< Ezekiyel 4 >

1 “Yanzu, ɗan mutum, ka ɗauki tubalin yumɓu, ka ajiye shi a gabanka ka kuma zāna birnin Urushalima a kansa.
And you O son of humankind take yourself a brick and you will set it before you and you will inscribe on it a city Jerusalem.
2 Sa’an nan ka yi mata ƙawanya. Ka kafa mata katangar ƙawanya, ka gina katangar da ɗan tudu ka kewaye ta da dundurusai.
And you will make on it a siege and you will build on it a siege-wall and you will pour out on it a mound and you will set up on it armies and set on it battering-rams all around.
3 Sa’an nan ka ɗauki kwanon ƙarfe, ka shirya shi kamar katangar ƙarfe tsakaninka da birnin ka kuma zuba mata ido. Za tă kasance a ƙarƙashin ƙawanya, kai kuwa za ka yi mata ƙawanya. Wannan zai zama alama ga gidan Isra’ila.
And you take yourself a baking tray of iron and you will make it a wall of iron between you and between the city and you will direct face your to it and it will be in state of siege and you will lay siege on it [will be] a sign it for [the] house of Israel.
4 “Sa’an nan ka kwanta a hagunka ka kuma sa zunubin gidan Isra’ila a kanka. Za ka ɗauki zunubinsu na waɗansu kwanakin da kake kwance a gefenka.
And you lie down on side your left and you will put [the] iniquity of [the] house of Israel on it [the] number of the days which you will lie on it you will bear iniquity their.
5 Na ɗora maka kwanaki bisa ga shekarun zunubinsu. Saboda haka cikin kwana 390 za ka ɗauki zunubin gidan Isra’ila.
And I I have assigned to you [the] years of iniquity their to [the] number of days three hundreds and ninety day[s] and you will bear [the] iniquity of [the] house of Israel.
6 “Bayan ka gama haka, ka sāke kwantawa, a wannan lokaci a gefen damarka, ka kuma ɗauki zunubin gidan Yahuda. Na ɗora maka kwanaki 40, kwana guda a madadin shekara guda.
And you will complete these and you will lie down on side your (right *Q(K)*) a second [time] and you will bear [the] iniquity of [the] house of Judah forty day[s] a day for the year a day for the year I have assigned it to you.
7 Ka juya fuskarka wajen ƙawanyar Urushalima da hannunka a buɗe ka yi annabci a kanta.
And to [the] siege of Jerusalem you will direct face your and arm your [will be] bared and you will prophesy on it.
8 Zan ɗaura ka da igiyoyi don kada ka juya daga wannan gefe zuwa wani gefe sai ka gama kwanakin ƙawanyarka.
And there! I will put on you ropes and not you will turn yourself from side your to side your until completing you [the] days of siege your.
9 “Ka ɗauki alkama da sha’ir, wake da acca, gero da maiwa; ka sa su a tulun ajiya ka kuma yi amfani da su don yin burodi wa kanka. Za ka ci shi a kwanaki 390 da za ka kwanta a gefenka.
And you take yourself wheat and barley and bean[s] and lentils and millet and spelt and you will put them in a vessel one and you will make them for yourself into bread [the] number of the days which you - [will be] lying on side your three hundreds and ninety day[s] you will eat it.
10 Ka auna shekel ashirin na abinci don kowace rana ka kuma ci shi a ƙayyadadden lokaci.
And food your which you will eat it by weight [will be] twenty shekel[s] to the day from time to time you will eat it.
11 Haka ma ka auna kashi ɗaya bisa shida na garwan ruwa ka sha shi a ƙayyadadden lokaci.
And water by measure you will drink sixth of hin from time to time you will drink [it].
12 Ka ci abinci yadda za ka ci ƙosai sha’ir, ka gasa shi a gaban mutane, ka yi amfani da najasar mutane kamar itacen wuta.”
And a bread cake of barley you will eat it and it in [the] dung of [the] excrement of humankind you will bake it to eyes their.
13 Ubangiji ya ce, “Ta haka mutanen Isra’ila za su ci ƙazantaccen abinci a cikin al’ummai inda zan kore su in kai.”
And he said Yahweh thus they will eat [the] people of Israel bread their unclean among the nations where I will banish them there.
14 Sai na ce, “Ba haka ba ne, Ubangiji Mai Iko Duka! Ban taɓa ƙazantar da kaina ba. Daga ƙuruciyata har zuwa yanzu ban taɓa cin wani abin da aka samu ya mutu ko abin da namun jeji suka kashe ba. Ba nama marar tsabtan da ya taɓa shiga bakina.”
And I said alas! O Lord Yahweh here! self my not [has been] made unclean and a carcass and a torn animal not I have eaten since youth my and until now and not it has gone in mouth my [the] flesh of unclean meat.
15 Sai ya ce, “To da kyau, zan bari ka gasa burodin a kan kashin shanu a maimakon najasar mutane.”
And he said to me see I give to you ([the] dung of *Q(k)*) cattle in place of [the] dung of humankind and you will make bread your on them.
16 Sa’an nan ya ce mini, “Ɗan mutum, zan yanke tanadin abinci a Urushalima. Mutane za su auna abincin da za su ci da tsoro su kuma auna ruwan da za su sha cikin fargaba,
And he said to me O son of humankind here I [am] about to break [the] staff of bread in Jerusalem and they will eat bread by weight and in anxiety and water by measure and in horror they will drink.
17 domin abinci da ruwa za su kāsa. Za su damu da ganin juna za su kuma lalace saboda zunubinsu.
So that they may lack bread and water and they will be appalled everyone and brother his and they will waste away in iniquity their.

< Ezekiyel 4 >