< Ezekiyel 39 >

1 “Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
“But as for you, son of man, prophesy against Gog, and you shall say: Thus says the Lord God: Behold, I am above you, O Gog, prince of the head of Meshech and Tubal.
2 Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
And I will turn you around, and I will lead you away, and I will cause you to rise up from the parts of the north. And I will bring you over the mountains of Israel.
3 Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
And I will strike your bow in your left hand, and I will cast away your arrows from your right hand.
4 A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
You will fall upon the mountains of Israel, you and all your companies, and your peoples who are with you. I have given you over to the wild animals, to the birds, and to every flying thing, and to the beasts of the earth, in order to be devoured.
5 Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
You will fall upon the face of the field. For I have spoken, says the Lord God.
6 Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
And I will send a fire upon Magog, and upon those who are living confidently in the islands. And they shall know that I am the Lord.
7 “‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
And I will make known my holy name in the midst of my people, Israel, and my holy name will no longer be defiled. And the Gentiles shall know that I am the Lord, the Holy One of Israel.
8 Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
Behold, it approaches, and it is done, says the Lord God. This is the day, about which I have spoken.
9 “‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
And the inhabitants from the cities of Israel will go forth, and they will kindle and burn the weapons, the shields and the spears, the bows and the arrows, and the staff and the lance. And they will kindle fires with them for seven years.
10 Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And they will not carry wood from the countryside, and they will not cut from the forests. For they will kindle the weapons with fire. And they will prey upon those who had preyed upon them, and they will plunder those who had plundered them, says the Lord God.
11 “‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
And this shall be in that day: I will give Gog a renowned place as a sepulcher in Israel, the valley of the wayfarers to the east of the sea, which will cause astonishment in those who pass by. And in that place, they will bury Gog and all his multitude, and it will be called the valley of the multitude of Gog.
12 “‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
And the house of Israel will bury them, so that they may cleanse the land, for seven months.
13 Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
Then all the people of the earth will bury them, and this shall be for them a renowned day, on which I have been glorified, says the Lord God.
14 “‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
And they shall appoint men to continually examine the earth, so that they may seek out and bury those who have remained on the surface of the earth, so that they may cleanse it. Then, after seven months, they will begin to seek.
15 Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
And they will go around, traveling the earth. And when they will have seen the bone of a man, they will station a marker beside it, until the undertakers may bury it in the valley of the multitude of Gog.
16 Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
And the name of the city will be: the Multitude. And they shall cleanse the earth.
17 “Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
As for you, then, son of man, thus says the Lord God: Say to every flying thing, and to all the birds, and to all the beasts of the field: Assemble! Hurry! Rush together from every side to my victim, which I have immolated for you, a great victim upon the mountains of Israel, so that you may consume flesh, and drink blood!
18 Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
You shall eat the flesh of the powerful, and you shall drink the blood of the princes of the earth, of rams and lambs and he-goats and bulls, and of fattened birds and all that is fat.
19 A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
And you shall consume the fat unto satiation, and you shall drink the blood unto inebriation, from the victim that I will immolate for you.
20 A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
And you shall be satiated, upon my table, from horses and powerful horsemen, and from all the men of war, says the Lord God.
21 “Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
And I will set my glory among the Gentiles. And all the nations shall see my judgment, which I have accomplished, and my hand, which I have laid upon them.
22 Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
And the house of Israel shall know that I am the Lord, their God, from that day and thereafter.
23 Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
And the Gentiles shall know that the house of Israel was taken captive because of their own iniquity, because they abandoned me. And so I concealed my face from them, and I delivered them into the hands of their enemies, and they all fell by the sword.
24 Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
I have acted toward them in accord with their uncleanness and wickedness, and so I concealed my face from them.
25 “Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
Because of this, thus says the Lord God: Now I will lead back the captivity of Jacob, and I will take pity upon the entire house of Israel. And I will act with zeal on behalf of my holy name.
26 Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
And they shall bear their shame and all their transgression, by which they betrayed me, though they were living in their own land confidently, dreading no one.
27 Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
And I will lead them back from among the peoples, and I will gather them together from the lands of their enemies, and I will be sanctified in them, in the sight of the many nations.
28 Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
And they shall know that I am the Lord, their God, because I carried them away to the nations, and I gathered them upon their own land, and I did not abandon any of them there.
29 Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
And I will no longer conceal my face from them, for I have poured out my Spirit upon the entire house of Israel, says the Lord God.”

< Ezekiyel 39 >