< Ezekiyel 4 >

1 “Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki tubalin yumɓu, ka ajiye shi a gabanka ka kuma zāna birnin Urushalima a kansa.
“Sen, ey insanoğlu, bir tuğla al, önüne koy, üzerine Yeruşalim Kenti'ni çiz.
2 Sa’an nan ka yi mata ƙawanya. Ka kafa mata katangar ƙawanya, ka gina katangar da ɗan tudu ka kewaye ta da dundurusai.
Kenti kuşat, duvarla çevir. Kente karşı toprak rampalar yap, ordugah kur, çevresine kütükler yerleştir.
3 Sa’an nan ka ɗauki kwanon ƙarfe, ka shirya shi kamar katangar ƙarfe tsakaninka da birnin ka kuma zuba mata ido. Za tă kasance a ƙarƙashin ƙawanya, kai kuwa za ka yi mata ƙawanya. Wannan zai zama alama ga gidan Isra’ila.
Sonra demir bir sac al; demirden bir duvar gibi kendinle kentin arasına koy. Yüzünü ona doğru çevir. Kent kuşatma altında tutulacak, onu sen kuşatacaksın. Bu İsrail halkı için bir belirti olacak.
4 “Sa’an nan ka kwanta a hagunka ka kuma sa zunubin gidan Isra’ila a kanka. Za ka ɗauki zunubinsu na waɗansu kwanakin da kake kwance a gefenka.
“Sonra sol yanına uzan, İsrail halkının günahını yüklen. Sol yanına uzanacağın günler kadar onların suçunun cezasını çekeceksin.
5 Na ɗora maka kwanaki bisa ga shekarun zunubinsu. Saboda haka cikin kwana 390 za ka ɗauki zunubin gidan Isra’ila.
Suçlarının yıl sayısı kadar sana gün ayırdım. Böylece üç yüz doksan gün İsrail halkının suçunun cezasını çekeceksin.
6 “Bayan ka gama haka, ka sāke kwantawa, a wannan lokaci a gefen damarka, ka kuma ɗauki zunubin gidan Yahuda. Na ɗora maka kwanaki 40, kwana guda a madadin shekara guda.
“Bunu yaptıktan sonra, bu kez sağ yanına uzan, Yahuda halkının suçunun cezasını çek. Sana kırk gün, her yıl için bir gün ayırdım.
7 Ka juya fuskarka wajen ƙawanyar Urushalima da hannunka a buɗe ka yi annabci a kanta.
Yüzünü Yeruşalim kuşatmasına çevir, çıplak kollarını kaldırıp Yeruşalim'e karşı peygamberlik et.
8 Zan ɗaura ka da igiyoyi don kada ka juya daga wannan gefe zuwa wani gefe sai ka gama kwanakin ƙawanyarka.
Kuşatma günlerini bitirinceye dek bir yandan öbür yana dönmemen için seni halatlarla bağlayacağım.
9 “Ka ɗauki alkama da sha’ir, wake da acca, gero da maiwa; ka sa su a tulun ajiya ka kuma yi amfani da su don yin burodi wa kanka. Za ka ci shi a kwanaki 390 da za ka kwanta a gefenka.
“Buğday, arpa, bakla, mercimek, darı, kızıl buğday al, bir kaba koy. Bunlardan kendine ekmek yap. Bir yanına uzanacağın üç yüz doksan gün boyunca bu ekmekten yiyeceksin.
10 Ka auna shekel ashirin na abinci don kowace rana ka kuma ci shi a ƙayyadadden lokaci.
Her gün belirli zamanda yemen için yirmi şekel ekmek tartacaksın.
11 Haka ma ka auna kashi ɗaya bisa shida na garwan ruwa ka sha shi a ƙayyadadden lokaci.
Bunun gibi suyu da belirli zamanda, ölçüyle, bir hinin altıda biri kadar içeceksin.
12 Ka ci abinci yadda za ka ci ƙosai sha’ir, ka gasa shi a gaban mutane, ka yi amfani da najasar mutane kamar itacen wuta.”
Yiyeceğini arpa pidesi yer gibi ye ve insan dışkısından ateş yakıp üzerinde halkın gözü önünde pişir.”
13 Ubangiji ya ce, “Ta haka mutanen Isra’ila za su ci ƙazantaccen abinci a cikin al’ummai inda zan kore su in kai.”
RAB, “Uluslar arasına dağıtacağım İsrail halkı böylelikle kirli sayılan yiyecekleri yiyecek” dedi.
14 Sai na ce, “Ba haka ba ne, Ubangiji Mai Iko Duka! Ban taɓa ƙazantar da kaina ba. Daga ƙuruciyata har zuwa yanzu ban taɓa cin wani abin da aka samu ya mutu ko abin da namun jeji suka kashe ba. Ba nama marar tsabtan da ya taɓa shiga bakina.”
Ben, “Eyvah, ey Egemen RAB!” diye karşılık verdim, “Hiçbir zaman kirli sayılan bir şeye dokunmadım. Gençliğimden bu yana kendiliğinden ölmüş ya da yabanıl bir hayvan tarafından öldürülmüş bir hayvanın etini yemedim, ağzıma kirli sayılan et koymadım.”
15 Sai ya ce, “To da kyau, zan bari ka gasa burodin a kan kashin shanu a maimakon najasar mutane.”
“Peki” dedi, “Ekmeğini insan dışkısı yerine tezek yakıp üzerinde pişirmene izin vereceğim.”
16 Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, zan yanke tanadin abinci a Urushalima. Mutane za su auna abincin da za su ci da tsoro su kuma auna ruwan da za su sha cikin fargaba,
Sonra, “İnsanoğlu, Yeruşalim'i her türlü yiyecekten yoksun bırakacağım” dedi, “Bu halk yiyeceğini tartıyla ve kaygı içinde yiyecek, suyunu ölçüyle ve şaşkınlık içinde içecek.
17 domin abinci da ruwa za su kāsa. Za su damu da ganin juna za su kuma lalace saboda zunubinsu.
Yiyeceği de suyu da azalacak. Hepsi şaşkınlığa düşecek, günahları içinde eriyip yok olacak.

< Ezekiyel 4 >