< Ezekiyel 43 >
1 Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da take fuskantar gabas,
Then did he lead me to the gate, even the gate that was turned in an eastern direction.
2 sai na ga ɗaukakar Allah na Isra’ila tana tahowa daga gabas. Muryarsa ta yi kamar rurin ruwaye masu gudu, ƙasa kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.
And, behold, the glory of the God of Israel came from the way of the east; and his voice was like a noise of many waters; and the earth gave light from his glory.
3 Wahayin da na gani ya yi kamar wahayin da na gani sa’ad da ya zo don yă hallaka birnin, kamar kuma wahayin da na gani kusa da Kogin Kebar, na kuwa fāɗi rubda ciki.
And it was like the appearance of the vision which I had seen, yea, like the vision that I had seen when I came to destroy the city; and the visions were like the vision that I had seen by the river Kebar: and I fell upon my face.
4 Ɗaukakar Ubangiji ta shiga haikali ta ƙofar da take fuskantar gabas.
And the glory of the Lord came into the house by the way of the gate which was turned in an eastern direction.
5 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin fili na can ciki, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
Then did the Spirit take me up, and bring me into the inner court: and, behold, the glory of the Lord filled the house.
6 Yayinda mutumin yana tsaye kusa da ni, na ji wani yana magana da ni daga cikin haikalin.
And I heard him speaking unto me out of the house; and a man was standing alongside of me.
7 Ya ce, “Ɗan mutum, wannan shi ne kursiyina da wurin tafin ƙafafuna. A nan ne zan zauna a cikin Isra’ilawa har abada. Gidan Isra’ila ba zai ƙara ɓata sunana mai tsarki ba, ko su ko sarakunansu, ta wurin karuwanci da gumakan da ba su da rai, sarakunansu a masujadan kan tudu.
And he said unto me, Son of man, [this] is the place of my throne, and the place of the soles of my feet, where I will dwell in the midst of the children of Israel forever: and the house of Israel shall not defile any more my holy name, neither they, nor their kings, by their lewdness, nor by the carcasses of their kings on their high-places.
8 Sa’ad da suka sa madogarar ƙofarsu kusa da madogarar ƙofata, da katanga kawai a tsakanina da su, sun ɓata sunana mai tsarki ta wurin ayyukansu masu banƙyama. Saboda haka na hallaka su cikin fushina.
Inasmuch as they placed their threshold by my threshold, and their door-posts close by my door-posts, and the wall being only between me and them, and they defiled my holy name by their abominations which they committed; so that I made an end of them in my anger.
9 Yanzu bari su kawar da karuwancinsu da gumakansu waɗanda ba su da rai na sarakunansu daga gabana, zan kuwa zauna a cikinsu har abada.
Now will they have to put away their lewdness, and the carcasses of their kings, far from me, and I will dwell in the midst of them for ever.
10 “Ɗan mutum, ka bayyana haikalin ga mutanen Isra’ila, don su ji kunya saboda zunubansu. Bari su yi la’akari da fasalin,
Thou, son of man, tell the house of Israel of the house, that they may be confounded because of their iniquities: and let them measure the outlines.
11 kuma in suka ji kunyar abubuwan da suka aikata, sai ka sanar musu fasalin haikalin da shirye-shiryensa, ƙofofinsa na shiga da fita, dukan fasalinsa da dukan ƙa’idodinsa da dokokinsa. Ka rubuta waɗannan a gabansu saboda su yi aminci da fasalinsa su kuma kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
And if they be confounded because of all that they have done: then let them know the form of the house, and its arrangements, and its means of egress, and its entrances, and all its forms, and all its statutes, and all its forms, and all its laws, and write them down before their eyes; that they may observe the whole of its form, and all its statutes, and carry them out.
12 “Wannan ita ce dokar haikalin. Dukan filin da yake kewaye a kan dutsen, zai zama wuri mafi tsarki. Dokar haikalin ke nan.
This is the law for the house, Upon the top of the mount shall its whole limit all round about be most holy: behold, this is the law for the house.
13 “Waɗannan su ne aune-aunen bagade a tsawon kamu, wannan kamu shi ne kamun tafin hannu. Zurfin magudanar ruwansa kamu ɗaya ne fāɗinsa kuma kamu ɗaya, tare da da’ira kamun tafi ɗaya kewaye da gefensa. Wannan kuma shi ne tsayin bagaden.
And these are the measures of the altar in cubits, The cubit is a cubit and a hand-breadth; and the bottom shall be a cubit high, and a cubit broad, and its border on its edge round about shall be a span: and this shall be the outside of the altar.
14 Daga lambatun da yake a ƙasa har zuwa ƙaramin mahaɗin da yake ƙasa wanda ya kewaye bagade, tsayinsa kamu biyu ne, fāɗinsa kuma kamu guda. Daga ƙaramin mahaɗi zuwa babban mahaɗin wanda ya kewaye bagade, zai zama kamu huɗu, fāɗinsa kuwa kamu ɗaya.
And from the bottom upon the ground up to the lower projection shall be two cubits, and the breadth one cubit; and from the lesser projection up to the greater projection shall be four cubits, and the breadth one cubit.
15 Murhun bagaden kamu huɗu ne, akwai ƙahoni guda huɗu sun miƙe sama daga murhun.
And the upper portion of the altar shall be four cubits; and from the upper surface of the altar and upward shall be the four horns.
16 Murhun bagaden murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha biyu, fāɗinsa kuma kamu goma sha biyu.
And the upper surface of the altar shall be twelve cubits long, by twelve broad, square on its four sides.
17 Gefen bisa ma murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha huɗu fāɗinsa kuma kamu goma huɗu, da da’ira da yake da fāɗin rabin kamu da magudanan ruwa kamu guda kewaye. Matakan bagaden suna fuskantar gabas.”
And the projection shall be fourteen cubits in length, by fourteen in breadth on its four sides; and the border round about it shall be half a cubit; and its bottom shall be a cubit round about; and its steps shall look toward the east.
18 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa waɗannan su ne za su zama ƙa’idodi don yin hadaya ta ƙonawa da yayyafawar jini a kan bagaden sa’ad da aka gina shi.
And he said unto me, Son of man, thus hath said the Lord Eternal, These are the statutes of the altar on the day when it shall be finished, to offer thereon burnt-offerings, and to sprinkle thereon blood.
19 Za ka ba da ɗan bijimi a matsayin hadaya ta ƙonawa ga firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, na iyalin Zadok, waɗanda suke zuwa kusa don hidima a gabana, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And thou shalt give to the priests the Levites that are of the seed of Zadok, who approach unto me, saith the Lord Eternal, to minister unto me, a young bullock for a sin-offering.
20 Za ka ɗibi jininsa ka zuba shi a ƙahoni huɗu na bagaden a gefen bisa da kuma kewaye da da’irar, ta haka za ka tsarkake bagaden ka kuma yi kafara dominsa.
And thou shalt take of his blood, and put it on its four horns, and on the four corners of the projection, and upon the border round about; and thou shalt cleanse it and make an atonement for it.
21 Za ka ɗauki bijimi na hadaya don zunubi ka ƙone shi a sashen da aka shirya na haikalin a wani wuri waje da wuri mai tsarki.
And thou shalt take the bullock of the sin-offering, and some one shall burn him at an appointed place of the house, without the sanctuary.
22 “A rana ta biyu za ka miƙa bunsuru marar lahani domin hadaya don zunubi, za a kuma tsarkake bagaden yadda aka yi da bijimin.
And on the second day shalt thou offer a he-goat without blemish for a sin-offering: and they shall cleanse the altar, as they did cleanse it with the bullock.
23 Sa’ad da ka gama tsarkake shi, sai ka miƙa ɗan bijimi da kuma rago daga cikin garke, dukansu marasa lahani.
When thou hast made an end of cleansing it, shalt thou offer a young bullock without blemish, and a ram out of the flock without blemish.
24 Za ka miƙa su a gaban Ubangiji, firistoci kuma za su barbaɗe gishiri a kansu su kuma miƙa su kamar hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
And thou shalt bring them near before the Lord, and the priests shall throw salt upon them, and they shall offer them up as a burnt-offering unto the Lord.
25 “Kwana bakwai za ka tanada bunsuru kullum domin hadaya don zunubi; za ka kuma tanada ɗan bijimi da rago daga garke, dukansu marasa lahani.
Seven days shalt thou prepare a goat for a sin-offering every day; and a young bullock, and a ram out of the flock, without blemish shall they prepare.
26 Kwana bakwai za su yi kafara saboda bagaden su kuma tsarkake shi; ta haka za su keɓe shi.
Seven days shall they atone for the altar and purify it; and they shall consecrate the same.
27 A ƙarshen waɗannan kwanaki, daga rana ta takwas zuwa gaba, firistoci za su miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kan bagade. Sa’an nan zan karɓe ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
And when these days are expired, it shall be, that on the eighth day, and thenceforward, the priests shall prepare upon the altar your burnt-offerings, and your peace-offerings: and I will accept you in favor, saith the Lord Eternal.