< Ezekiyel 39 >

1 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
[Yahweh said to me], “You human, prophesy about [more terrible things that will happen] to Gog, and say this [to him]: ‘Gog, I am opposed to you who rule Meshech and Tubal.
2 Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
I will turn you around and drag you [and your armies] from far north [of Israel] and send you to [fight on] the mountains in Israel.
3 Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
When you are there, I will snatch your bows from your left hands and cause your arrows to fall from your right hands.
4 A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
You and all the soldiers that are with you will die on the mountains in Israel. I will give your [corpses] to be food for the birds that eat [dead] flesh, and to the wild animals.
5 Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
You will die in the open fields. [That will surely happen because] I, Yahweh the Lord, [have said that it will happen].
6 Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
I will cause [many] fires to burn in Magog and among [all] those who live safely in the areas along their coasts, and they will know that it is I, Yahweh, [who have the power to do what I say that I will do].
7 “‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
I will enable my Israeli people to know that I am holy. I will no longer allow people to damage my reputation, and [people in other] nations will know that I, Yahweh the Lord, am the Holy One in Israel.
8 Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
[I], Yahweh the Lord, declare that it will soon be the day that those things will happen. It will be the day that I have spoken [to you] about.
9 “‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
At that time, those Israelis who live in the towns will go out and gather the weapons [from your dead soldiers], and use them to make fires [to cook their food]. They will burn the small and large shields, the bows and arrows, the war clubs, and spears. There will be enough weapons to use as firewood for seven years.
10 Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
They will not need to gather firewood in the fields or cut wood from trees in the forests, because those weapons will be all the firewood [that they will need]. And they will take valuable things from those who took valuable things from them, and steal things from people who stole things from them. [That is what I], Yahweh the Lord, declare [will happen].
11 “‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
At that time I will create a graveyard for you, Gog, [and your soldiers], in the valley east of the [Dead] Sea. That graveyard will block the road that travelers [usually walk on], because you, Gog and all [the soldiers] of your huge army will be buried there. [So] it will be named ‘the Valley of Gog’s Huge Army’.
12 “‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
For seven months the people of Israel will be burying those corpses. [It will be necessary to bury all of them], in order that the land will not be (defiled/considered unacceptable to me) [because of any unburied corpses].
13 Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
All the people of Israel will [do the work of] burying them. The day when I [win that victory] they will honor me.
14 “‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
After those seven months are ended, the Israeli people will appoint men to go throughout the land to bury corpses, in order that the land will not remain defiled.
15 Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
When they go through the land, when one of them sees a human bone, he will set up a marker beside it. [When] the gravediggers [see the markers, they will pick up the bones] and bury them in the Valley of Gog’s Huge Army.
16 Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
There will be a city there named Hamonah, [which means ‘huge army’]. And by doing this [work of burying the corpses], they will (cleanse the land/cause the land to be acceptable to me again).’”
17 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
[Yahweh said to me], “You human, this is what [I], Yahweh the Lord, say: Summon every kind of bird and wild animal. Say to them, ‘Gather together from everywhere and come to the feast that Yahweh is preparing for you. [It will be] a great feast on the mountains in Israel. [There] you will eat [men’s] flesh and drink their blood.
18 Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
You will eat the flesh of strong soldiers and drink the blood of kings [as if they were] fat animals—rams and lambs, goats and bulls—from the Bashan [region].
19 A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
At that feast that Yahweh is preparing for you, you will eat fat until your [stomachs] are full, and you will drink blood until [it is as though] you are drunk.
20 A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
[It will be as though] you are eating at a table that I [have set up for you. You will eat all you want of the flesh] of horses and their riders, strong soldiers [DOU] of every kind.’ [That is what I], Yahweh the Lord, declare.
21 “Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
I will show [people of] many nations that I am glorious, and all those nations will see how I punish them [DOU].
22 Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
After that time, the Israeli people will know that I, Yahweh their God, [have the power to do what I say that I will do].
23 Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
And the [people of other] nations will know that the Israeli people had been forced to go to other countries because they sinned by not being faithful to me. I (turned away from/abandoned) them, and allowed their enemies to capture them [IDM], and many [HYP] of them were killed by [their enemies’] swords.
24 Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
I punished them like they deserved to be punished because of their disgusting behavior and sins, and I turned away from them [MTY].
25 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
Therefore, this is [now] what I, Yahweh the Lord, say: I will now bring back from exile/Babylonia [the descendants of] Jacob; I will pity all the Israeli people, and I will [also] jealously protect my reputation.
26 Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
When the Israeli people [are back in their own country, they will] live safely in their land, with no one to cause them to be afraid, but they will be ashamed when they think about the disgraceful and unfaithful things that they did [previously].
27 Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
When I have brought them back from their enemies’ countries and gathered them together [in Israel], the people of many nations will know that I am holy.
28 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
And the Israeli people will know that I, Yahweh their Lord, [have the power to do what I say that I will do]. They will know that because [even though] I forced them to go to [other] countries, I will gather them together in their own country. I will not leave any of them in those countries.
29 Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
I will no longer turn away from them; I will pour out my Spirit on the Israeli people. [That will surely happen because I], Yahweh, have said it.”

< Ezekiyel 39 >