< Ezekiyel 39 >

1 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
" Et toi, fils de l'homme, prophétise contre Gog et dis: Ainsi parle le Seigneur Yahweh: Voici que je viens à toi, Gog, prince souverain de Mosoch et de Thubal.
2 Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
Je t'emmènerai, je te conduirai et je te ferai monter des confins du septentrion, et je t'amènerai sur les montagnes d'Israël.
3 Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
Là j'abattrai ton arc de ta main gauche, et je ferai tomber tes flèches de ta main droite.
4 A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
Tu tomberas sur les montagnes d'Israël, toi et tous tes bataillons, et les peuples qui seront avec toi; aux oiseaux de proie, aux oiseaux de toute sorte, et aux animaux des champs je t'ai donné en pâture.
5 Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Tu tomberas sur la face des champs, car moi j'ai parlé, — oracle du Seigneur Yahweh.
6 Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
J'enverrai le feu dans le pays de Magog et chez ceux qui habitent en sécurité dans les îles, et ils sauront que je suis Yahweh.
7 “‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
Et je ferai connaître mon saint nom au milieu de mon peuple d'Israël, et je ne profanerai plus mon saint nom; et les nations sauront que je suis Yahweh, saint en Israël.
8 Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
Ces choses viennent et elles s'accompliront, — oracle du Seigneur Yahweh; c'est là le jour dont j'ai parlé!
9 “‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
Alors les habitants des villes d'Israël sortiront; ils brûleront et mettront en flammes les armes, l'écu, le bouclier, l'arc, les flèches, le bâton et le javelot; ils en feront du feu pendant sept ans.
10 Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Ils n'apporteront plus le bois de la campagne, et ils n'en couperont point dans les forêts; car c'est avec les armes qu'ils feront du feu; ils dépouilleront ceux qui les dépouillaient, ils pilleront ceux qui les pillaient, — oracle du Seigneur Yahweh.
11 “‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
Et il arrivera en ce jour-là: Je donnerai à Gog un lieu où sera son sépulcre en Israël, la vallée des Passants, à l'orient de la mer; et ce sépulcre fermera le chemin aux passants. C'est là qu'on enterrera Gog et toute sa multitude, et on appellera ce lieu la vallée d'Hamon-Gog.
12 “‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
La maison d'Israël les enterrera, afin de purifier le pays, sept mois durant.
13 Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Tout le peuple du pays enterrera, et ce sera pour eux un jour glorieux; celui où j'aurai fait éclater ma gloire, — oracle du Seigneur Yahweh.
14 “‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
Et ils désigneront des hommes dont la charge sera de parcourir le pays, enterrant les passants, ceux qui seront restés sur la face de la terre, — pour la purifier; après sept mois ils feront leurs recherches.
15 Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
Et quand ces hommes parcourront le pays, si l'un d'eux voit des ossements humains, il dressera à coté un signal, jusqu'à ce que les enterreurs les aient mis en terre dans la vallée d'Hamon-Gog.
16 Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
Et Hamona sera même le nom d'une ville; et c'est ainsi qu'ils purifieront le pays.
17 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
Et toi, fils de l'homme, ainsi parle le Seigneur Yahweh: Dis aux oiseaux de toute sorte, et à tous les animaux des champs: Assemblez-vous et venez! Réunissez-vous des alentours à mon sacrifice que je fais pour vous, un grand sacrifice sur les montagnes d'Israël; vous mangerez de la chair et vous boirez du sang.
18 Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
C'est de la chair de héros que vous mangerez, c'est du sang de princes de la terre que vous boirez, béliers, agneaux et boucs, jeunes taureaux, bœufs gras de Basan tous ensemble.
19 A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
Vous mangerez de la graisse à satiété, vous boirez du sang jusqu'à l'ivresse, à mon sacrifice que j'ai fait pour vous.
20 A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Vous vous rassasierez à ma table de coursiers et de cavaliers, de héros et de guerriers de toute sorte, — oracle du Seigneur Yahweh.
21 “Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
Je manifesterai ma gloire parmi les nations, et toutes les nations verront mon jugement que j'exécuterai; et ma main que j'étendrai sur eux.
22 Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
Et la maison d'Israël saura que je suis Yahweh, son Dieu, dès ce jour et à l'avenir:
23 Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
et les nations sauront que c'est à cause de son iniquité que la maison d'Israël a été menée en exil, parce qu'ils m'ont été infidèles; aussi je leur ai caché ma face, je les ai livrés aux mains de leurs ennemis, afin qu'ils tombassent tous par l'épée.
24 Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
C'est en raison de leur souillure et de leur prévarication que je les ai traités ainsi et que je leur ai caché ma face.
25 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
C'est pourquoi ainsi parle le Seigneur Yahweh: Maintenant, je ramènerai les captifs de Jacob, j'aurai compassion de toute la maison d'Israël, et je me montrerai jaloux de mon nom.
26 Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
Ils porteront leur ignominie, et toutes les infidélités qu'ils ont commises envers moi, quand ils habiteront sur leur terre en sécurité, sans que personne les inquiète.
27 Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
Quand je les ramènerai d'entre les peuples, que je les rassemblerai des pays de leurs ennemis et que je me serai sanctifié en eux, aux yeux de beaucoup de nations,
28 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
ils sauront que je suis Yahweh, leur Dieu, en ce que je les aurai emmenés captifs chez les nations, et rassemblés ensuite sur leur propre sol; et je ne laisserai plus aucun d'eux là-bas.
29 Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
Et je ne leur cacherai plus ma face, parce que j'aurai répandu mon Esprit sur la maison d'Israël, — oracle du Seigneur Yahweh. "

< Ezekiyel 39 >