< Ezekiyel 39 >

1 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
TUHAN Yang Mahatinggi berkata, "Hai manusia fana, ancamlah Gog, raja agung dari negeri-negeri Mesekh dan Tubal, dan katakanlah kepadanya bahwa Aku ini musuhnya.
2 Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
Aku akan membelokkan dia, dan membawa dia keluar dari daerah jauh di utara, ke gunung-gunung Israel.
3 Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
Di situ akan Kupukul busurnya sampai lepas dari tangan kirinya, dan Kujatuhkan anak-anak panahnya dari tangan kanannya.
4 A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
Di atas gunung-gunung Israel, Gog bersama seluruh tentara dan sekutunya akan gugur, dan mayat-mayat mereka akan Kuberikan kepada segala burung dan binatang buas untuk dimakan.
5 Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Prajurit-prajurit itu akan jatuh dan mati di ladang-ladang. Aku, TUHAN Yang Mahatinggi telah berbicara.
6 Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
Aku akan menimbulkan kebakaran di tanah Magog dan di pantai-pantai, di mana penduduknya hidup dengan tentram. Maka tahulah mereka semua bahwa Akulah TUHAN.
7 “‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
Tetapi di tengah-tengah orang Israel, akan Kunyatakan nama-Ku yang suci, dan nama-Ku itu tak akan lagi dicemarkan. Maka tahulah bangsa-bangsa bahwa Akulah TUHAN, Allah yang suci dari Israel."
8 Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
TUHAN Yang Mahatinggi berkata, "Sungguh, hari yang Kusebut itu akan datang.
9 “‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
Penduduk kota-kota di Israel akan keluar berbondong-bondong untuk mengumpulkan senjata-senjata yang telah ditinggalkan, yaitu perisai dan pedang, busur dan anak panah serta tongkat pemukul. Semua itu mereka jadikan kayu bakar, dan itu cukup untuk tujuh tahun.
10 Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Jadi mereka tidak perlu mengumpulkan kayu bakar di ladang atau menebang pohon di hutan, sebab senjata-senjata yang ditinggalkan itu cukup banyak untuk bahan bakar. Mereka akan merampok dan merampas harta orang-orang yang telah merampok dan merampas harta mereka. Aku, TUHAN Yang Mahatinggi telah berbicara."
11 “‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
TUHAN berkata, "Bilamana semua itu terjadi, Aku akan memberikan kepada Gog tanah pekuburan di Israel, di Lembah Penyeberangan yang terletak di sebelah timur dari Laut Mati. Di situlah Gog dan seluruh tentaranya akan dikuburkan, dan lembah itu akan disebut 'Lembah Pasukan Gog'.
12 “‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
Tujuh bulan lamanya orang-orang Israel akan sibuk menguburkan semua jenazah supaya tanah itu tidak najis lagi.
13 Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Seluruh penduduk negeri akan membantu pekerjaan penguburan itu; dan untuk itu mereka akan menerima penghargaan pada hari kemenangan-Ku. Aku, TUHAN Yang Mahatinggi telah berbicara.
14 “‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
Setelah tujuh bulan itu lewat, beberapa orang akan ditugaskan menjelajahi negeri itu untuk mencari mayat-mayat yang masih terkapar di tanah, dan jika ada, menguburkannya untuk membersihkan negeri itu dari yang najis.
15 Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
Dalam perjalanan itu, setiap kali mereka menemukan tulang manusia, mereka akan memberi tanda di sampingnya, supaya tukang-tukang kubur melihat itu dan menguburkan tulang itu di Lembah Pasukan Gog.
16 Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
Dengan cara itu tanah itu dibersihkan dari yang najis. (Di kemudian hari, di lembah itu akan ada kota yang namanya sama dengan Pasukan Gog.)"
17 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
TUHAN Yang Mahatinggi berkata kepadaku, "Hai manusia fana, panggillah semua burung dan binatang lainnya, supaya datang dari mana-mana untuk memakan kurban yang Kusediakan bagi mereka. Aku akan mengadakan pesta besar di gunung-gunung Israel, di sana mereka dapat makan daging dan minum darah.
18 Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
Mereka dapat memakan mayat-mayat pahlawan, dan minum darah para penguasa dunia. Para pahlawan dan penguasa itu akan dibunuh seperti kambing-kambing jantan atau anak-anak kambing, atau banteng-banteng gemuk.
19 A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
Sesudah Kubunuh orang-orang itu seperti kurban, burung-burung dan binatang-binatang lain akan memakan semua lemaknya sampai muak, dan meminum darah sampai mabuk.
20 A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Pada meja-Ku mereka dapat mengenyangkan perut dengan semua kuda dan penunggangnya dan dengan para pejuang. Aku, TUHAN Yang Mahatinggi telah berbicara."
21 “Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
TUHAN berkata, "Aku akan memperhatikan kemuliaan-Ku kepada bangsa-bangsa. Mereka semua akan melihat bagaimana Aku mempergunakan kuasa-Ku untuk melaksanakan keputusan-keputusan yang adil.
22 Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
Mulai saat itu orang Israel akan tahu bahwa Akulah TUHAN Allah mereka.
23 Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
Dan semua bangsa akan insaf bahwa orang Israel dikirim ke pembuangan karena dosa mereka terhadap Aku. Mereka sudah Kutinggalkan dan Kubiarkan dikalahkan oleh musuh dan dibunuh dalam pertempuran.
24 Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
Kuperlakukan mereka setimpal dengan kenajisan dan kejahatan mereka, lalu Kutinggalkan mereka."
25 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
TUHAN Yang Mahatinggi berkata, "Tetapi sekarang Aku akan mengasihani umat Israel keturunan Yakub, dan membuat mereka makmur kembali. Dengan demikian Aku menjaga agar nama-Ku tetap dihormati.
26 Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
Bila mereka tinggal lagi dengan tenang di negeri mereka sendiri, dan tak ada seorang pun yang mengancam mereka, maka mereka akan melupakan bagaimana mereka telah dipermalukan karena mengkhianati Aku.
27 Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
Aku akan membawa mereka kembali dari negeri-negeri musuh mereka, dan kesucian-Ku akan tampak kepada semua bangsa karena perbuatan-Ku itu.
28 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
Maka tahulah umat-Ku bahwa Akulah TUHAN Allah mereka. Sebab Akulah yang mengirim mereka ke pembuangan, tetapi Aku juga yang membawa mereka pulang ke negeri mereka sendiri, tanpa meninggalkan seorang pun dari mereka di sana.
29 Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Aku akan mencurahkan Roh-Ku atas bangsa Israel, dan tak akan meninggalkan mereka lagi. Aku, TUHAN Yang Mahatinggi telah berbicara."

< Ezekiyel 39 >