha biyu, fāɗinsa kuma kamu goma sha biyu.
The hearth is twelve cubits in length and twelve cubits in width, a square.
17 Gefen bisa ma murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha huɗu fāɗinsa kuma kamu goma huɗu, da da’ira da yake da fāɗin rabin kamu da magudanan ruwa kamu guda kewaye. Matakan bagaden suna fuskantar gabas.”
Its border is fourteen cubits in length and fourteen cubits in width on each of its four sides, and its rim is a half cubit in width. The gutter is a cubit in width all around with its steps facing east.”
18 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa waɗannan su ne za su zama ƙa’idodi don yin hadaya ta ƙonawa da yayyafawar jini a kan bagaden sa’ad da aka gina shi.
Next he said to me, “Son of man, the Lord Yahweh says this: These are the regulations for the altar on the day they make it, for raising the burnt offering onto it, and for sprinkling blood on it.
19 Za ka ba da ɗan bijimi a matsayin hadaya ta ƙonawa ga firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, na iyalin Zadok, waɗanda suke zuwa kusa don hidima a gabana, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
You will give a bull from the cattle as a sin offering for the Levitical priests who are the descendants of Zadok, those who come near to me to serve me—this is the Lord Yahweh's declaration.
20 Za ka ɗibi jininsa ka zuba shi a ƙahoni huɗu na bagaden a gefen bisa da kuma kewaye da da’irar, ta haka za ka tsarkake bagaden ka kuma yi kafara dominsa.
Then you will take some of its blood and place it on the altar's four horns and the four sides of its edge and on the surrounding rim; you will cleanse it and make atonement for it.
21 Za ka ɗauki bijimi na hadaya don zunubi ka ƙone shi a sashen da aka shirya na haikalin a wani wuri waje da wuri mai tsarki.
Then take the bull for the sin offering and burn it in the appointed part of the temple area outside of the sanctuary.
22 “A rana ta biyu za ka miƙa bunsuru marar lahani domin hadaya don zunubi, za a kuma tsarkake bagaden yadda aka yi da bijimin.
Then on the second day you will offer a male goat without blemish from the goats as a sin offering; the priests will cleanse the altar just as they cleansed it with the bull.
23 Sa’ad da ka gama tsarkake shi, sai ka miƙa ɗan bijimi da kuma rago daga cikin garke, dukansu marasa lahani.
When you finish its cleansing, offer an unblemished bull from the cattle and an unblemished ram from the flock.
24 Za ka miƙa su a gaban Ubangiji, firistoci kuma za su barbaɗe gishiri a kansu su kuma miƙa su kamar hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
Offer them before Yahweh; the priests will throw salt onto them and raise them up as a burnt offering to Yahweh.
25 “Kwana bakwai za ka tanada bunsuru kullum domin hadaya don zunubi; za ka kuma tanada ɗan bijimi da rago daga garke, dukansu marasa lahani.
You must prepare a male goat as a sin offering daily for seven days, and the priests must also prepare an unblemished bull of the cattle and unblemished ram from the flock.
26 Kwana bakwai za su yi kafara saboda bagaden su kuma tsarkake shi; ta haka za su keɓe shi.
They must atone for the altar for seven days and purify it, and in this way they must consecrate it.
27 A ƙarshen waɗannan kwanaki, daga rana ta takwas zuwa gaba, firistoci za su miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kan bagade. Sa’an nan zan karɓe ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
They must complete these days, and on the eighth day and onward it will come about that the priests will prepare your burnt offerings and your peace offerings on the altar, and I will accept you—this is the Lord Yahweh's declaration.”

< Ezekiyel 43 >