< Ezekiyel 39 >
1 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
Aa le mitokia amy Goge ry ana’ ondatio, le ano ty hoe: Inay ty nafè’ Iehovà Talè: Inao t’ie atreatreko ry Goge, roandrian-drovabei’ i Meseke naho i Tobale;
2 Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
hampitoliheko naho haronjeko mb’eo naho ho rambeseko boak’ an-kotsokotsoke fara’ i avaratsey vaho haseseko hiatreatre o vohi’ Israeleo;
3 Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
ho takapiheko boak’ am-pità’o havia ty fale’o, vaho hampipopoheko boak’ am-pità’o havana o ana-pale’ oo.
4 A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
Ie hitsingoro amo vohi’ Israeleo, ihe naho o lia-rai’o iabio naho i valobohòke mihipok’ ama’oy; hatoloko amy ze hene karaza-voroñe naho amy ze fonga mpitiliñe vaho amo bibin-kivokeo habotse’e.
5 Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Hitsingoritritse amy ze montoñe iaby irehe; amy te Izaho ty nivolañe, hoe t’Iehovà Talè.
6 Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
Hahitriko amy Magoge ty afo, naho amo mimoneñe amo tokonoseoo. vaho ho fohi’ iareo te Izaho Iehovà.
7 “‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
Izay ty hampahafohineko añivo’ ondatiko Israeleo ty tahinako masiñe naho tsy ho tivàñe ka ty añarako masiñe vaho ho fohi’ o fifeheañeo te Izaho Iehovà ro Masiñe am’Israele ao.
8 Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
Hehe te tondroke, naho toe ho heneke, hoe t’Iehovà Talè, i andro nivolañakoy.
9 “‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
Hiakatse mb’eo o mpimoneñe amo rova’ Israeleo le ho viañe’ iereo afo hamorototo o fialiañeo, o fikalañan’ arañañeo, o fañaron-tsirao, o fale naho ana-paleo, o kobaiñe naho lefoñeo vaho harehe’ iareo añ’ afo hahamodo fito taoñe;
10 Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
le tsy eo ty hitoha hatae an-kivok’ añe, ndra hamira hatae añ’ala ao; fa harehe’e añ’ afo ao o fialiañeo; naho ho kopaheñe o nikopak’ iareoo, vaho ho kamereñe o nikametse am’ iareoo, hoe t’Iehovà Talè.
11 “‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
Hifetsak’ amy andro zay te ho tolorako toetse e Israele ao ho kibori’ i Goge, i vavatanem-pitsàhañe atiñana’ i riakeiy; ze hanebam-pitsake; ao ty handeveña’ iareo i Goge naho i valobohò’ey; vaho ho tokaveñe ty hoe: Vavatanem-balobohò’ i Goge.
12 “‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
Fito volañe ty handeveña’ i anjomba’ Israeley iareo hañalio i taney.
13 Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Eka hene handenteke iareo ze ondati’ i taney, le hahazoako engeñe vaho ho andro añonjonañe ahy hoe t’Iehovà Talè.
14 “‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
Ho joboñe’ iereo ondaty mahafitoloñe, hiranga i taney mindre amo mpitsàkeo handenteke ze mbe midoñe ambone tane eo, hañalio aze; toe hitsoeke mifototse ami’ty volam-paha-fito iereo.
15 Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
Aa naho iranga’ t’indaty vaho ie mahaisake taola’ ondaty, le hañoreña’e vorovoro marine aze eo ampara’ te naleve’ o mpandentekeo am-bavatane’ i Valobohò’ i Gogey ao.
16 Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
Le hatao Hamonà ka ty añara’ i rovay; izay ty hañaliova’ iareo i taney.
17 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
Aa ihe, ana’ondatio, hoe ty nafè’ Iehovà Talè: Misaontsia amy ze fonga karazam-boroñe naho amy ze hene bibin-kivoke: Mitontona, mb’etoa; songa hivory añ’ ila’ i fisoroñakoy, i hisoroñako ho anahareoy, fisoroñam-bey an-kaboa’ Israele ey, hihinana’ areo nofotse naho hinoma’ areo lio.
18 Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
Habotse’ areo ty nofo’ o fanalolahio naho hinoñe ty lio’ o roandria’ ty tane toio; hoe t’ie añondrilahy naho ose-lahy vaho añombelahy songa vinondrake e Basane ao.
19 A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
Fonga hamotseke solike ampara’ te etsake, naho hinon-dio ampara’ te mamo amy soroñe nisoroñako ho anahareoy
20 A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
ie hampivontsiñeñe am-pandambañako eo amo soavalao naho amo sarete maozatseo vaho amo lahin-defoñe iabio, hoe t’Iehovà Talè.
21 “Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
Aa le hajadoko amo kilakila’ ndatio ty engeko, naho ho oni’ o kilakila’ ndatio i zaka nafetsakoy vaho ty tañako napetako am’ iareo.
22 Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
Le ho fohi’ i anjomba’ Israeley te Izaho Iehovà, Andrianañahare’ iareo henane zay vaho nainai’e.
23 Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
Ho fohi’ o kilakila’ ndatio te nisese mb’ am-pandrohizañe añe ty anjomba’ Israele ty amo hakeo’eo amy t’ie niola amako, le naetako am’ iereo ty tareheko naho natoloko am-pità’ o rafelahi’ iareoo, vaho fonga nitsingorom-pibara.
24 Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
Mira ami’ty haleora’ iareo naho ami’ty fiolà’ iareo ty nanoeko am’ iareo, vaho nañetahako tarehe.
25 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
Aa le hoe ty nafè’Iehovà Talè: Hampoliko henane zao ty fandrohiza’ Iakobe naho ho tretrezeko iaby ty anjomba’ Israele vaho ho farahieko ty añarako masiñe.
26 Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
Ie amy zay, ho haliño’ iereo ty fisalara’ iareo ty amo fiolàñe niolà’ iareo amakoo ie fa mierañerañe an-tane’ iareo ao, ie tsy eo ty mpañembañe,
27 Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
naho hampoliko hirik’ amo kilakila’ ndatio iereo, naho hambineko boak’ an-tane’ o rafelahi’eo vaho ho toloreñ’ asin-draho am-pahaisaham-pifeheañe maro;
28 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
le ho fohi’ iereo te Izaho Iehovà Andrianañahare’ iareo, ty nanese iareo mb’am-pandrohizañe añe añivo’ o kilakila’ ndatio naho natontoko boak’ an-tane’ iareo añe naho leo raike tsy hapoko
29 Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
vaho tsy hañetahako tarehe ka fa hakofòko amy anjomba’ Israeley ty Tioko, hoe t’Iehovà Talè.