< Ezekiyel 39 >

1 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
Tu pois, ó filho do homem, prophetiza ainda contra Gog, e dize: Assim diz o Senhor Jehovah: Eis que eu estou contra ti, ó Gog, principe e chefe de Mesech e de Tubal.
2 Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
E te farei voltar, e te porei seis anzoes, e te farei subir das bandas do norte, e te trarei aos montes de Israel.
3 Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
E tirarei o teu arco da tua mão esquerda, e farei cair as tuas frechas da tua mão direita.
4 A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
Nos montes de Israel cairás, tu e todas as tuas tropas, e os povos que estão comtigo; e ás aves de rapina, e ás aves de toda a aza, e aos animaes do campo, te dei por pasto.
5 Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Sobre a face do campo cairás, porque eu o fallei, diz o Senhor Jehovah.
6 Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
E enviarei um fogo a Magog, e entre os que habitam seguros nas ilhas; e saberão que eu sou o Senhor.
7 “‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
E farei conhecido o meu sancto nome no meio do meu povo Israel, e nunca mais deixarei profanar o meu sancto nome; e as nações saberão que eu sou o Senhor, o Sancto em Israel.
8 Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
Eis que é vindo, e será feito, diz o Senhor Jehovah: este é o dia de que tenho fallado.
9 “‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
E os habitantes das cidades de Israel sairão, e accenderão fogo, e queimarão as armas, e os escudos e as rodelas, com os arcos, e com as frechas, e com os bastões de mão, e com as lanças; e accenderão fogo com ellas por sete annos.
10 Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
E não trarão lenha do campo, nem a cortarão dos bosques, mas com as armas accenderão fogo; e roubarão aos que os roubaram, e despojarão aos que os despojaram, diz o Senhor Jehovah.
11 “‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
E succederá que, n'aquelle dia, darei ali a Gog um logar de sepultura em Israel, o valle dos que passam ao oriente do mar; e este tapará os narizes aos que passarem; e ali sepultarão a Gog, e a toda a sua multidão, e lhe chamarão o valle da multidão de Gog.
12 “‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
E a casa de Israel os enterrará por sete mezes, para purificar a terra.
13 Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Pois todo o povo da terra os enterrará, e lhes será de nomeada o dia em que eu fôr glorificado, diz o Senhor Jehovah.
14 “‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
E separarão uns homens que incessantemente passarão pela terra, para que elles, juntamente com os que passam, sepultem os que tiverem ficado sobre a face da terra, para a purificarem: ao cabo de sete mezes farão esta busca.
15 Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
E os que passam pela terra passarão, e, vendo algum o osso de um homem, lhe levantará ao pé um signal, até que os enterradores o houverem enterrado no valle da multidão de Gog.
16 Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
E tambem o nome da cidade será Hamona: assim purificarão a terra.
17 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
Tu, pois, ó filho do homem, assim diz o Senhor Jehovah, dize ás aves de toda a aza, e a todos os animaes do campo: Ajuntae-vos e vinde, congregae-vos de ao redor para o meu sacrificio, que eu sacrifiquei por vós, um sacrificio grande, nos montes de Israel, e comei carne e bebei sangue.
18 Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
Comereis a carne dos principes da terra; dos carneiros, dos cordeiros, e dos bodes, e dos bezerros, todos cevados de Basan.
19 A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
E comereis a gordura até vos fartardes, e bebereis o sangue até vos embebedardes, do meu sacrificio, que sacrifiquei por vós.
20 A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
E vos fartareis á minha mesa, de cavallos, e de carros, de valentes, e de todos os homens de guerra, diz o Senhor Jehovah.
21 “Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
E eu porei a minha gloria entre as nações, e todas as nações verão o meu juizo, que eu tiver executado, e a minha mão, que sobre ellas tiver carregado.
22 Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
E saberão os da casa de Israel que eu sou o Senhor seu Deus, desde aquelle dia em diante.
23 Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
E as nações saberão que os da casa d'Israel, por causa da sua iniquidade, foram levados em captiveiro, porque se rebellaram contra mim, e eu escondi d'elles a minha face, e os entreguei nas mãos de seus adversarios, e todos cairam á espada.
24 Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
Conforme a sua immundicia e conforme as suas prevaricações usei com elles, e escondi d'elles a minha face.
25 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
Portanto assim diz o Senhor Jehovah: Agora tornarei a trazer os captivos de Jacob, e me compadecerei de toda a casa d'Israel; zelarei pelo meu sancto nome;
26 Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
Quando houverem levado sobre si a sua vergonha, e toda a sua rebeldia, com que se rebellaram contra mim, habitando elles seguros na sua terra, sem haver quem os espantasse.
27 Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
Quando eu os tornar a trazer de entre os povos, e os houver ajuntado das terras de seus inimigos, e eu fôr sanctificado n'elles aos olhos de muitas nações,
28 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
Então saberão que eu sou o Senhor seu Deus, vendo que eu os fiz levar em captiveiro entre as nações, e os tornei a ajuntar para a sua terra, e nenhum d'elles deixei lá mais
29 Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Nem esconderei mais a minha face d'elles, quando eu houver derramado o meu espirito sobre a casa de Israel, diz o Senhor Jehovah.

< Ezekiyel 39 >