< Ezekiyel 39 >

1 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
And thou, son of man, prophesy against Cog, and say: Thus saith the Lord God: Behold, I come against thee, O Cog, the chief prince of Mosoch and Thubal.
2 Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
And I will turn thee round, and I will lead thee out, and will make thee go up from the northern parts: and will bring thee upon the mountains of Israel.
3 Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
And I will break thy bow in thy left hand, and I will cause thy arrows to fall out of thy right hand.
4 A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
Thou shalt fall upon the mountains of Israel, thou and all thy bands, and thy nations that are with thee: I have given thee to the wild beasts, to the birds, and to every fowl, and to the beasts of the earth to be devoured.
5 Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Thou shalt fall upon the face of the field: for I have spoken it, saith the Lord God.
6 Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
And I will send a fire on Magog, and on them that dwell confidently in the islands: and they shall know that I am the Lord.
7 “‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
And I will make my holy name known in the midst of my people Israel, and my holy name shall be profaned no more: and the Gentiles shall know that I am the Lord, the Holy One of Israel.
8 Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
Behold it cometh, and it is done, saith the Lord God: this is the day whereof I have spoken.
9 “‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
And the inhabitants shall go forth of the cities of Israel, and shall set on fire and burn the weapons, the shields, and the spears, the bows and the arrows, and the handstaves and the pikes: and they shall burn them with fire seven years.
10 Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And they shall not bring wood out of the countries, nor cut down out of the forests: for they shall burn the weapons with fire, and shall make a prey of them to whom they had been a prey, and they shall rob those that robbed them, saith the Lord God.
11 “‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
And it shall come to pass in that day, that I will give Gog a noted place for a sepulchre in Israel: the valley of the passengers on the east of the sea, which shall cause astonishment in them that pass by: and there shall they bury Cog, and all his multitude, and it shall be called the valley of the multitude of Cog.
12 “‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
And the house of Israel shall bury them for seven months to cleanse the land.
13 Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And all the people of the land shall bury him, and it shall be unto them a noted day, wherein I was glorified, saith the Lord God.
14 “‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
And they shall appoint men to go continually about the land, to bury and to seek out them that were remaining upon the face of the earth, that they may cleanse it: and after seven months they shall begin to seek.
15 Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
And they shall go about passing through the land: and when they shall see the bone of a man, they shall set up a sign by it, till the buriers bury it in the valley of the multitude of Cog.
16 Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
And the name of the city shall be Amona, and they shall cleanse the land.
17 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
And thou, O son of man, saith the Lord God, say to every fowl, and to all the birds, and to all the beasts of the field: Assemble yourselves, make haste, come together from every side to my victim, which I slay for you, a great victim upon the mountains of Israel: to eat flesh, and drink blood.
18 Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
You shall eat the flesh of the mighty, and you shall drink the blood of the princes of the earth, of rams, and of lambs, and of he goats, and bullocks, and of all that are well fed and fat.
19 A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
And you shall eat the fat till you be full, and shall drink blood till you be drunk of the victim which I shall slay for you.
20 A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And you shall be filled at my table with horses, and mighty horsemen, and all the men of war, saith the Lord God.
21 “Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
And I will set my glory among the nations: and all nations shall see my judgment that I have executed, and my hand that I have laid upon them.
22 Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
And the house of Israel shall know that I am the Lord their God from that day and forward.
23 Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
And the nations shall know that the house of Israel were made captives for their iniquity, because they forsook me, and I hid my face from them: and I delivered them into the hands of their enemies, and they fell all by the sword.
24 Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
I have dealt with them according to their uncleanness, and wickedness, and hid my face from them.
25 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
Therefore, thus saith the Lord God: Now will I bring back the captivity of Jacob, and will have mercy on all the house of Israel: and I will be jealous for my holy name.
26 Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
And they shall bear their confusion, and all the transgressions wherewith they have transgressed against me, when they shall dwell in their land securely fearing no man:
27 Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
And I shall have brought them back from among the nations, and shall have gathered them together out of the lands of their enemies, and shall be sanctified in them, in the sight of many nations.
28 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
And they shall know that I am the Lord their God, because I caused them to be carried away among the nations; and I have gathered them together unto their own land, and have not left any of them there.
29 Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
And I will hide my face no more from them, for I have poured out my spirit upon all the house of Israel, saith the Lord God.

< Ezekiyel 39 >