< Ezekiyel 43 >

1 Sai mutumin ya kawo ni ƙofar da take fuskantar gabas,
Derpå førte han mig hen til Østporten.
2 sai na ga ɗaukakar Allah na Isra’ila tana tahowa daga gabas. Muryarsa ta yi kamar rurin ruwaye masu gudu, ƙasa kuma ta haskaka da ɗaukakarsa.
Og se Israels Guds Herlighed kom østerfra, og det lød som mange Vandes Brus, og Jorden lyste af hans Herlighed.
3 Wahayin da na gani ya yi kamar wahayin da na gani sa’ad da ya zo don yă hallaka birnin, kamar kuma wahayin da na gani kusa da Kogin Kebar, na kuwa fāɗi rubda ciki.
Synet var som det, jeg havde set, da han kom for at ødelægge Byen, og Vognen så ud som den, jeg havde set ved Floden Kebar. Da faldt jeg på mit Ansigt.
4 Ɗaukakar Ubangiji ta shiga haikali ta ƙofar da take fuskantar gabas.
Og HERRENs Herlighed drog ind i Templet gennem den Port, hvis Forside vendte mod Øst.
5 Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni cikin fili na can ciki, ɗaukakar Ubangiji kuwa ta cika haikalin.
Men Ånden løftede mig op og bragte mig ind i den indre Forgård, og se, HERRENs Herlighed fyldte Templet.
6 Yayinda mutumin yana tsaye kusa da ni, na ji wani yana magana da ni daga cikin haikalin.
Og jeg hørte en tale til mig ud fra Templet, medens Manden stod ved Siden af mig,
7 Ya ce, “Ɗan mutum, wannan shi ne kursiyina da wurin tafin ƙafafuna. A nan ne zan zauna a cikin Isra’ilawa har abada. Gidan Isra’ila ba zai ƙara ɓata sunana mai tsarki ba, ko su ko sarakunansu, ta wurin karuwanci da gumakan da ba su da rai, sarakunansu a masujadan kan tudu.
og han sagde: Menneskesøn! Her er min Trones og mine Fodsålers Sted, hvor jeg vil bo midt iblandt Israeliterne til evig Tid. Israels Hus skal ikke mere vanhellige mit hellige Navn, hverken de eller deres konger, med deres Bolen eller deres kongers Lig,
8 Sa’ad da suka sa madogarar ƙofarsu kusa da madogarar ƙofata, da katanga kawai a tsakanina da su, sun ɓata sunana mai tsarki ta wurin ayyukansu masu banƙyama. Saboda haka na hallaka su cikin fushina.
de, som satte deres Tærskel lige ved min og deres Dørstolper lige ved mine, kun med en Mur imellem mig og dem, og vanhelligede mit hellige Navn ved de Vederstyggeligheder, de øvede, så jeg måtte tilintetgøre dem i min Vrede.
9 Yanzu bari su kawar da karuwancinsu da gumakansu waɗanda ba su da rai na sarakunansu daga gabana, zan kuwa zauna a cikinsu har abada.
Nu skal de fri mig for deres Bolen og deres Kongers Lig, så jeg kan bo iblandt dem til evig Tid.
10 “Ɗan mutum, ka bayyana haikalin ga mutanen Isra’ila, don su ji kunya saboda zunubansu. Bari su yi la’akari da fasalin,
Men du, Menneskesøn, giv Israels Hus en Beskrivelse af Templet, dets Udseende og Form, at de må skamme sig over deres Misgerninger.
11 kuma in suka ji kunyar abubuwan da suka aikata, sai ka sanar musu fasalin haikalin da shirye-shiryensa, ƙofofinsa na shiga da fita, dukan fasalinsa da dukan ƙa’idodinsa da dokokinsa. Ka rubuta waɗannan a gabansu saboda su yi aminci da fasalinsa su kuma kiyaye dukan ƙa’idodinsa.
Og dersom de skammer sig over alt, hvad de har gjort, så kundgør dem Templets Omrids og Indretning, dets Udgange og Indgange, et helt Billede deraf; ligeledes alle Vedtægter og Love derom; og skriv det op for deres Øjne, at de må mærke sig Billedet i sin Helhed og alle Vedtægterne og holde dem.
12 “Wannan ita ce dokar haikalin. Dukan filin da yake kewaye a kan dutsen, zai zama wuri mafi tsarki. Dokar haikalin ke nan.
Dette er Loven om Templet: På Bjergets Tinde skal alt dets Område til alle Sider være højhelligt; se, det er Loven om Templet.
13 “Waɗannan su ne aune-aunen bagade a tsawon kamu, wannan kamu shi ne kamun tafin hannu. Zurfin magudanar ruwansa kamu ɗaya ne fāɗinsa kuma kamu ɗaya, tare da da’ira kamun tafi ɗaya kewaye da gefensa. Wannan kuma shi ne tsayin bagaden.
Følgende er Alterets Mål i Alen, en Alen en Håndsbred længere end sædvanlig: Foden var en Alen høj og en Alen bred, Kantlisten Randen rundt et Spand høj. Om Alterets Højde gælder følgende:
14 Daga lambatun da yake a ƙasa har zuwa ƙaramin mahaɗin da yake ƙasa wanda ya kewaye bagade, tsayinsa kamu biyu ne, fāɗinsa kuma kamu guda. Daga ƙaramin mahaɗi zuwa babban mahaɗin wanda ya kewaye bagade, zai zama kamu huɗu, fāɗinsa kuwa kamu ɗaya.
Fra Foden underneden op til det nederste Fremspring to Alen med en Alens Bredde; og fra det lille Fremspring til det store fire Alen med en Alens Bredde.
15 Murhun bagaden kamu huɗu ne, akwai ƙahoni guda huɗu sun miƙe sama daga murhun.
Ildstedet var fire Alen højt, og fra Ildstedet ragede fire Horn i Vejret.
16 Murhun bagaden murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha biyu, fāɗinsa kuma kamu goma sha biyu.
Ildstedet var tolv Alen langt og tolv Alen bredt, så det dannede en ligesidet Firkant.
17 Gefen bisa ma murabba’i ne, tsawonsa kamu goma sha huɗu fāɗinsa kuma kamu goma huɗu, da da’ira da yake da fāɗin rabin kamu da magudanan ruwa kamu guda kewaye. Matakan bagaden suna fuskantar gabas.”
Det store Fremspring var fjorten Alen langt og fjorten Alen bredt på alle fire Sider; det lille Fremspring seksten Alen langt og seksten Alen bredt på alle fire Sider; Kantlisten rundt om en halv Alen bred og Foden en Alen bred rundt om. Trappen var på Østsiden.
18 Sai ya ce mini, “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa waɗannan su ne za su zama ƙa’idodi don yin hadaya ta ƙonawa da yayyafawar jini a kan bagaden sa’ad da aka gina shi.
Og han sagde til mig: Menneskesøn! Så siger den Herre HERREN: Følgende er Vedtægteme om Alteret, på den Dag det bygges til at ofre Brændofre og sprænge Blod på:
19 Za ka ba da ɗan bijimi a matsayin hadaya ta ƙonawa ga firistoci, waɗanda suke Lawiyawa, na iyalin Zadok, waɗanda suke zuwa kusa don hidima a gabana, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Så lyder det fra den Herre HERREN: Levitpræsterne, som nedstammer fra Zadok og må nærme sig mig for at gøre Tjeneste for mig, skal du give en ung Tyr til Syndoffer;
20 Za ka ɗibi jininsa ka zuba shi a ƙahoni huɗu na bagaden a gefen bisa da kuma kewaye da da’irar, ta haka za ka tsarkake bagaden ka kuma yi kafara dominsa.
og du skal tage noget af dens Blod og stryge det på Alterets fire Horn, på Fremspringets fire Hjørner og på Kantlisten rundt om og således rense det for Synd og fuldbyrde Soningen for det.
21 Za ka ɗauki bijimi na hadaya don zunubi ka ƙone shi a sashen da aka shirya na haikalin a wani wuri waje da wuri mai tsarki.
Og du skal tage Syndoffertyren og brænde den ved Tempelvagten uden for Helligdommen.
22 “A rana ta biyu za ka miƙa bunsuru marar lahani domin hadaya don zunubi, za a kuma tsarkake bagaden yadda aka yi da bijimin.
Næste Dag skal du bringe en lydefri Gedebuk som Syndoffer, og de skal rense Alteret for Synd, ligesom de rensede det med Tyren.
23 Sa’ad da ka gama tsarkake shi, sai ka miƙa ɗan bijimi da kuma rago daga cikin garke, dukansu marasa lahani.
Og når du er til Ende med at rense det for Synd, skal du bringe en lydefri ung Tyr og en lydefri Væder af Småkvæget;
24 Za ka miƙa su a gaban Ubangiji, firistoci kuma za su barbaɗe gishiri a kansu su kuma miƙa su kamar hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji.
du skal bringe dem for HERRENs Åsyn, og Præsterne skal strø Salt på dem og ofre dem som Brændoffer for HERREN.
25 “Kwana bakwai za ka tanada bunsuru kullum domin hadaya don zunubi; za ka kuma tanada ɗan bijimi da rago daga garke, dukansu marasa lahani.
Syv Dage skal du daglig ofre en Syndofferbuk, og man skal ofre en ung Tyr og en Væder af Småkvæget, lydefri Dyr;
26 Kwana bakwai za su yi kafara saboda bagaden su kuma tsarkake shi; ta haka za su keɓe shi.
i syv Dage skal man fuldbyrde Soningen for Alteret og rense det og indvie det.
27 A ƙarshen waɗannan kwanaki, daga rana ta takwas zuwa gaba, firistoci za su miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama a kan bagade. Sa’an nan zan karɓe ku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Således skal man bære sig ad i disse Dage. Og på den ottende Dag og siden hen skal Præsterne ofre eders Brændofre og Takofre på Alteret; og jeg vil have Behag i eder, lyder det fra den Herre HERREN.

< Ezekiyel 43 >