< Ezekiyel 39 >

1 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
Et toi, fils de l'homme, prophétise contre Gog, et dis: Ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Voici, j'en veux à toi, ô Gog, prince de Rosh, de Méshec et de Tubal.
2 Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
Je te conduirai, je t'entraînerai, je te ferai monter de l'extrême nord, et je t'amènerai sur les montagnes d'Israël.
3 Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
J'abattrai ton arc de ta main gauche, et ferai tomber tes flèches de ta main droite.
4 A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
Tu tomberas sur les montagnes d'Israël, toi et toutes tes troupes, et les peuples qui t'accompagnent; je t'ai livré en pâture aux oiseaux de proie, à tous les oiseaux et aux bêtes des champs.
5 Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Tu tomberas sur la surface de la terre, car j'ai parlé, dit le Seigneur, l'Éternel.
6 Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
Et j'enverrai le feu dans Magog, et parmi ceux qui habitent en sécurité dans les îles, et ils sauront que je suis l'Éternel.
7 “‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
Je ferai connaître mon saint nom au milieu de mon peuple d'Israël, et je ne profanerai plus mon saint nom, et les nations sauront que je suis l'Éternel, le Saint d'Israël.
8 Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
Voici, ces choses arrivent; elles se réalisent, dit le Seigneur, l'Éternel; c'est le jour dont j'ai parlé.
9 “‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
Les habitants des villes d'Israël sortiront, allumeront et brûleront les armes, les boucliers et les écus, les arcs et les flèches, les lances et les javelines, et ils en feront du feu pendant sept ans.
10 Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
On n'apportera point de bois des champs, on n'en coupera point dans les forêts, parce qu'ils feront du feu avec ces armes; ils dépouilleront ceux qui les avaient dépouillés, et pilleront ceux qui les avaient pillés, dit le Seigneur, l'Éternel.
11 “‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
En ce jour-là, je donnerai à Gog une sépulture en Israël, la vallée des passants, à l'orient de la mer; et cette sépulture bornera le chemin aux passants. C'est là qu'on enterrera Gog et toute sa multitude; et on appellera cette vallée, la vallée d'Hamon-Gog (de la multitude de Gog).
12 “‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
La maison d'Israël les enterrera pendant sept mois, afin de purifier le pays;
13 Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Et tout le peuple du pays les enterrera, et il en aura du renom, au jour où je me glorifierai, dit le Seigneur, l'Éternel.
14 “‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
Ils mettront à part des gens qui ne feront que parcourir le pays et qui, avec les passants, enterreront ceux qui seront restés à la surface de la terre, afin de la purifier, et pendant sept mois entiers ils seront à la recherche.
15 Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
Et si, en parcourant le pays, ils arrivent à voir des ossements d'hommes, ils dresseront près d'eux un signal, jusqu'à ce que les enterreurs les aient enterrés dans la vallée d'Hamon-Gog.
16 Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
Il y aura aussi une ville appelée Hamona (multitude). Ainsi l'on purifiera le pays.
17 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
Et toi, fils de l'homme, ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Dis aux oiseaux de toute espèce, et à toutes les bêtes des champs: Assemblez-vous, venez, réunissez-vous de toute part, pour le sacrifice que je fais pour vous, un grand sacrifice sur les montagnes d'Israël. Vous mangerez de la chair, et vous boirez du sang.
18 Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
Vous mangerez la chair des héros, vous boirez le sang des princes de la terre; des béliers, des agneaux, des boucs, tous engraissés en Bassan.
19 A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
Vous mangerez de la graisse jusqu'à en être rassasiés, et vous boirez du sang jusqu'à vous enivrer, au sacrifice que je ferai pour vous.
20 A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Vous serez rassasiés à ma table, des chevaux et des cavaliers, des héros et de tous les hommes de guerre, dit le Seigneur, l'Éternel.
21 “Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
Je manifesterai ma gloire parmi les nations, et toutes les nations verront mon jugement, que j'exercerai, et comment je leur ferai sentir ma main.
22 Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
Et la maison d'Israël saura que je suis l'Éternel, leur Dieu, dès ce jour et à l'avenir.
23 Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
Et les nations sauront que la maison d'Israël a été transportée en captivité à cause de ses iniquités, parce qu'ils ont péché contre moi. Aussi j'ai caché ma face devant eux, et je les ai livrés entre les mains de leurs ennemis, afin que tous ils tombent par l'épée.
24 Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
Je les ai traités selon leurs souillures et selon leur crime, et j'ai caché ma face devant eux.
25 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
C'est pourquoi, ainsi a dit le Seigneur, l'Éternel: Maintenant je ramènerai les captifs de Jacob, et j'aurai pitié de toute la maison d'Israël, et je serai jaloux de mon saint nom.
26 Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
Ils auront supporté leur ignominie, et tous les péchés dont ils se sont rendus coupables envers moi, lorsqu'ils demeureront en sécurité dans leur pays, sans que personne les épouvante.
27 Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
Lorsque je les ramènerai d'entre les peuples, et que je les rassemblerai des pays de leurs ennemis, je serai sanctifié par eux aux yeux de beaucoup de nations.
28 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
Et ils sauront que je suis l'Éternel leur Dieu, lorsqu'après les avoir transportés parmi les nations, je les aurai réunis dans leur pays, sans en laisser aucun en arrière.
29 Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Et je ne cacherai plus ma face devant eux, car je répandrai mon Esprit sur la maison d'Israël, dit le Seigneur, l'Éternel.

< Ezekiyel 39 >